Sashe 13
Feeryal Part 2 Complete Hausa Novel.t · about 8 min read
Miemie ta bita da sauri Feeryal bata tsaya ba sai da ta fice a farfajiyar side d'in gaba d'aya.
ta tsaya tana maida numfashi kamar wacce tayi tsere.
Miemie ta karaso da sauri murya a raunace ta na fad'in
"Yi hakuri Feeryal kin gaji da jirana ne kika shigo ko, ai dama tafiya kikayi abinki baki shiga musu side ba bare ayi miki rashin mutunci,
wlh na mance kina jirana kiyi hakuri dan Allah."
Feeryal ta maida hawayen da suka ciko mata ido sannan ta ce
"Ya Ajmal ne ya ce naje na kira Ameerah wai wannan na kiran ta, shine fa na je."
"Waye wannan kuma Feeryal?."
"Um wai waye sunan shi ma wannan babban yayannan naku mana wai waye ma sunan shi, am Sahab."
"Sahab kuma bamu da wani yaya mai suna Sahab, Ya Abdurrahim ke nan ."
"Eh shi, mamansa ta ce kar na sake ce masa yaya shi ba yayana bane,
dama nima ban san shi ba."
da sauri Miemie ta ruko hannun ta ta ce
"Kibar maganar taho muje kiyi hakuri kinji."
ta janyo ta suka yi gaba.
Shirye shiryen bikin Abdurrahim da Kuraiba yana dad'a kankama, musamman a gurin iyayen su mata Mommy da kuma Hajiya Luba, a d'ya gefen har da Alhaji Jibiril wato mahaifin Kuraiba,
dan yana matukar farin cikin had'a zuri'a da baban family sanannen family irin family'n A.A FIYA.
Daddy ya ba Mommy isasshan kud'en da zai isa yin lefe,
a b'angaren sa baya nuna farin ciki ko akasin sa game da auren.
da farko shima yaso d'an nasa yaje gida can Yelwan Shendam ya nimi mata, amma da Mommy ta buga kasa ta kekashe ita tayi masa mata sai ya kyale ta, tun da ita uwa ce ita ma tana da hakki a kan sa,
sannan kuma ya d'an yaba da gidan da matar ta fito.
Dubai Mommy ta tafi suka had'e da Hajiyan Dubai bayan sun had'a akwatuna set biyu suka wuce Egypt suka had'a set uku kafin ta biyo girgi da kayan ta dawo.
sashin Hajiya aka jibge kayan, 'yan'uwa da abokan arziki ana ta zuwa gani, anata yaba kyau da tarin yawa da tsada irin na kayan.
Feeryal da ta fito daga bathroom d'aure da towel, ta isa gaban wardrobe da sauri ta bud'e gefen da su pant da pat d'in ta suke.
ido ta d'an waro tuno da pat d'in ta ya kare ga period d'in ta ya zo.
dafe goshi tayi tana fad'in
"Wayyo na mance ashe ya kare."
sai kuma ta rufe wardrobe d'in tayi waje tana fad'in
"Ammie Ammie."
a sakiyar parlour suka had'e da Aunty da kiran nata yasata fitowa daga kitchen.
"Ya akayi ne Feeryal mene ne da irin wannan kiran?."
baki ta turo tare da langwab'ar da kai cikin muryar shagwab'a ta ce
"Ammie pat d'ina ya kare."
ido Aunty ta waro gaba d'aya ta mance da tame d'in period d'in ta ya yi, dan ko wani tame tana zuwa duba pant da pat nata,
tagama mancewa da wancan watan pat d'in zai kare bazai kai wannan watan ba.
ta ce
"Subhanallah na gama mantawa ne amma bari Baba Rabi yanzu ta fita taje ta siyo miki, jira yanzu za'a kawo miki."
Aunty ta juya da sauri ta koma kitchen in da suke aiki da Baba Rabi.
ita kuma ta juya ta koma d'aki.
Ta kasa zama sai sintirin shiga bayi take tana wanke shi da ruwa,
sam bata son jini ya b'ata mata jiki ko kad'an,
a rana takanyi amfani da pat kusan goma dan duk san da zataje fisari to fa sai ta canza pat.
gaba d'aya ta damu tana jin ta kamar a kan kaya take,
da sauri ta d'au hijabi ta zura kan towel d'in jikin ta,
ta fita da sauri ta nufi sashin su Miemie.
A parlour ta tadda Ammah ita da Faisal.
ta gaishesu tare da tambayar Ammah Miemie,
Ammah ta ce
"Tana sashin Hajiya."
