Sashe 5
Feeryal Part 2 Complete Hausa Novel.t · about 8 min read
Feeryal ce kwance ke baccin ta cikin kwanciyar hankali,
kiran wayar ta dake karkashin pillow da take kai yata da ita.
mika tayi had'e da salati ta zura hannun ta karkashin pillow ta janyo wayar, batare da ta duba mai kiran nata ba ta kai wayar kunne idanunta a lumshe cikin muryar bacci ta ce
"Hello."
numfashi ya sauke mai sauti ya ce
"Har na cire rai da picking call d'ina, Feeryal me yasa bakya d'aga wayata?
i miss you Feeryal ko sau d'aya ki bani dama mana,
hope kina lafiya."
shiru tayi batayi magana ba, amma ta gane mai muryar.
Major Sadam ya rumtse idanunsa yana jin sonta na zaga jini da jijiyar sa ya ce
"Please Baby let me know kina sona."
nan ma shiru tayi wayar tana kunnen ta.
"Feeryal." ya kira sunan ta.
a hankali ta maida idanunta ta lumshe tana saurarar sa, nanma shiru batayi magana ba.
"Kinyi min izini anjima na kira ki bayan kin gama bacci?."
a hankali ta bud'e idanunta cikin tsiririyar muryar ta ta ce
"Eh."
cikin matukar jin dad'in amsashi da tayi ya ce
"Yes! thank you bye."
Ta sauke wayar a kunnen ta, ta mike zaune tare da yin hamma,
har yanzu bacci ne cike tam a idanunta,
sai dai tana jin yunwa dan daren jiya bata ci ba ta kwanta.
ta kalli agogo karfe 11 har da rabi.
ta zame blanket d'in da ke rufe a jikin ta.
ta zamo bakin gado ta mike ta nufi kofa ta fito,
daga ita sai riga da wandon bacci pink masu samtsi.
Tun daga bakin kofa ta ke fad'in
"Ammie yunwa Ammie yunwa nake ji."
a tsakir parlour ta tsaya tayi wani dogon mika mai had'e da hamma ta saki hannayen ta sharaf tana b'ata fuska ta cuno d'an karamin bakinta gaba cikin muryar shagwab'a tashiga bubbuga kafa a kasa wan da ilahirin jikin ta matsawa suke tana fad'in
"Ammieeeee ina cake d'ina."
ta nufi dinnin tana cigaba da kiran Ammien nata.
Aunty ta fito daga kichin da sauri ganin ta nufi dinning tana mussuke ido da hannayen ta bata ma kallon gaban ta.
Aunty ta ce
"Ke Feeryal."
cak ta tsaya bata kai ga karasawa dinning d'in ba.
ta juyo tana tura baki da fad'in
"Ammie yunwa nake ji."
"Maza je ki canza kayan jikin ki sai kiyi wanka kizo."
ta juya tana yarfe hannu cike da shagwab'a ta koma d'aki.
A hankali ya tura plt d'in abincin ya mike, Aunty da ta fito daga kichin rike da wani had'ad'd'en kula, perpesun naman kaza ne dayaji kayan had'i na musamman acikin kular.
ta ce "Har ka gama ne Abdurrahim?."
ya ce
"Eh nagama Aunty."
"Dama na karo maka wannan ne to gashi ka tafi da shi."
ta mika masa kular ya amsa tare da fad'in
"Nagode."
tayi murmushi, shiko ya juya ya fita.....!
Mommyn Twins ce
Da sauri Miemie ta shigo d'akin Feeryal ta isketa kwance tana aikin ta na buga game a waya.
ta hayo gadon tana fad'in
"Yanzu dama wayar nan tana hannun ki nake ta kira baki d'aga ba."
fuska ta marairaice ta ce
"Ayya Miemie wayar a nan na barta yanzu na shigo na d'auka."
"Shine kin ga kira bazaki bi kiran ba."
"Ai missed call d'in da yawa shine kawai ni ban duba ba."
"To Allah ya shirye ki watarana sai arziki ya kira ki kin ki d'agawa ya wuce ki."
dariya Feeryal ta yi ta ce
"Yi hakuri to, ya akayi?."
"Tun d'azu nake ta kiran ki nace miki ki shirya anjima zamuje, dinner yayar kawar mu, Safeenat Sa'id."
"Ke da su wa da su Ameerah wai? ni kam bazanje ba kuje abin ku, kitaho min da tsaraba."
