Sashe 42
Feeryal Part 2 Complete Hausa Novel.t · about 8 min read
Daddy na zaune a parlour'n Hajiya bayan sun gaisa, Hajiya tayi ta kawo masa hirarraki, yana amsata amma gaba d'aya hankalin sa na ga maganar da take cikin ransa, wanda yake tunanin tinkarar Hajiyar da shi.
Daddy ya gyara zama ya fuskanci ta da kyau ya yi karfin halin soma magana.
r"Hajiya dama wata magana nake tafe da shi, amma bansan da wace fuska zaki fiskanci lamarin ba,
amma Hajiya dan Allah ina so ki fahimce ni, a matsayin ki na uwa a gare ni, nasan kinfi kowa son ganin farinciki na,
yin tawassali da Allah babu abin da yafishi dad'i da samin nasara a rayuwa,
ka yadda Allah shike da ikon yin komai a duniyar nan, duk abin da ya sami bawa da sanin ubangiji duk kuma abun da kaga ya faru da kai dama rubucacce ne cikin kaddarar ka sai dai wani yazamo sila,
shirka haramun ce babu laifin da Allah baya yafewa bawa har idan yamutu yana aikatashi face shirka,
haramun ne shaidar zur abin da baka da tabbaci akan sa ka tabbatar da cewa hakan ne."
da sauri Hajiya ta ce
"To Abubakar ni ban gane in da wanna batun naka ya dosa ba,
wai wa'azi kake yi min ko me?
tun kafin kazo duniya nake jin wa'azi,
ai naga kamar shirin fita kayi katashi ka tafi Allah ya bada sa'a, wa'azi kam ai andad'e ana jin sa."
Daddy ya d'an yi shiru da wasi-wasi tap cikin ransa ya gyara zama yana son dai-dai nutsuwar sa, kai tsaye yasoma fad'in
"Hajiya ba haka ba,
abin da nake tafe da shi nake son sanar miki shine,
ina so na bawa Abdulrahim auren FEERYAL, saboda wasu dalilai idan da zaki fahimceni da zan zayyano miki dalilan nawa, kuma nasan zaki bani goyon baya..."
wani irin zabura Hajiya tayi tamkar taga wani muhimmin mugun abin tsoratarwa.
wani irin bugawa kirjin Ajmal daya sako kai zai shigo parlour'n ya yi har sai da ya kai hannu ya dafe kirjin nasa, dake bugu dum-dum-dum!.
wani irin bakin abu yaga ya gilma masa a ido, ya juya da sauri ya koma side d'in su.
a parlour'n kuwa Hajiya
ta mike tsaye a zabure take fad'in
"Abubakar kasan me kake fad'a kuwa! ko kunne na ne yajiyo min ba dai-dai ba?
aljanar kake son aurawa abokin turawa!
to bari kaji wlh ko bayan ba raina banyarda ka aura masa ita ba,
bama shi ba ko wani d'a a gidan nan kai koma waye har idan da dangantaka sakani na da shi, wlh ban yarda ba ban yafe maka ba Abubakar idan ka aurawa wa wani jikana,
wannan mayyar aljanar ruwan bare jikana na fari abokin turawa!."
Daddy da yaji kamar ciwon sa zai tashi sabar tashin hankalin da ya shiga agurin,
dama yasan da kamar wuya Hajiya ta yadda.
ya dafe kirjinsa da ya soma yi masa zugi ya ce
"Hajiya da zaki fahimce ni ki bani dama na kawo miki dalilai na."
"Rufamin baki dalilan banza da lilan hofi,
ai baka da wani dalilin da zaka gayamin akan auren mutum da aljana,
ai in zaka mutu babu abin da zai sa ayi auren nan, ko mutuwa zakayi sai dai ka mutu Abubakar."
Hajiya ta juya ta shige d'aki tana falle zane tana gyara d'aurawa sabar masifa.
bata karasa ciki ba takuma juyowa ta dawo
"Ni za'a kawowa zancen banza zancen iska,
to maza-maza kaje ka fita da yarinyar nan a gidan nan yanzu, idan kuma ba haka ba ni nafita na bar maka gidan ka,
baka zab'eta a kaina ba ai dama shi yasa ka masa kan ta zauna wai ana bincike,
ai ita yakamata ayi bincike a kanta ba wasu ba,
to wlh idan baka kori yarinyar nan ba saina sassab'a maka."