"Wayyo Allah."
ta fad'a a kasan ranta a fili kuwa cewa ta yi
"Ammah bari na d'auki abu a d'akin Miemie."
Ammah ta yi murmushi tana cewa
"Ke da d'akin ku har sai kin fad'a zaki shige shi."
itama murmushi tayi.
Faisal kuwa cewa ya yi
"Kar dai Miemie ta koya miki halin gulmar nan nata."
nan ma murmushi tayi ta wuce d'akin.
wardrobe d'in ta ta bud'e ta bincika ko zataga pat tagama dube-duben ta bata gani ba,
abin haushin ma ga wayar ta a kan gado bata tafi da shi ba bare ta karb'i wayar Ammah ta kirata da shi tun da itama bata fito da wayar ta ba.
kamar zatayi kuka ta fito.
Amma ta ce
"Kin sami abin ko ta canza masa gurin ajiya, kin san halin ta da iya b'oye abu kamar me."
d'an jim tayi tana jin nauyin ta ce ga abin da take nima ga Faisal a gurin, sai kuma ta girgiza kai ta ce
"Zanje na dawo kafin ta dawo."
Ammah ta ce
"Ko zakije ki kirata acan tazo ta baki, Miemie idan ta sami hira ba dawowan yanzu ba, bare anje ganin kayan lefe."
Feeryal tayi shiru bata isa taje sashin Hajiya ba kam.
maganar Amma ta kuma ji
"Kije ki kirata Miemie fa bazata dawo yanzu ba."
a hankali ta juya ta fita, kamar kwai ya fashe mata a ciki a haka ta isa kofar Hajiya.
ganin tsayuwa bazai ficceta ba tayi jahadi tasa kai ciki.
Mutane da yawa cikin parlour'n da wanda ta tab'a gani da wanda bata tab'a ganin su ba.
an baje kaya cikin parlour' kamar masu shirin bud'e ShopRite.
gaba d'aya mutane tun shagala da kallon kayan sai santi suke.
har ta karaso ciki babu wanda ya lura da ita, tana ta baza ido dan ta ga ta ina Hajiya take, amma bata ga ko walkiyan ta a parlour'n ba.
da sauri ta isa in da Miemie take tsaye tana ta d'aga kaya tana aikin zuba surutu.
ta tab'a ta ta baya,
bige hannunta tayi tana cewa
"Dalla barni kai gawani arnen sarka wayyo Allah na."
Feeryal ta kuma tab'ata, sai sannan ta juyo baki ta washe ta ce
"La Feeryal ke ce dama na d'auka Nabila ce take tab'ani ta nuna min wani abin,
ke zokiga kaya dan Allah wai duk wa mutum d'aya za'a kai."
hannu Feeryal ta yarfe ta ce
"Dan Allah Miemie ba wannan ba taho muje ki bani pat nawa ya kare Baba Rabi taje siyo min bata dawo ba."
"To naji zauna bari na gama ganin wannan akwatin."
ta turata kan kujerar bayan ta, ta zauna tab'as a kan kujerar.
tana kokarin ta shi ta kuma mai data
"Dan Allah ki tsaya na gama gani muje na baki."
Miemie ta zauna kan hanun kujerar tayi banga banga da kafafunta ga mutane ata gefen ta babu ta yadda zatayi ta mike.
"Miemie muje ki bani dan Allah sai ki dawo."
bata ko jinta hankalin ta nakan magana da kallon kaya.
Ya kosa da jin maganar Hajiya da Mommy ta kawo karar sa gurin ta,
kan yaki zuwa su tattauna yadda shagalin bikin nasu zai kasance da amaryar tasa.
ya mike daga kan kujerar da yake zaune cikin d'akin Hajiya da ta gama zuban ta baya ma jinta idanun sa yana kan waya, ya mike yana d'an jan gajeren tsaki ya zura takalmansa.
ganin tafiya zaiyi Hajiya ta ce
"Kai abokin turawa maza kaje gidan su yarinyar nan kar ka sake baka je ba na gaya maka ke nan,
in banda abin ka ana son yi maka gata ma dube ka fa gabjeje da kai ace baka da iyali,
sa'anninka duk sunyi aure da 'ya'ya uku hud'u,
dubi d'an nan Isa d'an gidan bappanku Jibo matansa biyu da 'ya'ya shida, gasu nan dugui-dugui tafe da kafafunsu,
tafiya na Yelwan nan na ganshi cikin 'ya'yan sa gwanin sha'awa, kuma sa'anka ne,
sai yaushe ne zakayi auren kai idan aka barka haka zakayi ta zama babu aure, ina kuwa uwarka zata so,
itama zataso ganin 'yan jikokin ta kamar yadda nake ganin ku nake jin dad'i."
