Sashe 43
Feeryal Part 2 Complete Hausa Novel.t · about 7 min read
Hajiya abin bai mata ba da daddare tayi tattaki zuwa sashin Daddy,
takuma jaddada masa ko bayan ranta akayi auren nan bata yafe ba.
Hajiya bala'i take tana fad'in
"Sabo da aljanar yarinyar nan ta gama shiga jikin ka, shine kake nima ka kakabawa abokin turawa ita dan shima ta shige jikin nasa ko,
to kai da kayi gayyarta kaje can ka karata badai jikana ba,
wlh takar baki idan ka kuskira sai ka biyani nono na!
kuma gobe-goben nan nake son yarinyar nan tabar gidan nan, idan bata tafi gobe ba ni zan tafi kuma kar ka sake kaje in da nake bani ba kai ke nan."
Hajiya ta juya ta fita tana cigaba da bala'i.
Wad'annan kalaman da Hajiya ta fad'a sunyi mugun tsayawa Daddy a rai, dan kalmace mai girman gaske akan kowani d'a idan uwa ta gaya masa.
kalaman sunyi masa girma har sai da yaji kamar ciwonsa na shirin tashi.
ranar a daddafe ya kwana kirjinsa na zafi.
washegari da safe Daddy ya kira Bappa Salihu na Yelwa mahaifin Mommy kanin mahaifin su, yasanar masa abun da ke faruwa.
Bappa Salihu ya ce
"Hajiya Hanne ke nan, wannan magana bazata yuwu a waya ba zanyi tattaki nazo Lagos d'in, insha'allahu gobe zuwa jibi zan shigo Jos nahayo jirgi na iso nan Lagos d'in."
Daddy ya yi ta masa godiya kana ya katse kiran.
lambar Abdulrahim ya kira ya ce yazo yana niman sa.
batare da b'ata lokaci ba ya shigo parlour'n nasa.
ya nimi guri ya zauna tare da gaida Daddy ya amsa yana kuma duban sa da kyau, sannan ya d'anyi gyaran murya kana ya ce
"Abdulrahim nakiraka ne domin nagaya maka hukuncin dana zartar a kanka,
duk da kakarka ta nuna rashin amincewar ta,
bazanyi kasa a gwuiwa ba zan sanar maka kafin lokacin dana yanke yazo,
Abdulrahim zan aura maka Feeryal bayan ganin dacewar hakan na zartar da hukuncin."
da karfi ya yi wani irin d'agowa ya dubi Daddy.
Daddy ya jijjiga kai tare da fad'in
"Kwarai kuwa hukuncin dana yanke ke nan."
kasa ya yi da kansa batare da ya ce ko mai ba.
Daddy ya ce
"Tashi kaje idan na tsaida rana zan sanar maka."
da sauri ya ce
"Amma Daddy."
"Amma me Abdulrahim musu zakayi min?."
kai yakuma sunkuyar wa, bai kuma magana ba,
a sannu ya mike ya yi waje Daddy yabi bayan sa da kallo.
Abdulrahim na fita Daddy ya kira Mommy a waya ya ce tazo yana son magana da ita.
Mommy ta shigo ta same shi a parlour ta nimi guri ta zauna.
Daddy ya dube ta kana ya ce
"Hajiya Halima nakira ki ne domin na sanar miki abun da na yanke kan d'ana,
bana so ace kinji maganar a gun wani, ki kalli hakan a kan rashin adalci;
ina sanar miki hakan ne dalilin ke ma uwa ce a gare shi, kafin na zartar da hukunci yana da kyau na sanar miki,
zan d'aurawa Abdulrahim aure da Feeryal,
ni mahaifin Abdulrahim ita na zab'a masa a matsayin mata."
Daddy na kaiwa nan ya mike yanufi kofar fita
wani irin daramm damm Mommy taji tamkar saukar aradu aka, sabar tashin hankali da d'inbin mamaki da jin abun tamkar almara kasa iya furta komai tayi.
tabi shi da kallo har ya b'acewa ganin ta.
sai sannan ta sauke wani uban ajiyan zuciya kamar wacce ta suma ta farfad'o.
ta ce
"Tabd'ijan wlh karya ne bazai tab'a yuwuwa ba!."
