Sashe 40
Feeryal Part 2 Complete Hausa Novel.t · about 8 min read
Umma Karima ta d'auko tsinken gwajin ciki ta mika mata d'an karamin kwantena ta sata gaba suka shiga bayi tana tsaye a kanta tayi fitsari ta bata.
ta saka PT ciki taja ta tsaya tana fifita da d'an kwalinta.
bai mata ba ta fito parlour rike da PT, gani tayi d'akin ya kasa mata.
'ya'yan nata suka biyo ta.
wani uban ashar Umma Karima ta mulmulo ganin amsar tana da ciki sinken gwajin ya bayar.
ta sake shi a kasa ta sa hannu akai tana fad'in
"Nashiga uku ni Karima Saddiqa kema cikin kikayi!
a ina kika samo ciki wani d'an kutumar uban ne ya miki ciki!."
Kulu ta waro ido ta juya sad'af-sad'af ta yi waje tana kama baki.
Saddiqa tayi kasa da kai jiki na rawa.
Umma Karima ta buga mata tsawa
"Dan uban ki ina tambayarki uban wa yamiki ciki zaki gaya min ne ko sai naci kutumar uban ki."
Saddiqa ta zabura murya na rawa ta ce
"Um..mu...."
sai kuma tayi shiru.
Umma Karima tayi kukan kura tayi kanta da sauri ta b'oye bayan Bilkisu tana fad'in
"Zan gaya miki Umma."
"Zo nan gaba na ki gaya min."
ta fad'a tana huci.
ta zo jiki na rawa tashiga kame-kame ta na fad'in
"Um..um..saurayin Aunty Siyama ne."
Siyama da Umma Karima suka waro ido a tare.
Umma Karima ta ce
"Au tsinanne tambad'ad'd'e, d'an akuya sabo da shi ya zamo bunsuru yabita ya barbare ta yakuma biyoki ke ma,
sabo da wancan karon ban d'auki mataki a kan saba, shine bari ya kuma b'ulluwa ta hanyar baya ya d'ura miki ciki ke ma,
ke Siyama d'an gidan uban waye ne shi da yake binku yana barbarar ku,
sai na ga uban sa Wallahi."
su Nabila suka waro ido dan dama basusan da na Siyama ba.
Kulu da saurinta ta shige sashin Hajiya.
Hajiya na ganin ta babu aikan da ta mata ta ce
"Ke Kulu ina hayakin dana aike ki karb'a?."
Kulu ta ware ido ta rike hab'a ta ce
"Hajiya wlh akwai babban matsala a gidan nan, wannan yarinya Saddiqa 'yar wajen Hajiya Karima ciki take da shi, ciki tayiyo wlh Hajiya yanzun nan aka gano tana da ciki."
Hajiya ta saka salati tana fad'in
"Wasayyawu ni jikar mutane hud'u Saddiqa'n ce tayiyo ciki, ciki dai acikin gidan nan,
maza kirawa min Abubakar da abokin turawa."
Kulu ta d'au wayar Hajiya ta kira lambar Daddy yana d'agawa ta mika mata.
ta karb'a ta kai kunne tana ta ce
"Abubakar kasan musifar dake faruwa agidan nan kuwa, maza kazo yanzu ina niman ka."
ta kashe ta ce wa Kulu kira min abokin turawa.
wayarsa tayi ta ringing bai d'aga ba.
Kulu ta ce "Bai d'aga ba Hajiya."
ba'a jima ba Daddy ya shigo da fargabar abin da Hajiya zata ce masa dan yasan maganar Hajiya bazai wuce akan Feeryal ba.
tun kafin ya zauna ta ce
"Abubakar Saddiqa da cikin shege a cikin gidan nan, wace irin musifa ce wannan, acikin gidan ka cikin shege ya b'ullo."
da sauri Daddy da maganar ta duki kirjinsa ya kai hannu ya dafe kirji.
ya zauna kan kujera da kyar hannunsa dafe da kirjin sa.
"Innalillahi wa innailaihirraji'un!."
kalmar data fito daga bakin Daddy ke nan.