Kofa ya nufa yana fad'in
"Ko naje ko banje ba aure ai bazai fasu ba, to kuyi mana kawai, me zai sa sai naje."
yayi waje yana d'aga kiran da ya shigo wayarsa."
Hajiya ta d'aga murya tana cewa
"Ai aure kamma kamar anyi an gama baza'a cigaba da zuba maka ido ka cigaba da zama tuzuru ba."
Da sauri ta waiga jin ana jan abu akan kujerar da take kai.
caraf idanunta ya sauka cikin nashi.
wani irin mugun fad'uwar gaba ne ya ziyarce ta zuciyarta ya yi wani irin tsalle kamar zai faso kirkinta ya fito.
da d'a gimtse fuska ya yi yana gyara rukon wayar da ke kunnensa,
ya yin da hannunsa guda ke rike da rigarsa da ke kan kujerar da Miemie ta turata kai.........!
9
Da karfi ta janye idanunta daga cikin nashi wanda kad'an yarage ta kwalla ihu tsabar tsoro ga wani irin mashahuriyar kwarjinin dake cike cikin idanun nasa.
da sauri ta kalli inda hannunsa yake yana kokarin jan rigarsa a kan kujerar da take zaune a kai.
da sauri ta wani irin zabura ta mike tsaye jiki na kyarma.
ya d'ago rigar yana mai ware idanunsa a kansa, ya yin da fuskarsa ya dad'a sauyawa izuwa na b'acinrai karara.
ido Feeryal ta ware kan rigar da sauri ta dafe kirjinta dake ta tsalle yana niman hanyar fita, numfashin ta na sarkewa tagama sadakarwa fita zaiyi ya bar gangar jikin ta.
bata ankara ba taji ya jefo mata rigar kan fuskarta tare da jan dogon tsaki
"Mssttt stupid wawuyar kazama."
kana ya juya ya fice a parlour'n.
hanu na rawa ta ciro farin rigar daga kan fuskarta,
wanda jini ya yi makeken shati a jiki.
tana rarraba ido cikin parlour'n sai dai babu wanda ya lura da abin da ya faru kowa hankalin sa na kan kallon kayan da suke kallo.
ta tsaya tana maida numfashi kamar wacce tayi tsere.
Miemie ta karaso da sauri murya a raunace ta na fad'in
"Yi hakuri Feeryal kin gaji da jirana ne kika shigo ko, ai dama tafiya kikayi abinki baki shiga musu side ba bare ayi miki rashin mutunci,
wlh na mance kina jirana kiyi hakuri dan Allah."
Feeryal ta maida hawayen da suka ciko mata ido sannan ta ce
"Ya Ajmal ne ya ce naje na kira Ameerah wai wannan na kiran ta, shine fa na je."
"Waye wannan kuma Feeryal?."
"Um wai waye sunan shi ma wannan babban yayannan naku mana wai waye ma sunan shi, am Sahab."
"Sahab kuma bamu da wani yaya mai suna Sahab, Ya Abdurrahim ke nan ."
"Eh shi, mamansa ta ce kar na sake ce masa yaya shi ba yayana bane,
dama nima ban san shi ba."
da sauri Miemie ta ruko hannun ta ta ce
"Kibar maganar taho muje kiyi hakuri kinji."
ta janyo ta suka yi gaba.
Shirye shiryen bikin Abdurrahim da Kuraiba yana dad'a kankama, musamman a gurin iyayen su mata Mommy da kuma Hajiya Luba, a d'ya gefen har da Alhaji Jibiril wato mahaifin Kuraiba,
dan yana matukar farin cikin had'a zuri'a da baban family sanannen family irin family'n A.A FIYA.
Daddy ya ba Mommy isasshan kud'en da zai isa yin lefe,
a b'angaren sa baya nuna farin ciki ko akasin sa game da auren.
da farko shima yaso d'an nasa yaje gida can Yelwan Shendam ya nimi mata, amma da Mommy ta buga kasa ta kekashe ita tayi masa mata sai ya kyale ta, tun da ita uwa ce ita ma tana da hakki a kan sa,
sannan kuma ya d'an yaba da gidan da matar ta fito.