A haukace Mommy ta mike tabi bayan sa, ta hango har ya shiga mota direba ya ja shi sun nufi get.
sashin Hajiya ta nufa tana zuba ruwan bala'i bata ko ganin gaban ta.
tun daga bakin kofa take fad'in
"Hajiya ciwon nan ya fara tab'awa Alhaji kwakwalwa fa, kinji me yake gaya min yanzu kuwa, wai zai aurawa Abdulrahim wannan aljanar yarinyar."
Hajiya ta ce "Wato bai janye maganar ba ke nan, to ai sai ya yi mugani, ba sai ma ya ganta a gidan ba."
ta fita fuuu Mommy tabi bayan ta.
"Ina aljanar take fito kibar gidan nan, tun da bana uban ki bane."
Hajiya ta fad'a sanda suke shiga parlour'n Aunty.
Aunty ta mike tsaye da sauri.
Mommy ta wurga mata kallon banza sannan ta ce
"Kina tunanin yadda kika sami kan Alhaji haka zaki sami na d'ana, wlh karya kike ba dai d'ana ba kam."
tuni Hajiya ta wuce d'akin Feeryal ta na fad'in
"Ina kike fito kibar gidan nan jikana yafi karfin ki."
Hajiya ta shiga raba ido cikin d'akin ganin bata ciki, ta wuce har cikin bayi, nan ma bata nan.
ta fito tana fad'in
"Ina kika b'oye ta fito da ita yau bazata kuma kwana gidan nan ba."
Aunty bata ce kala ba suka karaci masifarsu suka gama bincikota basu ganta ba suka tafi.
sai da suka tafi tukun Feeryal dake kichin suna aiki da Baba Rabi ta fito.
dan tajiyo hayaniyar su kuma tasan a kanta ne bai wuce ace tabar musu gida ba, dan Aunty bata sanar mata da abun da ke faruwa ba.
Mommy bil hakki ta d'aga bori babu wanda ya isa ya aurawa d'an ta Feeryal.
a gefe guda ma Hajiya na nata,
a d'aya gefen kuwa labari daya isarwa Umma Karima kaukane kawai batayi.
Bappa Salihu baiyi kasa a gwuiwa ba ya diro Lagos bayan maganar su da Daddy da kwana biyu, ya iso da daddare.
bai bari sai gari ya waye ba ya iso sashin Hajiya.
Hajiya tayi mamakin ganin sa a irin wannan lokacin.
Hajiya ta cewa Kulu ta kawo masa abinci
Bappa Salihu ya ce
"Bar abincin ki Hajiya Hanne bacin abincinki bane ya kawo ni."
Hajiya ta d'aga hanci sama tana cewa
"Yoo wata maganar aka gaya maka ke nan, nifa in akan batun auren abokin turawa ne da aljanar yarinyar nan ne,
bafa zan zuba ido ina gani a kakabawa jikana damuwa ba."
"Yanzu fisabilillahi Hajiya Hanne, ya kyautu ke nan kirika jifan d'anki da irin wad'an nan munanan kalamai,
mutumin da ba wani cikakken lafiya yake da shi ba, kike son ki rika d'aga masa hankali,
haba Hajiya Hanne har duniyar tayi miki dad'i irin haka, yau idan ya fad'i ya mutu wayake da asara,
ni bazan yadda nasa iso akan wani dalilinki mara ma'ana ki salwantar min da rayuwar d'a ba,
sabo da Yaya Shitu Fiya bashi da rai shike nan kike so ke ki baje kafa kizamo kece uwar kece uban,
to kar ki manta muna nan mu rai uku masu rai, ba kuma zamu sa miki ido ki nima yiwa 'ya'yan mu baki akarin banza ba,
musamman shi jigon mu Abubakar,
wani irin shirme ne wannan,
kiyi gaggawar janye furucinki a kanshi in ba so kike ki zamo ajalinsa ba,
daga ya so had'a sunnar annabi shike nan kibi ki tada hankalin ki,
bakin ciki kike da sunnar annabin?."