Hajiya takama jan hanci tana cigaba da fad'in
"Dama ashe abin da yasa kaki rabata da gidan nan ke nan, Abubakar nasake fad'a maka in zaka mutu abokin turawa bazai auri yarinyar nan ba,
yaushene ma yayi aure da za'a sake masa wani auren, kai wlh ko shekara goma ya yi da yin auren fari idan wannan aljanar yarinyar ce bazaiyi na biyu da ita ba,
tashi maza ka fita min anan ni zaka kawo wa tsiya."
Daddy ya mike jiki ba kwari ya fita.
A b'angare Ajmal kuwa d'akin sa ya shige ya kulle kansa ciki.
ya kafa kansa jikin garu-bango yana jin wani irin azaba cikin ransa.
yarika dukan jikin garu-bango yana fad'in
"Why Why why! ya akayi nayi nauyin baki ne, ni nake son FEERYAL Daddy ba Ya Abdulrahim ba."
ido ya rumtse da karfi tare da buga kanta a jikin bongo, sai kuma ya zame kasa ya zauna ya mike kafafunsa, ya jingina bayansa da jikin garu yana juya kai hannunsa na dafe da gefen zuciyar sa, ya yin da idanunsa ke a rumtse.
Daddy kuwa yana fita ya shiga mota direba yakai shi office sai dai me yakasa zama office d'in ya fito yasa direba ya maida shi gida.
Aunty ta mike tsaye da sauri ganin Daddy ya ya shigo bedroom d'in ta.
ta ce
"Daddy ba dai mantuwa kayi ba, naga ka dawo da wuri."
zama ya yi yana cewa
"Zauna Fad'imatu muyi magana."
Aunty ta zauna tana kallon shi da alamun soma shiga fargaba.
"Fad'imatu."
Daddy ya kira sunanta.
"Na'am Daddy."
ta amsa zuciyar ta na d'an harbawa.
"Jiya magabatan wannan yaro mai son Feeryal Major Sadam sunzo, nasa akayi musu masauki a masaukin ba'i na cikin company;
sunzo nima masa auren ta sannan sun taho da shirin su sunaso a yanka musu sadaki, da sa rana duk a jiyan, dan suna tafe da kud'i idan aka yanka sadaki subiya nan take, a samusu ranar da bazai wuce wata guda ba.
sai dai ni na ce musu nayi mata miji tuntuni,
kuma a halin da ake ciki zan aurar da ita wa mijin da nayi mata nan da kwanaki kad'an,
Fad'imatu na sami Hajiya da ma nasan ba lallai ne ta aminta da abun da naje mata da shi ba,
ina da yakinin bani kad'ai ba kowa zai amfana da abinda nake son aiwatar wa."
Aunty ta jinjina kai kamar ko da yaushe acikin yadda da maigidan nata take ta ce
"Insha'allahu duk abin da kake son aiwatarwa alkhairi ne,
amma mene ne shi d'in Daddy?."
numfashi ya sauke sannan ya ce
"Zan aurawa Abdulrahim Feeryal hakan ne kawai zai kaini ga tsira daga farmakin da ake kawo min cikin bacci, wanda bansan ta ina ne yake zuwa ba."
zumbur Aunty ta mike tana girgiza kai da fad'in
"Aa Daddy dan Allah kar ka soma, dan Allah kar kabar maganar nan ta fita na roke ka, kaje ka sami Hajiya ka ce mata dama fad'a kawai kayi ba zartarwa zakayi ba;
Daddy ka rufa min asiri ya zanyi da rayuwa ta a cikin gidan nan idan wannan maganar ta fita,
ya zanyi da Hajiya da Hajiya Halima da sauran 'yan gidan nan, Daddy so kake na tattara na tafi ko, dani da Feeryal d'in duka,
dan Allah Daddy kar ka sake wannan maganar, Feeryal kam ma tana da wanda zata aura Major Sadam, ka bashi auren ta kawai."
"Fad'imatu zauna dan Allah."
Daddy ya fad'a yana ruko hannunta.
kai ta girgiza ta ce
"Aa Daddy tsoro nake ji dan Allah ka janye batun nan."