Abdurrahim da shigowarsa ke nan yaga kiran Hajiya yana masallaci.
ya karaso da sauri ganin yanda Daddy ke dafe da kirjinsa zaton sa ciwon sa ne ya tashi yasa Hajiya ta kira sa.
ya sunkuya gaban Daddy tare da cire hannunsa dake kirjinsa ya d'aura nasa yana fad'in
"Daddy ya kake jin kirjin ya ke maka."
ido ya rumtse ya ce
"Zafi sosai yake min Abdurrahim."
Hajiya ta ce
"Yo wad'an nan 'ya'ya su zasu kasheka, bansan meye kake jira ace wad'annan gandan-gandan d'in 'yanmata suna zaune a gida babu aure, ba dole su d'auko magana ba,
gaba d'ayan su da an musu aure kan lokaci da yanzu 'ya'ya biyu ko uku suke da shi,
har autar tasu Nabila takai ta haifi d'a d'aya zuwa biyu;
to Saddiqa ta d'auko ciki sauran ma ba'a san in da hali zaiyi ba."
da karfi Abdurrahim ya d'ago ya furta
"Ciki!."
Hajiya ta ce "Kwarai kuwa cikin shege tayi, wannan irin abin kunya ace daga gidan nan ya fito."
wani irin mikewa ya yi damasunsa sukayi wani irin bud'ewa, b'acin rai karara ake iya hangowa kan fuskarsa.
da sauri ya juya yana taka kafafunsa a kasa, kasa tana amsa sautin takunsa
dip-dip-dip!.
ya b'allo reshen fulawa ya nufi sashin Umma Karima.
yadda ya fad'o cikin parlour ba 'ya'yan nata ba hatta ita kanta Umma Karima sai da ta razana..
ya yi kan su su Saddiqa da duka kan mai uwa da wabi, ba ita kad'ai ba har da su Bilkisu Rahma Nabila.
sai da itacen ta karye tayi kaca-kaca a jikinsu.
Siyama ta mike da gudu ta masa bayan Umma Karima dan bulalar sai da ya same ta,
ransa ya kai kololuwa wajen b'aci yayi jifa guntuwar itacen hannunsa,
ya cafko
Saddiqa yana kokarin kuncen belt d'in wandon sa.
Umma Karima ta yi saurin cewa
"Wlh in gaya maka Abdurrahim fyad'e aka mata, fyad'e d'an iskan yaron ya yi mata bada son ranta ba."
wani mari ya d'auketa da shi sai da ta kife kasa.
ya shiga nuna su da yatsa cikin kakkausar muya yake fad'in
"Wallahi! idan kukasa bakincikin ku ya yi sanadiyyar bugawar zuciyar Daddy, na rantse dukkanin ku sai na cire zuciyoyin ku da hannuna!."
ya yi shot da Saddiqa a yadda yake jin kansa idan yacigaba da tsayu zai iya kusan kashe ta da duka......!
Mommyn Twins ce
Abdulrahim na fita Umma Karima tayi kan 'ya'yan ta tana fad'in
"Ai kin gani Saddiqa kin janyo muku duka dukan ku, idan badun nace masa fyad'e akayi miki ba da kinci ubanki a hannunsa,
yazama dole kema aje a cire cikin nan,
dan wlh ban shiryawa abin kunya ba,
'yan iskan yara suna ni man sa ni a bakin duniya."
a b'angaren Daddy kuwa da kyar ya iya mikewa yana jin kirjin sa na yi masa zafi, ya lallab'a ya tafi sashin Aunty.
ganin yanayin sa Aunty ta tare shi a d'an tsorace tana fad'in
"Subhanallahi ya dai Daddy ba dai jikin ba dai?."
ta rike hannunsa ganin yana kokarin zama bakin gado, ya zauna yana mai dad'a kankame hannunta.
Aunty tayi kokarin zame hannunta tana fad'in
"Daddy bakasha magani ba ko bari na d'auko maka kasha."
ya dad'a rike hannunta tare da girgiza mata kai ya ce
"Barshi Fad'imatu dan ko na sha ma babu amfanin da zai min."
jikin ta ya yi sanyi sosai ta ce
"Daddy dan Allah kar ka bani tsoro, me kake ji yanzu, ya kirjin ya ke maka."