Hajiya ta ce
"Ni dama ai ban masa baki ba na gaya masa ne kawai bai isa ya aurawa jikana aljana ba."
Bappa Salihu ya ce
"To ai ba jikan ki bane ke kad'ai, kin san munfiki iko da Abubakar."
Hajiya ta ce
"To kuzo ku zauna da 'ya'yan ku ai dama tun ba yauba kuke nuna min bushashshen iko da gadara, nifa gara na koma gun dangina ma, dana zauna ana gwada min wani gadara,
in dai aure ne da wannan aljanar ko bani gidan nan baza'ayi sa ba."
Hajiya ta mike ta shige d'aki ta soma tattare-tattaren kaya, tana mita.
Bappa Salihu ya mike ya fita yana girgiza kai da fad'in
"Hajiya Hanne ikon Allah."
Washegari da safe bayan sallar asuba Daddy ya shigo sashin Aunty, tana kan sallaya yazuba mata goro da minti a gaban ta.
da sauri ta d'ago ta ce
"Daddy wannan fa?."
zama ya yi a bakin gado sannan ya ce
"Na auren Abdulrahim da Feeryal ne da aka d'aura yanzu.......!
*Masha'allah anan wannan littafi na biyu ya kawo karshe sai mun had'u a littafi na na uku*🤗
*FEERYAL littafin kud'i ne ki biya domin karantawa cikin aminci 500 account no 3170524141 Rashida Salihu first bank.
ki tura shaidar biya ta Whatsapp number ta 08034690723 ina maraba da ku masoya na ni ma ina kaunar ku*🤗
Bari muzo mu raka FEERYAL d'akin ABDULRAHIM kowa ya tafi cikin shiri fa dan bamusan ya zamu tarar uwargida Kuraiba ba😂🤸⛹ï¸
takuma jaddada masa ko bayan ranta akayi auren nan bata yafe ba.
Hajiya bala'i take tana fad'in
"Sabo da aljanar yarinyar nan ta gama shiga jikin ka, shine kake nima ka kakabawa abokin turawa ita dan shima ta shige jikin nasa ko,
to kai da kayi gayyarta kaje can ka karata badai jikana ba,
wlh takar baki idan ka kuskira sai ka biyani nono na!
kuma gobe-goben nan nake son yarinyar nan tabar gidan nan, idan bata tafi gobe ba ni zan tafi kuma kar ka sake kaje in da nake bani ba kai ke nan."
Hajiya ta juya ta fita tana cigaba da bala'i.
Wad'annan kalaman da Hajiya ta fad'a sunyi mugun tsayawa Daddy a rai, dan kalmace mai girman gaske akan kowani d'a idan uwa ta gaya masa.
kalaman sunyi masa girma har sai da yaji kamar ciwonsa na shirin tashi.
ranar a daddafe ya kwana kirjinsa na zafi.
washegari da safe Daddy ya kira Bappa Salihu na Yelwa mahaifin Mommy kanin mahaifin su, yasanar masa abun da ke faruwa.
Bappa Salihu ya ce
"Hajiya Hanne ke nan, wannan magana bazata yuwu a waya ba zanyi tattaki nazo Lagos d'in, insha'allahu gobe zuwa jibi zan shigo Jos nahayo jirgi na iso nan Lagos d'in."
Daddy ya yi ta masa godiya kana ya katse kiran.
lambar Abdulrahim ya kira ya ce yazo yana niman sa.
batare da b'ata lokaci ba ya shigo parlour'n nasa.
ya nimi guri ya zauna tare da gaida Daddy ya amsa yana kuma duban sa da kyau, sannan ya d'anyi gyaran murya kana ya ce
"Abdulrahim nakiraka ne domin nagaya maka hukuncin dana zartar a kanka,
duk da kakarka ta nuna rashin amincewar ta,
bazanyi kasa a gwuiwa ba zan sanar maka kafin lokacin dana yanke yazo,
Abdulrahim zan aura maka Feeryal bayan ganin dacewar hakan na zartar da hukuncin."
da karfi ya yi wani irin d'agowa ya dubi Daddy.