"Ke ma ashe bazaki saurare ni kiji dalilai na ba,
Fad'imatu kaf duniya babu wanda yake fahimtata sama da ke, kin fi kowa sanin damuwa na, zauna dan Allah."
jiki a sanyaye ta koma in da ta tashi.
ya dube ta da kyau kana ya soma magana
"Na jima ina tunanin wanda zan zab'awa Feeryal a matsayin abokin rayuwarta, tun lokacin da ta fara tasowa,
nake yi mata fatan nagartaccen miji, wanda zai kula da ita yaji kan lamuranta,
a daren da aka rasa Feeryal ranar auren Abdulrahim,
yasa kafa yafita nemo ta batare da wani ya sani ba, yaje ya kwato ta a hannun wad'an da suka so b'ata mata rayuwa,
lokacin da ya dawowa da ita gidan nan tun a ranar naji shine ya dace da rayuwarta."
zama Daddy ya gyara kana ya kira sunan ta
"Fad'imatu kinsan wa yake citona cikin munanan mafarkan da nake, kuma me nake ji ake fad'a a kanta,
Feeryal ce;
cemin ake itace hasken kub'uta ta kar na barta tayi nesa daga rayuwa ta."
a hankali yashiga bata labarin abubuwan da yake gani cikin mafarki wanda dama bai tab'a zama ya fad'a mata irin abubuwan da yake gani ba, sai dai idan ya farka ya ce mata, zasu kashe shi.
sannan ya d'aura da fad'in
"Dama ina da shirin aura mishi ita, tun a daren ranar auren shi naga dacewar hakan,
dalilin da yasa na dad'a karfafawa kuwa a shine mafarki na,
Fad'imatu shin kina so na dad'a kasancewa cikin yanayin da na shiga a kwanakin baya ne,
ki karfafa min gwuiwa mana,
ina ji a raina da gaske Feeryal alkhairi ce a rayuwar mu,
zamanta a cikin mu alhaki ne."
Aunty ta sauke numfashi ta ce
"Daddy bana fatan ka sake kasancewa cikin halin da ka shiga a baya,
amma Daddy Hajiya fa bazata tab'a amincewa ba, sannan ita kanta uwar Abdulrahim Hajiya Halima bazata amince ba,
sannan shi kansa Abdulrahim d'in da
'yan'uwan ka da kowa da kowa ma, ba lallai ne su amin ta ba,
me zai hana idan ta auri Major Sadam d'in ace ya zauna da ita a garin nan, ai kaga muna tare da ita ke nan bamuyi nesa da juna ba."
Daddy ya ce
"Amincewar Hajiya kad'ai nake bukata, bayan ita bana bukatar kowa sai ya aminta."
Aunty tayi shiru tana tunanin taya hakan zata kasance, lallai kuwa matsala yanzu ne zata kunno kai.
Da kyar Ajmal ya samu ya rarrashi zuciyarsa, yafito cikin 'yan'uwan sa.
Daddy ya gyara zama ya fuskanci ta da kyau ya yi karfin halin soma magana.
r"Hajiya dama wata magana nake tafe da shi, amma bansan da wace fuska zaki fiskanci lamarin ba,
amma Hajiya dan Allah ina so ki fahimce ni, a matsayin ki na uwa a gare ni, nasan kinfi kowa son ganin farinciki na,
yin tawassali da Allah babu abin da yafishi dad'i da samin nasara a rayuwa,
ka yadda Allah shike da ikon yin komai a duniyar nan, duk abin da ya sami bawa da sanin ubangiji duk kuma abun da kaga ya faru da kai dama rubucacce ne cikin kaddarar ka sai dai wani yazamo sila,
shirka haramun ce babu laifin da Allah baya yafewa bawa har idan yamutu yana aikatashi face shirka,
haramun ne shaidar zur abin da baka da tabbaci akan sa ka tabbatar da cewa hakan ne."
da sauri Hajiya ta ce
"To Abubakar ni ban gane in da wanna batun naka ya dosa ba,
wai wa'azi kake yi min ko me?
tun kafin kazo duniya nake jin wa'azi,
ai naga kamar shirin fita kayi katashi ka tafi Allah ya bada sa'a, wa'azi kam ai andad'e ana jin sa."
Daddy ya d'an yi shiru da wasi-wasi tap cikin ransa ya gyara zama yana son dai-dai nutsuwar sa, kai tsaye yasoma fad'in
"Hajiya ba haka ba,
abin da nake tafe da shi nake son sanar miki shine,
ina so na bawa Abdulrahim auren FEERYAL, saboda wasu dalilai idan da zaki fahimceni da zan zayyano miki dalilan nawa, kuma nasan zaki bani goyon baya..."
wani irin zabura Hajiya tayi tamkar taga wani muhimmin mugun abin tsoratarwa.
wani irin bugawa kirjin Ajmal daya sako kai zai shigo parlour'n ya yi har sai da ya kai hannu ya dafe kirjin nasa, dake bugu dum-dum-dum!.