Dubai Mommy ta tafi suka had'e da Hajiyan Dubai bayan sun had'a akwatuna set biyu suka wuce Egypt suka had'a set uku kafin ta biyo girgi da kayan ta dawo.
sashin Hajiya aka jibge kayan, 'yan'uwa da abokan arziki ana ta zuwa gani, anata yaba kyau da tarin yawa da tsada irin na kayan.
Feeryal da ta fito daga bathroom d'aure da towel, ta isa gaban wardrobe da sauri ta bud'e gefen da su pant da pat d'in ta suke.
ido ta d'an waro tuno da pat d'in ta ya kare ga period d'in ta ya zo.
dafe goshi tayi tana fad'in
"Wayyo na mance ashe ya kare."
sai kuma ta rufe wardrobe d'in tayi waje tana fad'in
"Ammie Ammie."
a sakiyar parlour suka had'e da Aunty da kiran nata yasata fitowa daga kitchen.
"Ya akayi ne Feeryal mene ne da irin wannan kiran?."
baki ta turo tare da langwab'ar da kai cikin muryar shagwab'a ta ce
"Ammie pat d'ina ya kare."
ido Aunty ta waro gaba d'aya ta mance da tame d'in period d'in ta ya yi, dan ko wani tame tana zuwa duba pant da pat nata,
tagama mancewa da wancan watan pat d'in zai kare bazai kai wannan watan ba.
ta ce
"Subhanallah na gama mantawa ne amma bari Baba Rabi yanzu ta fita taje ta siyo miki, jira yanzu za'a kawo miki."
Aunty ta juya da sauri ta koma kitchen in da suke aiki da Baba Rabi.
ita kuma ta juya ta koma d'aki.
Ta kasa zama sai sintirin shiga bayi take tana wanke shi da ruwa,
sam bata son jini ya b'ata mata jiki ko kad'an,
a rana takanyi amfani da pat kusan goma dan duk san da zataje fisari to fa sai ta canza pat.
gaba d'aya ta damu tana jin ta kamar a kan kaya take,
da sauri ta d'au hijabi ta zura kan towel d'in jikin ta,
ta fita da sauri ta nufi sashin su Miemie.
A parlour ta tadda Ammah ita da Faisal.
ta gaishesu tare da tambayar Ammah Miemie,
Ammah ta ce
"Tana sashin Hajiya."
"Wayyo Allah."
ta fad'a a kasan ranta a fili kuwa cewa ta yi
"Ammah bari na d'auki abu a d'akin Miemie."
Ammah ta yi murmushi tana cewa
"Ke da d'akin ku har sai kin fad'a zaki shige shi."
itama murmushi tayi.
Faisal kuwa cewa ya yi
"Kar dai Miemie ta koya miki halin gulmar nan nata."
nan ma murmushi tayi ta wuce d'akin.
wardrobe d'in ta ta bud'e ta bincika ko zataga pat tagama dube-duben ta bata gani ba,
abin haushin ma ga wayar ta a kan gado bata tafi da shi ba bare ta karb'i wayar Ammah ta kirata da shi tun da itama bata fito da wayar ta ba.
kamar zatayi kuka ta fito.
Amma ta ce
"Kin sami abin ko ta canza masa gurin ajiya, kin san halin ta da iya b'oye abu kamar me."
d'an jim tayi tana jin nauyin ta ce ga abin da take nima ga Faisal a gurin, sai kuma ta girgiza kai ta ce
"Zanje na dawo kafin ta dawo."
Ammah ta ce
"Ko zakije ki kirata acan tazo ta baki, Miemie idan ta sami hira ba dawowan yanzu ba, bare anje ganin kayan lefe."
Feeryal tayi shiru bata isa taje sashin Hajiya ba kam.
maganar Amma ta kuma ji
"Kije ki kirata Miemie fa bazata dawo yanzu ba."
a hankali ta juya ta fita, kamar kwai ya fashe mata a ciki a haka ta isa kofar Hajiya.
ganin tsayuwa bazai ficceta ba tayi jahadi tasa kai ciki.
Mutane da yawa cikin parlour'n da wanda ta tab'a gani da wanda bata tab'a ganin su ba.
an baje kaya cikin parlour' kamar masu shirin bud'e ShopRite.
gaba d'aya mutane tun shagala da kallon kayan sai santi suke.
har ta karaso ciki babu wanda ya lura da ita, tana ta baza ido dan ta ga ta ina Hajiya take, amma bata ga ko walkiyan ta a parlour'n ba.
da sauri ta isa in da Miemie take tsaye tana ta d'aga kaya tana aikin zuba surutu.
ta tab'a ta ta baya,
bige hannunta tayi tana cewa
"Dalla barni kai gawani arnen sarka wayyo Allah na."