"Zafi sosai yake min Fad'imatu sai ina ji kamar zafin yafi na baya."
kallon sa ta ke cikin tsoro "Fad'imatu."
ya kira sunan ta murya a sanyaye ta gyad'a masa kai alamun tana jinsa.
hannunta ya dad'a rikewa gam kana ya soma magana
"A cikin gida na ni Abubakar Fiya, aka samu mai yin ciki a waje a cikin 'ya'yana,
Fad'imatu ina jin zafi sosai cikin zuciya ta."
wani irin waro ido Aunty tayi kirjinta ya buga da karfi ta ce
"Daddy wacce irin magana ce wannan maraddad'in ji!?."
kai ya gyad'a mata ya ce
"Tabbas Saddiqa tayi ciki a waje Fad'imatu har haka na gaza a gida na?
me mutane zasuce a kaina."
Aunty ta dad'a jin gaban ta ya tsinke jikin ta ya yi sanyi matuka,
taji rashin dad'in abun ba kad'an ba,
duk da mugun hali irin na uwar Saddiqa bazatayi fatan ace d'iyarta ta kasance cikin wannan halin ba,
jiki a sanyaye ta ce
"Daddy baka gaza ba masu taimako ne aka sami sakaki daga wajen su, uwa ita ke taimakon uba wajen yiwa 'ya'ya tarbiyya, a yayin da uba ya fita nima,
kayi hakuri Daddy jarabawa ce babu wanda yafi karfin kaddara,
mutane zasu fahimceka dan sun san cewa kai tsayayyen uba ne;
ka rungumi kaddara mai imani ne ake jarabtar shi ta ko wacce hanya,
shin Daddy ka mance imanin mutum bazai cika ba har sai ya gaskata ya kuma yarda da wad'annan abubuwa guda shida,
yadda da ALLAH d'aya ne kayi imani da shi, da mala'ikunsa da duk littattafan da ya saukar, da duk manzannin da ya aiko,
da ranar karshe wato ranar kiyama,
da KADDARA mai kyau ko mara kyau;
Daddy kaddarar mu ce bazamu tab'a ketare masa ba, kayi hakuri dan Allah Daddy ka barwa Allah ko mai kaji Daddy."
ta zauna gefen sa ta cigaba da kwantar masa da hankali,
wanda cikin kankanin lokaci yaji nutsuwa tare da shi.
A cikin gidan kuwa labari ya soma yawo kamar dai yadda idan abu ya faru ake kai kawo da shi.
sai dai wannna karo masu yawo da zance kasa-kasa sukeyi dan yau abin maganar daga tushin uwar kai kawo ya fito, wato Umma Karima.
tarika sakaye wa tana cewa ai fyad'e aka mata.
a ranar da abun ya faru da daddare Umma Karima tasa Saddiqa gaba suka ce sashin Daddy.
yana zaune a parlour yana kallon labarai a TV.
Mommy na zaune a gefe san yau ita ke da Daddy.
Umma Karima ta zauna saman kujerar da ke fuskantar sa, Saddiqa ta zauna a kasa.
Umma Karima ta marairaice murya dake nuni da zallar shiga matukar damuwa ta ce
"Alhaji yanzu fisabilillahi kaji abin da ya faru, amma baka zo kaji taya hakan ya faru ba,
shike nan za'a zuba ido a gyale yaron da ya keta mata haddi ya mata fyad'e ke nan, baza'a d'auki wani mataki ba,
ko d'an gidan uban waye baza'a tura hukuma suje su kamo sa ba,
shiru za'ayi da batun ke nan abu tun safe kayi shiru bakace ko mai ba har dare."
Daddy ya dube ta da d'iyar tata da ta sunkuyar da kai ya jinjina kai tare da fad'in
"Me kike so nace a kai bayan ke ce uwan ke ce uban, duk abin da kikaga dai-dai ne kije kiyi Hajiya Karima."
daga nan bai kuma cewa komai ba ya kwashi wayoyinsa da system d'in sa ya shige bedroom d'insa.