wani irin bakin abu yaga ya gilma masa a ido, ya juya da sauri ya koma side d'in su.
a parlour'n kuwa Hajiya
ta mike tsaye a zabure take fad'in
"Abubakar kasan me kake fad'a kuwa! ko kunne na ne yajiyo min ba dai-dai ba?
aljanar kake son aurawa abokin turawa!
to bari kaji wlh ko bayan ba raina banyarda ka aura masa ita ba,
bama shi ba ko wani d'a a gidan nan kai koma waye har idan da dangantaka sakani na da shi, wlh ban yarda ba ban yafe maka ba Abubakar idan ka aurawa wa wani jikana,
wannan mayyar aljanar ruwan bare jikana na fari abokin turawa!."
Daddy da yaji kamar ciwon sa zai tashi sabar tashin hankalin da ya shiga agurin,
dama yasan da kamar wuya Hajiya ta yadda.
ya dafe kirjinsa da ya soma yi masa zugi ya ce
"Hajiya da zaki fahimce ni ki bani dama na kawo miki dalilai na."
"Rufamin baki dalilan banza da lilan hofi,
ai baka da wani dalilin da zaka gayamin akan auren mutum da aljana,
ai in zaka mutu babu abin da zai sa ayi auren nan, ko mutuwa zakayi sai dai ka mutu Abubakar."
Hajiya ta juya ta shige d'aki tana falle zane tana gyara d'aurawa sabar masifa.
bata karasa ciki ba takuma juyowa ta dawo
"Ni za'a kawowa zancen banza zancen iska,
to maza-maza kaje ka fita da yarinyar nan a gidan nan yanzu, idan kuma ba haka ba ni nafita na bar maka gidan ka,
baka zab'eta a kaina ba ai dama shi yasa ka masa kan ta zauna wai ana bincike,
ai ita yakamata ayi bincike a kanta ba wasu ba,
to wlh idan baka kori yarinyar nan ba saina sassab'a maka."
Hajiya takama jan hanci tana cigaba da fad'in
"Dama ashe abin da yasa kaki rabata da gidan nan ke nan, Abubakar nasake fad'a maka in zaka mutu abokin turawa bazai auri yarinyar nan ba,
yaushene ma yayi aure da za'a sake masa wani auren, kai wlh ko shekara goma ya yi da yin auren fari idan wannan aljanar yarinyar ce bazaiyi na biyu da ita ba,
tashi maza ka fita min anan ni zaka kawo wa tsiya."
Daddy ya mike jiki ba kwari ya fita.
A b'angare Ajmal kuwa d'akin sa ya shige ya kulle kansa ciki.
ya kafa kansa jikin garu-bango yana jin wani irin azaba cikin ransa.
yarika dukan jikin garu-bango yana fad'in
"Why Why why! ya akayi nayi nauyin baki ne, ni nake son FEERYAL Daddy ba Ya Abdulrahim ba."
ido ya rumtse da karfi tare da buga kanta a jikin bongo, sai kuma ya zame kasa ya zauna ya mike kafafunsa, ya jingina bayansa da jikin garu yana juya kai hannunsa na dafe da gefen zuciyar sa, ya yin da idanunsa ke a rumtse.
Daddy kuwa yana fita ya shiga mota direba yakai shi office sai dai me yakasa zama office d'in ya fito yasa direba ya maida shi gida.
Aunty ta mike tsaye da sauri ganin Daddy ya ya shigo bedroom d'in ta.
ta ce
"Daddy ba dai mantuwa kayi ba, naga ka dawo da wuri."
zama ya yi yana cewa
"Zauna Fad'imatu muyi magana."
Aunty ta zauna tana kallon shi da alamun soma shiga fargaba.
"Fad'imatu."
Daddy ya kira sunanta.
"Na'am Daddy."
ta amsa zuciyar ta na d'an harbawa.
"Jiya magabatan wannan yaro mai son Feeryal Major Sadam sunzo, nasa akayi musu masauki a masaukin ba'i na cikin company;
sunzo nima masa auren ta sannan sun taho da shirin su sunaso a yanka musu sadaki, da sa rana duk a jiyan, dan suna tafe da kud'i idan aka yanka sadaki subiya nan take, a samusu ranar da bazai wuce wata guda ba.
sai dai ni na ce musu nayi mata miji tuntuni,
kuma a halin da ake ciki zan aurar da ita wa mijin da nayi mata nan da kwanaki kad'an,
Fad'imatu na sami Hajiya da ma nasan ba lallai ne ta aminta da abun da naje mata da shi ba,
ina da yakinin bani kad'ai ba kowa zai amfana da abinda nake son aiwatar wa."