Feeryal ta kuma tab'ata, sai sannan ta juyo baki ta washe ta ce
"La Feeryal ke ce dama na d'auka Nabila ce take tab'ani ta nuna min wani abin,
ke zokiga kaya dan Allah wai duk wa mutum d'aya za'a kai."
hannu Feeryal ta yarfe ta ce
"Dan Allah Miemie ba wannan ba taho muje ki bani pat nawa ya kare Baba Rabi taje siyo min bata dawo ba."
"To naji zauna bari na gama ganin wannan akwatin."
ta turata kan kujerar bayan ta, ta zauna tab'as a kan kujerar.
tana kokarin ta shi ta kuma mai data
"Dan Allah ki tsaya na gama gani muje na baki."
Miemie ta zauna kan hanun kujerar tayi banga banga da kafafunta ga mutane ata gefen ta babu ta yadda zatayi ta mike.
"Miemie muje ki bani dan Allah sai ki dawo."
bata ko jinta hankalin ta nakan magana da kallon kaya.
Ya kosa da jin maganar Hajiya da Mommy ta kawo karar sa gurin ta,
kan yaki zuwa su tattauna yadda shagalin bikin nasu zai kasance da amaryar tasa.
ya mike daga kan kujerar da yake zaune cikin d'akin Hajiya da ta gama zuban ta baya ma jinta idanun sa yana kan waya, ya mike yana d'an jan gajeren tsaki ya zura takalmansa.
ganin tafiya zaiyi Hajiya ta ce
"Kai abokin turawa maza kaje gidan su yarinyar nan kar ka sake baka je ba na gaya maka ke nan,
in banda abin ka ana son yi maka gata ma dube ka fa gabjeje da kai ace baka da iyali,
sa'anninka duk sunyi aure da 'ya'ya uku hud'u,
dubi d'an nan Isa d'an gidan bappanku Jibo matansa biyu da 'ya'ya shida, gasu nan dugui-dugui tafe da kafafunsu,
tafiya na Yelwan nan na ganshi cikin 'ya'yan sa gwanin sha'awa, kuma sa'anka ne,
sai yaushe ne zakayi auren kai idan aka barka haka zakayi ta zama babu aure, ina kuwa uwarka zata so,
itama zataso ganin 'yan jikokin ta kamar yadda nake ganin ku nake jin dad'i."
Kofa ya nufa yana fad'in
"Ko naje ko banje ba aure ai bazai fasu ba, to kuyi mana kawai, me zai sa sai naje."
yayi waje yana d'aga kiran da ya shigo wayarsa."
Hajiya ta d'aga murya tana cewa
"Ai aure kamma kamar anyi an gama baza'a cigaba da zuba maka ido ka cigaba da zama tuzuru ba."
Da sauri ta waiga jin ana jan abu akan kujerar da take kai.
caraf idanunta ya sauka cikin nashi.
wani irin mugun fad'uwar gaba ne ya ziyarce ta zuciyarta ya yi wani irin tsalle kamar zai faso kirkinta ya fito.
da d'a gimtse fuska ya yi yana gyara rukon wayar da ke kunnensa,
ya yin da hannunsa guda ke rike da rigarsa da ke kan kujerar da Miemie ta turata kai.........!
9
Da karfi ta janye idanunta daga cikin nashi wanda kad'an yarage ta kwalla ihu tsabar tsoro ga wani irin mashahuriyar kwarjinin dake cike cikin idanun nasa.
da sauri ta kalli inda hannunsa yake yana kokarin jan rigarsa a kan kujerar da take zaune a kai.
da sauri ta wani irin zabura ta mike tsaye jiki na kyarma.
ya d'ago rigar yana mai ware idanunsa a kansa, ya yin da fuskarsa ya dad'a sauyawa izuwa na b'acinrai karara.
ido Feeryal ta ware kan rigar da sauri ta dafe kirjinta dake ta tsalle yana niman hanyar fita, numfashin ta na sarkewa tagama sadakarwa fita zaiyi ya bar gangar jikin ta.
bata ankara ba taji ya jefo mata rigar kan fuskarta tare da jan dogon tsaki
"Mssttt stupid wawuyar kazama."
kana ya juya ya fice a parlour'n.
hanu na rawa ta ciro farin rigar daga kan fuskarta,
wanda jini ya yi makeken shati a jiki.
tana rarraba ido cikin parlour'n sai dai babu wanda ya lura da abin da ya faru kowa hankalin sa na kan kallon kayan da suke kallo.