Daddy ya jijjiga kai tare da fad'in
"Kwarai kuwa hukuncin dana yanke ke nan."
kasa ya yi da kansa batare da ya ce ko mai ba.
Daddy ya ce
"Tashi kaje idan na tsaida rana zan sanar maka."
da sauri ya ce
"Amma Daddy."
"Amma me Abdulrahim musu zakayi min?."
kai yakuma sunkuyar wa, bai kuma magana ba,
a sannu ya mike ya yi waje Daddy yabi bayan sa da kallo.
Abdulrahim na fita Daddy ya kira Mommy a waya ya ce tazo yana son magana da ita.
Mommy ta shigo ta same shi a parlour ta nimi guri ta zauna.
Daddy ya dube ta kana ya ce
"Hajiya Halima nakira ki ne domin na sanar miki abun da na yanke kan d'ana,
bana so ace kinji maganar a gun wani, ki kalli hakan a kan rashin adalci;
ina sanar miki hakan ne dalilin ke ma uwa ce a gare shi, kafin na zartar da hukunci yana da kyau na sanar miki,
zan d'aurawa Abdulrahim aure da Feeryal,
ni mahaifin Abdulrahim ita na zab'a masa a matsayin mata."
Daddy na kaiwa nan ya mike yanufi kofar fita
wani irin daramm damm Mommy taji tamkar saukar aradu aka, sabar tashin hankali da d'inbin mamaki da jin abun tamkar almara kasa iya furta komai tayi.
tabi shi da kallo har ya b'acewa ganin ta.
sai sannan ta sauke wani uban ajiyan zuciya kamar wacce ta suma ta farfad'o.
ta ce
"Tabd'ijan wlh karya ne bazai tab'a yuwuwa ba!."
A haukace Mommy ta mike tabi bayan sa, ta hango har ya shiga mota direba ya ja shi sun nufi get.
sashin Hajiya ta nufa tana zuba ruwan bala'i bata ko ganin gaban ta.
tun daga bakin kofa take fad'in
"Hajiya ciwon nan ya fara tab'awa Alhaji kwakwalwa fa, kinji me yake gaya min yanzu kuwa, wai zai aurawa Abdulrahim wannan aljanar yarinyar."
Hajiya ta ce "Wato bai janye maganar ba ke nan, to ai sai ya yi mugani, ba sai ma ya ganta a gidan ba."
ta fita fuuu Mommy tabi bayan ta.
"Ina aljanar take fito kibar gidan nan, tun da bana uban ki bane."
Hajiya ta fad'a sanda suke shiga parlour'n Aunty.
Aunty ta mike tsaye da sauri.
Mommy ta wurga mata kallon banza sannan ta ce
"Kina tunanin yadda kika sami kan Alhaji haka zaki sami na d'ana, wlh karya kike ba dai d'ana ba kam."
tuni Hajiya ta wuce d'akin Feeryal ta na fad'in
"Ina kike fito kibar gidan nan jikana yafi karfin ki."
Hajiya ta shiga raba ido cikin d'akin ganin bata ciki, ta wuce har cikin bayi, nan ma bata nan.
ta fito tana fad'in
"Ina kika b'oye ta fito da ita yau bazata kuma kwana gidan nan ba."
Aunty bata ce kala ba suka karaci masifarsu suka gama bincikota basu ganta ba suka tafi.
sai da suka tafi tukun Feeryal dake kichin suna aiki da Baba Rabi ta fito.
dan tajiyo hayaniyar su kuma tasan a kanta ne bai wuce ace tabar musu gida ba, dan Aunty bata sanar mata da abun da ke faruwa ba.