Aunty ta jinjina kai kamar ko da yaushe acikin yadda da maigidan nata take ta ce
"Insha'allahu duk abin da kake son aiwatarwa alkhairi ne,
amma mene ne shi d'in Daddy?."
numfashi ya sauke sannan ya ce
"Zan aurawa Abdulrahim Feeryal hakan ne kawai zai kaini ga tsira daga farmakin da ake kawo min cikin bacci, wanda bansan ta ina ne yake zuwa ba."
zumbur Aunty ta mike tana girgiza kai da fad'in
"Aa Daddy dan Allah kar ka soma, dan Allah kar kabar maganar nan ta fita na roke ka, kaje ka sami Hajiya ka ce mata dama fad'a kawai kayi ba zartarwa zakayi ba;
Daddy ka rufa min asiri ya zanyi da rayuwa ta a cikin gidan nan idan wannan maganar ta fita,
ya zanyi da Hajiya da Hajiya Halima da sauran 'yan gidan nan, Daddy so kake na tattara na tafi ko, dani da Feeryal d'in duka,
dan Allah Daddy kar ka sake wannan maganar, Feeryal kam ma tana da wanda zata aura Major Sadam, ka bashi auren ta kawai."
"Fad'imatu zauna dan Allah."
Daddy ya fad'a yana ruko hannunta.
kai ta girgiza ta ce
"Aa Daddy tsoro nake ji dan Allah ka janye batun nan."
"Ke ma ashe bazaki saurare ni kiji dalilai na ba,
Fad'imatu kaf duniya babu wanda yake fahimtata sama da ke, kin fi kowa sanin damuwa na, zauna dan Allah."
jiki a sanyaye ta koma in da ta tashi.
ya dube ta da kyau kana ya soma magana
"Na jima ina tunanin wanda zan zab'awa Feeryal a matsayin abokin rayuwarta, tun lokacin da ta fara tasowa,
nake yi mata fatan nagartaccen miji, wanda zai kula da ita yaji kan lamuranta,
a daren da aka rasa Feeryal ranar auren Abdulrahim,
yasa kafa yafita nemo ta batare da wani ya sani ba, yaje ya kwato ta a hannun wad'an da suka so b'ata mata rayuwa,
lokacin da ya dawowa da ita gidan nan tun a ranar naji shine ya dace da rayuwarta."
zama Daddy ya gyara kana ya kira sunan ta
"Fad'imatu kinsan wa yake citona cikin munanan mafarkan da nake, kuma me nake ji ake fad'a a kanta,
Feeryal ce;
cemin ake itace hasken kub'uta ta kar na barta tayi nesa daga rayuwa ta."
a hankali yashiga bata labarin abubuwan da yake gani cikin mafarki wanda dama bai tab'a zama ya fad'a mata irin abubuwan da yake gani ba, sai dai idan ya farka ya ce mata, zasu kashe shi.
sannan ya d'aura da fad'in
"Dama ina da shirin aura mishi ita, tun a daren ranar auren shi naga dacewar hakan,
dalilin da yasa na dad'a karfafawa kuwa a shine mafarki na,
Fad'imatu shin kina so na dad'a kasancewa cikin yanayin da na shiga a kwanakin baya ne,
ki karfafa min gwuiwa mana,
ina ji a raina da gaske Feeryal alkhairi ce a rayuwar mu,
zamanta a cikin mu alhaki ne."
Aunty ta sauke numfashi ta ce
"Daddy bana fatan ka sake kasancewa cikin halin da ka shiga a baya,
amma Daddy Hajiya fa bazata tab'a amincewa ba, sannan ita kanta uwar Abdulrahim Hajiya Halima bazata amince ba,
sannan shi kansa Abdulrahim d'in da
'yan'uwan ka da kowa da kowa ma, ba lallai ne su amin ta ba,
me zai hana idan ta auri Major Sadam d'in ace ya zauna da ita a garin nan, ai kaga muna tare da ita ke nan bamuyi nesa da juna ba."
Daddy ya ce
"Amincewar Hajiya kad'ai nake bukata, bayan ita bana bukatar kowa sai ya aminta."
Aunty tayi shiru tana tunanin taya hakan zata kasance, lallai kuwa matsala yanzu ne zata kunno kai.
Da kyar Ajmal ya samu ya rarrashi zuciyarsa, yafito cikin 'yan'uwan sa.