Miemie ta harare ta ta ce
"Ke kenan idan akace aje guri kice bazakije ba, kullum kina kunshe a gida a d'aki,
ina ruwan ki da su Ameerah a kansu zaki zauna,
yarinya tayi miki ne nagaya miki karki kuskura ki kyale ta,
barina naje na fad'awa Aunty mun tabayi Daddy ya ce muje, idan ta ce kije kuma sai kin je."
ta zamo a gadon da sauri tayi d'akin Aunty.
Jim kad'an ta dawo ta ce
"To wlh Aunty ta ce muje, bari ma na ciro miki kayan da zaki sa kifara shiri kafin nima naje na shirya,
8 za'a fara a tashi 11 bikine na kowa da kowa bawai zallan 'yammata ba har da iyaye."
ido Feeryal ta ware ta ce
"Wai da ma da daddre ne bikin ma?."
"E mana kin ga yanzu za'ayi magariba ki tashi ki fara shiri, wannan kayan zaki saka."
ta aje mata wani dogon rigan dokakkiyar les, had'e da gyale da takalmin da zasu hau da kayan.
Miemie bata tafi ba sai da ta ga ta shige wanka.
Tana fita ta gabatar da sallar magariba da aka rigada aka kira.
kana ta zauna zaman shafa mai.
Aunty ta turo kofa ta shigo, ta karaso cikin d'akin tana fad'in
"Har yanzu baki gama shirin ba."
fuska ta marairai ce ta ce
"Nayi wanka fa Ammie kaya zan sa."
Aunty ta d'aga kayan da Miemie ta ciro mata dasu aje a bakin gado ta dube ta ta ce
"Ya banga bra a cikin kayan ba."
"Ammieee jiya fa nasa."
"Dan jiya ansa sai yau kuma baza a sa ba, oh ni naga ikon Allah,
laifin Maryam ce."
wayarta ta d'aga ta lalub'o lambar Maryam tana d'agawa ta ce
"Ya miki kyau Maryam da kika kasa gwada mata aibun rashin sa bra."
"Ayya Aunty Faty wai kullum sai an d'aura laifin a kaina, kullum fa laifi na kike gani."
"Ai bazan fasa ganin laifin ki ba har sai randa ta koyi sawa da kanta batare da an ce tasa ba."
Aunty ta kashe wayar tana cewa
"Kullum bra ya kasan ce a jikin ki kwanciya ce kawai zaki cire sa."
baki ta turo tana marairaice fuska cike da shagwab'a.
Aunty ta ciro mata underwear da pant da bra.
ta ce
"Taso maza ki saka."
tana tsaye ta saka ta tayata ta karasa shirin.
da kanta tayi mata d'aurin d'an kwalli,
Feeryal na zaune gaban mirror Aunty tad'au sarkar da 'yan kunne na gold ta saka mata,
man lips kad'ai ta saka ko pauda babu a fuskarta.
amma kyawunta ya dad'a bayyana a gareta ya d'are wacce akayi awa 3 ana mata makeup.
Aunty ta tsaya tana kare mata kallo sai fad'in
"Tabarakallah masha'allah."
ta ke.
ta mika mata gyale ta yafa, ta gyara mata zaman gyalen, kana ta miko mata takalmin da Miemie ta d'auko mata, baya da tudu sosai ta zura a kyawawan fararen kafafunta.
ta fesa mata turare masu sanyin kamshi.
Aunty ta dubeta cike da farinciki ta ce
"Miqe na ganki d'iyar albarka."
ta miqe tsaye tana dariya.
Aunty tayi mata hoto da wayarta tana ta yaba kyawun ta.
Miemie ta shigo da sauri tana fad'in
"Allah dai yasa kin gama Feeryal."
ido Miemie ta waro ta ja ta tsaya tana kare mata kallo baki bud'e.
ta ce
"Kin ganki kuwa kamar ke ce amaryar."
Feeryal ta saki sassanyar murmurshi.
Miemie ta janyo hannunta ta ce
"Taho mu tafi mu ake jira.
"Miemie kada ku wuce karfe 10, ko ba'a tashiba ku dawo gida, kuma ku kula sosai dan Allah kada ku biyewa samaruka marasa d'a'an nan,
wai tukun na ma da gaske Daddy shi ya ce kuje."
cewar Aunty tana tsare Miemie da ido.