Mommy bil hakki ta d'aga bori babu wanda ya isa ya aurawa d'an ta Feeryal.
a gefe guda ma Hajiya na nata,
a d'aya gefen kuwa labari daya isarwa Umma Karima kaukane kawai batayi.
Bappa Salihu baiyi kasa a gwuiwa ba ya diro Lagos bayan maganar su da Daddy da kwana biyu, ya iso da daddare.
bai bari sai gari ya waye ba ya iso sashin Hajiya.
Hajiya tayi mamakin ganin sa a irin wannan lokacin.
Hajiya ta cewa Kulu ta kawo masa abinci
Bappa Salihu ya ce
"Bar abincin ki Hajiya Hanne bacin abincinki bane ya kawo ni."
Hajiya ta d'aga hanci sama tana cewa
"Yoo wata maganar aka gaya maka ke nan, nifa in akan batun auren abokin turawa ne da aljanar yarinyar nan ne,
bafa zan zuba ido ina gani a kakabawa jikana damuwa ba."
"Yanzu fisabilillahi Hajiya Hanne, ya kyautu ke nan kirika jifan d'anki da irin wad'an nan munanan kalamai,
mutumin da ba wani cikakken lafiya yake da shi ba, kike son ki rika d'aga masa hankali,
haba Hajiya Hanne har duniyar tayi miki dad'i irin haka, yau idan ya fad'i ya mutu wayake da asara,
ni bazan yadda nasa iso akan wani dalilinki mara ma'ana ki salwantar min da rayuwar d'a ba,
sabo da Yaya Shitu Fiya bashi da rai shike nan kike so ke ki baje kafa kizamo kece uwar kece uban,
to kar ki manta muna nan mu rai uku masu rai, ba kuma zamu sa miki ido ki nima yiwa 'ya'yan mu baki akarin banza ba,
musamman shi jigon mu Abubakar,
wani irin shirme ne wannan,
kiyi gaggawar janye furucinki a kanshi in ba so kike ki zamo ajalinsa ba,
daga ya so had'a sunnar annabi shike nan kibi ki tada hankalin ki,
bakin ciki kike da sunnar annabin?."
Hajiya ta ce
"Ni dama ai ban masa baki ba na gaya masa ne kawai bai isa ya aurawa jikana aljana ba."
Bappa Salihu ya ce
"To ai ba jikan ki bane ke kad'ai, kin san munfiki iko da Abubakar."
Hajiya ta ce
"To kuzo ku zauna da 'ya'yan ku ai dama tun ba yauba kuke nuna min bushashshen iko da gadara, nifa gara na koma gun dangina ma, dana zauna ana gwada min wani gadara,
in dai aure ne da wannan aljanar ko bani gidan nan baza'ayi sa ba."
Hajiya ta mike ta shige d'aki ta soma tattare-tattaren kaya, tana mita.
Bappa Salihu ya mike ya fita yana girgiza kai da fad'in
"Hajiya Hanne ikon Allah."
Washegari da safe bayan sallar asuba Daddy ya shigo sashin Aunty, tana kan sallaya yazuba mata goro da minti a gaban ta.
da sauri ta d'ago ta ce
"Daddy wannan fa?."
zama ya yi a bakin gado sannan ya ce
"Na auren Abdulrahim da Feeryal ne da aka d'aura yanzu.......!
*Masha'allah anan wannan littafi na biyu ya kawo karshe sai mun had'u a littafi na na uku*🤗
*FEERYAL littafin kud'i ne ki biya domin karantawa cikin aminci 500 account no 3170524141 Rashida Salihu first bank.
ki tura shaidar biya ta Whatsapp number ta 08034690723 ina maraba da ku masoya na ni ma ina kaunar ku*🤗
Bari muzo mu raka FEERYAL d'akin ABDULRAHIM kowa ya tafi cikin shiri fa dan bamusan ya zamu tarar uwargida Kuraiba ba😂🤸⛹ï¸