Mommy ta ce
"Haba Alhaji bai kamata ka ce haka ba, kamata ya yi ad'au mataki a kan yaron."
ta saka PT ciki taja ta tsaya tana fifita da d'an kwalinta.
bai mata ba ta fito parlour rike da PT, gani tayi d'akin ya kasa mata.
'ya'yan nata suka biyo ta.
wani uban ashar Umma Karima ta mulmulo ganin amsar tana da ciki sinken gwajin ya bayar.
ta sake shi a kasa ta sa hannu akai tana fad'in
"Nashiga uku ni Karima Saddiqa kema cikin kikayi!
a ina kika samo ciki wani d'an kutumar uban ne ya miki ciki!."
Kulu ta waro ido ta juya sad'af-sad'af ta yi waje tana kama baki.
Saddiqa tayi kasa da kai jiki na rawa.
Umma Karima ta buga mata tsawa
"Dan uban ki ina tambayarki uban wa yamiki ciki zaki gaya min ne ko sai naci kutumar uban ki."
Saddiqa ta zabura murya na rawa ta ce
"Um..mu...."
sai kuma tayi shiru.
Umma Karima tayi kukan kura tayi kanta da sauri ta b'oye bayan Bilkisu tana fad'in
"Zan gaya miki Umma."
"Zo nan gaba na ki gaya min."
ta fad'a tana huci.
ta zo jiki na rawa tashiga kame-kame ta na fad'in
"Um..um..saurayin Aunty Siyama ne."
Siyama da Umma Karima suka waro ido a tare.
Umma Karima ta ce
"Au tsinanne tambad'ad'd'e, d'an akuya sabo da shi ya zamo bunsuru yabita ya barbare ta yakuma biyoki ke ma,
sabo da wancan karon ban d'auki mataki a kan saba, shine bari ya kuma b'ulluwa ta hanyar baya ya d'ura miki ciki ke ma,
ke Siyama d'an gidan uban waye ne shi da yake binku yana barbarar ku,
sai na ga uban sa Wallahi."
su Nabila suka waro ido dan dama basusan da na Siyama ba.
Kulu da saurinta ta shige sashin Hajiya.
Hajiya na ganin ta babu aikan da ta mata ta ce
"Ke Kulu ina hayakin dana aike ki karb'a?."
Kulu ta ware ido ta rike hab'a ta ce
"Hajiya wlh akwai babban matsala a gidan nan, wannan yarinya Saddiqa 'yar wajen Hajiya Karima ciki take da shi, ciki tayiyo wlh Hajiya yanzun nan aka gano tana da ciki."
Hajiya ta saka salati tana fad'in
"Wasayyawu ni jikar mutane hud'u Saddiqa'n ce tayiyo ciki, ciki dai acikin gidan nan,
maza kirawa min Abubakar da abokin turawa."
Kulu ta d'au wayar Hajiya ta kira lambar Daddy yana d'agawa ta mika mata.
ta karb'a ta kai kunne tana ta ce
"Abubakar kasan musifar dake faruwa agidan nan kuwa, maza kazo yanzu ina niman ka."
ta kashe ta ce wa Kulu kira min abokin turawa.
wayarsa tayi ta ringing bai d'aga ba.
Kulu ta ce "Bai d'aga ba Hajiya."
ba'a jima ba Daddy ya shigo da fargabar abin da Hajiya zata ce masa dan yasan maganar Hajiya bazai wuce akan Feeryal ba.
tun kafin ya zauna ta ce
"Abubakar Saddiqa da cikin shege a cikin gidan nan, wace irin musifa ce wannan, acikin gidan ka cikin shege ya b'ullo."
da sauri Daddy da maganar ta duki kirjinsa ya kai hannu ya dafe kirji.
ya zauna kan kujera da kyar hannunsa dafe da kirjin sa.
"Innalillahi wa innailaihirraji'un!."
kalmar data fito daga bakin Daddy ke nan.