Miemie ta ce
"Allah Aunty shi ya ce muje tun da safe muka tambaye shi, ai ya ce ma zai je gurin d'aurin auren d'azu bayan sallar azahar wai Abba'n Feenat ya gayyace sa."
Aunty ta jijjiga kai dan tasan Alhaji Sa'id mahaifin Safeenat, da suke kira da Feenat suna d'an huld'a da Daddy.
ta ce "To shike nan sai kun dawo ku kula sosai dan Allah a fita kuma da addu'a."
suka ce to.
Suna fita suka hangi su Ameerah a jikin mota, da wasu kawayen su biyo.
Sahla ta tab'a Ameerah ta ce
"Kalli can ki ga wacce Miemie ta d'au ko."
Nabila ta ce
"Kan uba wa zata bi, lallai ma Miemie nan shine har da wani gayyato ta."
Ameerah ko tun kafin su karasu take aika musu harara.
kawayen nasu kuwa baki suka bud'e suna kallon Feeryal tare da fad'in
"Wow."
Ameerah ta dad'a b'ata rai har suka karaso in da suke.
ta ja dogon tsaki ta harari Feeryal sama da kasa sannan ta ce
"Ke Miemie wai ya za'ayi ki d'auko wannan kice zata bimu."
"Ina ruwan ki akan ki zata tafi."
cewar Miemie tana yi mata kallon sama da kasa.
Ameerah ta wani dalla musu harara ta ce
"To wlh ba a motar mu ba, ki dai san motar da zaki sata."
Nabila ta ce
"Gaya mata dai dan wannan motar ubanmu ne ya siya ba uban wata ba."
Miemie ta ce
"Ina dai babu wacce ta siyi motar a cikin ku,
to ai alhamdulillahi sai ku bari sai ko wacce acikin ku ta siya da kud'in ta kafin tayi gadara da shi,
na rantse dan dai kawai motar nan bazata d'auke mu bane dukan mu da wlh in mutuwa zakuyi sai ta shiga,
mttss zo muje Feeryal direban Ammah ya kaimu, daga nan ku had'iye motar a cikin ku,
in kuma ba haka ba to wlh duk randa fita ta kama mu sai ta shiga, in zaku mutu sai dai ku mutu."
taja Feeryal sukayi sashin Ammah.
kiran wayar ta dake karkashin pillow da take kai yata da ita.
mika tayi had'e da salati ta zura hannun ta karkashin pillow ta janyo wayar, batare da ta duba mai kiran nata ba ta kai wayar kunne idanunta a lumshe cikin muryar bacci ta ce
"Hello."
numfashi ya sauke mai sauti ya ce
"Har na cire rai da picking call d'ina, Feeryal me yasa bakya d'aga wayata?
i miss you Feeryal ko sau d'aya ki bani dama mana,
hope kina lafiya."
shiru tayi batayi magana ba, amma ta gane mai muryar.
Major Sadam ya rumtse idanunsa yana jin sonta na zaga jini da jijiyar sa ya ce
"Please Baby let me know kina sona."
nan ma shiru tayi wayar tana kunnen ta.
"Feeryal." ya kira sunan ta.
a hankali ta maida idanunta ta lumshe tana saurarar sa, nanma shiru batayi magana ba.
"Kinyi min izini anjima na kira ki bayan kin gama bacci?."
a hankali ta bud'e idanunta cikin tsiririyar muryar ta ta ce
"Eh."
cikin matukar jin dad'in amsashi da tayi ya ce
"Yes! thank you bye."
Ta sauke wayar a kunnen ta, ta mike zaune tare da yin hamma,
har yanzu bacci ne cike tam a idanunta,
sai dai tana jin yunwa dan daren jiya bata ci ba ta kwanta.
ta kalli agogo karfe 11 har da rabi.
ta zame blanket d'in da ke rufe a jikin ta.
ta zamo bakin gado ta mike ta nufi kofa ta fito,
daga ita sai riga da wandon bacci pink masu samtsi.
Tun daga bakin kofa ta ke fad'in
"Ammie yunwa Ammie yunwa nake ji."
a tsakir parlour ta tsaya tayi wani dogon mika mai had'e da hamma ta saki hannayen ta sharaf tana b'ata fuska ta cuno d'an karamin bakinta gaba cikin muryar shagwab'a tashiga bubbuga kafa a kasa wan da ilahirin jikin ta matsawa suke tana fad'in
"Ammieeeee ina cake d'ina."
ta nufi dinnin tana cigaba da kiran Ammien nata.
Aunty ta fito daga kichin da sauri ganin ta nufi dinning tana mussuke ido da hannayen ta bata ma kallon gaban ta.
Aunty ta ce
"Ke Feeryal."
cak ta tsaya bata kai ga karasawa dinning d'in ba.
ta juyo tana tura baki da fad'in
"Ammie yunwa nake ji."
"Maza je ki canza kayan jikin ki sai kiyi wanka kizo."
ta juya tana yarfe hannu cike da shagwab'a ta koma d'aki.
A hankali ya tura plt d'in abincin ya mike, Aunty da ta fito daga kichin rike da wani had'ad'd'en kula, perpesun naman kaza ne dayaji kayan had'i na musamman acikin kular.
ta ce "Har ka gama ne Abdurrahim?."
ya ce
"Eh nagama Aunty."
"Dama na karo maka wannan ne to gashi ka tafi da shi."
ta mika masa kular ya amsa tare da fad'in
"Nagode."
tayi murmushi, shiko ya juya ya fita.....!
Mommyn Twins ce
Da sauri Miemie ta shigo d'akin Feeryal ta isketa kwance tana aikin ta na buga game a waya.
ta hayo gadon tana fad'in
"Yanzu dama wayar nan tana hannun ki nake ta kira baki d'aga ba."
fuska ta marairaice ta ce
"Ayya Miemie wayar a nan na barta yanzu na shigo na d'auka."
"Shine kin ga kira bazaki bi kiran ba."
"Ai missed call d'in da yawa shine kawai ni ban duba ba."
"To Allah ya shirye ki watarana sai arziki ya kira ki kin ki d'agawa ya wuce ki."
dariya Feeryal ta yi ta ce
"Yi hakuri to, ya akayi?."
"Tun d'azu nake ta kiran ki nace miki ki shirya anjima zamuje, dinner yayar kawar mu, Safeenat Sa'id."
"Ke da su wa da su Ameerah wai? ni kam bazanje ba kuje abin ku, kitaho min da tsaraba."
Miemie ta harare ta ta ce
"Ke kenan idan akace aje guri kice bazakije ba, kullum kina kunshe a gida a d'aki,
ina ruwan ki da su Ameerah a kansu zaki zauna,
yarinya tayi miki ne nagaya miki karki kuskura ki kyale ta,
barina naje na fad'awa Aunty mun tabayi Daddy ya ce muje, idan ta ce kije kuma sai kin je."
ta zamo a gadon da sauri tayi d'akin Aunty.
Jim kad'an ta dawo ta ce
"To wlh Aunty ta ce muje, bari ma na ciro miki kayan da zaki sa kifara shiri kafin nima naje na shirya,
8 za'a fara a tashi 11 bikine na kowa da kowa bawai zallan 'yammata ba har da iyaye."
ido Feeryal ta ware ta ce
"Wai da ma da daddre ne bikin ma?."
"E mana kin ga yanzu za'ayi magariba ki tashi ki fara shiri, wannan kayan zaki saka."
ta aje mata wani dogon rigan dokakkiyar les, had'e da gyale da takalmin da zasu hau da kayan.
Miemie bata tafi ba sai da ta ga ta shige wanka.
Tana fita ta gabatar da sallar magariba da aka rigada aka kira.
kana ta zauna zaman shafa mai.
Aunty ta turo kofa ta shigo, ta karaso cikin d'akin tana fad'in
"Har yanzu baki gama shirin ba."
fuska ta marairai ce ta ce
"Nayi wanka fa Ammie kaya zan sa."
Aunty ta d'aga kayan da Miemie ta ciro mata dasu aje a bakin gado ta dube ta ta ce
"Ya banga bra a cikin kayan ba."
"Ammieee jiya fa nasa."
"Dan jiya ansa sai yau kuma baza a sa ba, oh ni naga ikon Allah,
laifin Maryam ce."
wayarta ta d'aga ta lalub'o lambar Maryam tana d'agawa ta ce
"Ya miki kyau Maryam da kika kasa gwada mata aibun rashin sa bra."
"Ayya Aunty Faty wai kullum sai an d'aura laifin a kaina, kullum fa laifi na kike gani."
"Ai bazan fasa ganin laifin ki ba har sai randa ta koyi sawa da kanta batare da an ce tasa ba."