Abdurrahim da shigowarsa ke nan yaga kiran Hajiya yana masallaci.
ya karaso da sauri ganin yanda Daddy ke dafe da kirjinsa zaton sa ciwon sa ne ya tashi yasa Hajiya ta kira sa.
ya sunkuya gaban Daddy tare da cire hannunsa dake kirjinsa ya d'aura nasa yana fad'in
"Daddy ya kake jin kirjin ya ke maka."
ido ya rumtse ya ce
"Zafi sosai yake min Abdurrahim."
Hajiya ta ce
"Yo wad'an nan 'ya'ya su zasu kasheka, bansan meye kake jira ace wad'annan gandan-gandan d'in 'yanmata suna zaune a gida babu aure, ba dole su d'auko magana ba,
gaba d'ayan su da an musu aure kan lokaci da yanzu 'ya'ya biyu ko uku suke da shi,
har autar tasu Nabila takai ta haifi d'a d'aya zuwa biyu;
to Saddiqa ta d'auko ciki sauran ma ba'a san in da hali zaiyi ba."
da karfi Abdurrahim ya d'ago ya furta
"Ciki!."
Hajiya ta ce "Kwarai kuwa cikin shege tayi, wannan irin abin kunya ace daga gidan nan ya fito."
wani irin mikewa ya yi damasunsa sukayi wani irin bud'ewa, b'acin rai karara ake iya hangowa kan fuskarsa.
da sauri ya juya yana taka kafafunsa a kasa, kasa tana amsa sautin takunsa
dip-dip-dip!.
ya b'allo reshen fulawa ya nufi sashin Umma Karima.
yadda ya fad'o cikin parlour ba 'ya'yan nata ba hatta ita kanta Umma Karima sai da ta razana..
ya yi kan su su Saddiqa da duka kan mai uwa da wabi, ba ita kad'ai ba har da su Bilkisu Rahma Nabila.
sai da itacen ta karye tayi kaca-kaca a jikinsu.
Siyama ta mike da gudu ta masa bayan Umma Karima dan bulalar sai da ya same ta,
ransa ya kai kololuwa wajen b'aci yayi jifa guntuwar itacen hannunsa,
ya cafko
Saddiqa yana kokarin kuncen belt d'in wandon sa.
Umma Karima ta yi saurin cewa
"Wlh in gaya maka Abdurrahim fyad'e aka mata, fyad'e d'an iskan yaron ya yi mata bada son ranta ba."
wani mari ya d'auketa da shi sai da ta kife kasa.
ya shiga nuna su da yatsa cikin kakkausar muya yake fad'in
"Wallahi! idan kukasa bakincikin ku ya yi sanadiyyar bugawar zuciyar Daddy, na rantse dukkanin ku sai na cire zuciyoyin ku da hannuna!."
ya yi shot da Saddiqa a yadda yake jin kansa idan yacigaba da tsayu zai iya kusan kashe ta da duka......!
Mommyn Twins ce
Abdulrahim na fita Umma Karima tayi kan 'ya'yan ta tana fad'in
"Ai kin gani Saddiqa kin janyo muku duka dukan ku, idan badun nace masa fyad'e akayi miki ba da kinci ubanki a hannunsa,
yazama dole kema aje a cire cikin nan,
dan wlh ban shiryawa abin kunya ba,
'yan iskan yara suna ni man sa ni a bakin duniya."
a b'angaren Daddy kuwa da kyar ya iya mikewa yana jin kirjin sa na yi masa zafi, ya lallab'a ya tafi sashin Aunty.
ganin yanayin sa Aunty ta tare shi a d'an tsorace tana fad'in
"Subhanallahi ya dai Daddy ba dai jikin ba dai?."
ta rike hannunsa ganin yana kokarin zama bakin gado, ya zauna yana mai dad'a kankame hannunta.
Aunty tayi kokarin zame hannunta tana fad'in
"Daddy bakasha magani ba ko bari na d'auko maka kasha."
ya dad'a rike hannunta tare da girgiza mata kai ya ce
"Barshi Fad'imatu dan ko na sha ma babu amfanin da zai min."
jikin ta ya yi sanyi sosai ta ce
"Daddy dan Allah kar ka bani tsoro, me kake ji yanzu, ya kirjin ya ke maka."