Aunty ta kashe wayar tana cewa
"Kullum bra ya kasan ce a jikin ki kwanciya ce kawai zaki cire sa."
baki ta turo tana marairaice fuska cike da shagwab'a.
Aunty ta ciro mata underwear da pant da bra.
ta ce
"Taso maza ki saka."
tana tsaye ta saka ta tayata ta karasa shirin.
da kanta tayi mata d'aurin d'an kwalli,
Feeryal na zaune gaban mirror Aunty tad'au sarkar da 'yan kunne na gold ta saka mata,
man lips kad'ai ta saka ko pauda babu a fuskarta.
amma kyawunta ya dad'a bayyana a gareta ya d'are wacce akayi awa 3 ana mata makeup.
Aunty ta tsaya tana kare mata kallo sai fad'in
"Tabarakallah masha'allah."
ta ke.
ta mika mata gyale ta yafa, ta gyara mata zaman gyalen, kana ta miko mata takalmin da Miemie ta d'auko mata, baya da tudu sosai ta zura a kyawawan fararen kafafunta.
ta fesa mata turare masu sanyin kamshi.
Aunty ta dubeta cike da farinciki ta ce
"Miqe na ganki d'iyar albarka."
ta miqe tsaye tana dariya.
Aunty tayi mata hoto da wayarta tana ta yaba kyawun ta.
Miemie ta shigo da sauri tana fad'in
"Allah dai yasa kin gama Feeryal."
ido Miemie ta waro ta ja ta tsaya tana kare mata kallo baki bud'e.
ta ce
"Kin ganki kuwa kamar ke ce amaryar."
Feeryal ta saki sassanyar murmurshi.
Miemie ta janyo hannunta ta ce
"Taho mu tafi mu ake jira.
"Miemie kada ku wuce karfe 10, ko ba'a tashiba ku dawo gida, kuma ku kula sosai dan Allah kada ku biyewa samaruka marasa d'a'an nan,
wai tukun na ma da gaske Daddy shi ya ce kuje."
cewar Aunty tana tsare Miemie da ido.
Miemie ta ce
"Allah Aunty shi ya ce muje tun da safe muka tambaye shi, ai ya ce ma zai je gurin d'aurin auren d'azu bayan sallar azahar wai Abba'n Feenat ya gayyace sa."
Aunty ta jijjiga kai dan tasan Alhaji Sa'id mahaifin Safeenat, da suke kira da Feenat suna d'an huld'a da Daddy.
ta ce "To shike nan sai kun dawo ku kula sosai dan Allah a fita kuma da addu'a."
suka ce to.
Suna fita suka hangi su Ameerah a jikin mota, da wasu kawayen su biyo.
Sahla ta tab'a Ameerah ta ce
"Kalli can ki ga wacce Miemie ta d'au ko."
Nabila ta ce
"Kan uba wa zata bi, lallai ma Miemie nan shine har da wani gayyato ta."
Ameerah ko tun kafin su karasu take aika musu harara.
kawayen nasu kuwa baki suka bud'e suna kallon Feeryal tare da fad'in
"Wow."
Ameerah ta dad'a b'ata rai har suka karaso in da suke.
ta ja dogon tsaki ta harari Feeryal sama da kasa sannan ta ce
"Ke Miemie wai ya za'ayi ki d'auko wannan kice zata bimu."
"Ina ruwan ki akan ki zata tafi."
cewar Miemie tana yi mata kallon sama da kasa.
Ameerah ta wani dalla musu harara ta ce
"To wlh ba a motar mu ba, ki dai san motar da zaki sata."
Nabila ta ce
"Gaya mata dai dan wannan motar ubanmu ne ya siya ba uban wata ba."
Miemie ta ce
"Ina dai babu wacce ta siyi motar a cikin ku,
to ai alhamdulillahi sai ku bari sai ko wacce acikin ku ta siya da kud'in ta kafin tayi gadara da shi,
na rantse dan dai kawai motar nan bazata d'auke mu bane dukan mu da wlh in mutuwa zakuyi sai ta shiga,
mttss zo muje Feeryal direban Ammah ya kaimu, daga nan ku had'iye motar a cikin ku,
in kuma ba haka ba to wlh duk randa fita ta kama mu sai ta shiga, in zaku mutu sai dai ku mutu."
taja Feeryal sukayi sashin Ammah.