"Zafi sosai yake min Fad'imatu sai ina ji kamar zafin yafi na baya."
kallon sa ta ke cikin tsoro "Fad'imatu."
ya kira sunan ta murya a sanyaye ta gyad'a masa kai alamun tana jinsa.
hannunta ya dad'a rikewa gam kana ya soma magana
"A cikin gida na ni Abubakar Fiya, aka samu mai yin ciki a waje a cikin 'ya'yana,
Fad'imatu ina jin zafi sosai cikin zuciya ta."
wani irin waro ido Aunty tayi kirjinta ya buga da karfi ta ce
"Daddy wacce irin magana ce wannan maraddad'in ji!?."
kai ya gyad'a mata ya ce
"Tabbas Saddiqa tayi ciki a waje Fad'imatu har haka na gaza a gida na?
me mutane zasuce a kaina."
Aunty ta dad'a jin gaban ta ya tsinke jikin ta ya yi sanyi matuka,
taji rashin dad'in abun ba kad'an ba,
duk da mugun hali irin na uwar Saddiqa bazatayi fatan ace d'iyarta ta kasance cikin wannan halin ba,
jiki a sanyaye ta ce
"Daddy baka gaza ba masu taimako ne aka sami sakaki daga wajen su, uwa ita ke taimakon uba wajen yiwa 'ya'ya tarbiyya, a yayin da uba ya fita nima,
kayi hakuri Daddy jarabawa ce babu wanda yafi karfin kaddara,
mutane zasu fahimceka dan sun san cewa kai tsayayyen uba ne;
ka rungumi kaddara mai imani ne ake jarabtar shi ta ko wacce hanya,
shin Daddy ka mance imanin mutum bazai cika ba har sai ya gaskata ya kuma yarda da wad'annan abubuwa guda shida,
yadda da ALLAH d'aya ne kayi imani da shi, da mala'ikunsa da duk littattafan da ya saukar, da duk manzannin da ya aiko,
da ranar karshe wato ranar kiyama,
da KADDARA mai kyau ko mara kyau;
Daddy kaddarar mu ce bazamu tab'a ketare masa ba, kayi hakuri dan Allah Daddy ka barwa Allah ko mai kaji Daddy."
ta zauna gefen sa ta cigaba da kwantar masa da hankali,
wanda cikin kankanin lokaci yaji nutsuwa tare da shi.
A cikin gidan kuwa labari ya soma yawo kamar dai yadda idan abu ya faru ake kai kawo da shi.
sai dai wannna karo masu yawo da zance kasa-kasa sukeyi dan yau abin maganar daga tushin uwar kai kawo ya fito, wato Umma Karima.
tarika sakaye wa tana cewa ai fyad'e aka mata.
a ranar da abun ya faru da daddare Umma Karima tasa Saddiqa gaba suka ce sashin Daddy.
yana zaune a parlour yana kallon labarai a TV.
Mommy na zaune a gefe san yau ita ke da Daddy.
Umma Karima ta zauna saman kujerar da ke fuskantar sa, Saddiqa ta zauna a kasa.
Umma Karima ta marairaice murya dake nuni da zallar shiga matukar damuwa ta ce
"Alhaji yanzu fisabilillahi kaji abin da ya faru, amma baka zo kaji taya hakan ya faru ba,
shike nan za'a zuba ido a gyale yaron da ya keta mata haddi ya mata fyad'e ke nan, baza'a d'auki wani mataki ba,
ko d'an gidan uban waye baza'a tura hukuma suje su kamo sa ba,
shiru za'ayi da batun ke nan abu tun safe kayi shiru bakace ko mai ba har dare."
Daddy ya dube ta da d'iyar tata da ta sunkuyar da kai ya jinjina kai tare da fad'in
"Me kike so nace a kai bayan ke ce uwan ke ce uban, duk abin da kikaga dai-dai ne kije kiyi Hajiya Karima."
daga nan bai kuma cewa komai ba ya kwashi wayoyinsa da system d'in sa ya shige bedroom d'insa.
Mommy ta ce
"Haba Alhaji bai kamata ka ce haka ba, kamata ya yi ad'au mataki a kan yaron."