Sashe 11
Feeryal Part 2 Complete Hausa Novel.t · about 7 min read
Kamar yadda Aunty ta ce da rana tare suka shiga kitchen da Feeryal.
Sosai Aunty ta dage wajen koyawa Feeryal nau'ikan girki kala-kala, bata yadda ta barta kara zube kamar yadda wasu masu kud'in suke yi wa 'ya'yan su ba,
komai sai dai masu aiki suyi ba dai 'ya'yan su ba, suna ganin wai hakan gata ne da yawa sai sunyi aure suke had'uwa da kalu bale daban-daban a gidan auren.
duk da Aunty d'iyar masu kud'i ce bata taso cikin tarbiyyar irin wad'an can 'ya'yan masu kud'in ba.
shiyasa ta zage damtse wajen koyawa Feeryal abubuwa da dama da suka shafi cikin gida.
yawan zama da Miemie takeyi a sashin itama ta karu da wasu abubuwa da dama.
Aunty ce zaune a parlour tana video call da Hajja Umma.
jiya aka sami nasarar zakulo mutum biyu daga cikin tawagar 'yan d'aukar amarya, da hukuma suke ta kan bincike a kansu har yanzu.
Aunty tace
"Amma dai Hajja Umma babu wata matsala ko?
ni fa tun da naji ance an kuma kama wasu 'yan gidan sa duk a tsoro nake,
kar sauran da suke a b'oye suce zasu fito d'aukar fansa."
Hajja Umma ta ce
"A'a babu komai insha'allah, wannan yaro Sadam Abokin Nasir Allah dai ya saka miki, yaron akwai kokari jiyan nan kusan da shi muka wuni a gidan nan da jami'an su, da daddare ya turo jami'an su biyu da folisawa biyu da Nasir ya turo
har muka waye gari yau da su,
har yanzu ma suna nan,
amma naji Alhaji yana cewa anan zasu cigaba da zama har zuwa a kare bincike."
Aunty ta sauke numfashi tare da cewa
"To Allah ya dad'a tsarewa."
"Amin ya Allah, wai ni kam ina kishiya take ne banji d'uriyar ta ba."
"Tana d'aki ai bata san muna waya da ke ba da kin ganta."
Aunty ta d'aga murya ta wala mata kira,
ta fito da sauri tana amsa kiran
"Taho ga Hajja Umma tana niman ki."
da sassarfa ta karaso inda Aunty take ta zauna gefen ta tare da kwantar da kanta a jikin ta, ido ta waro ta ce
"La Hajja Umma shine tun d'azu baki neme ni ba ko."
"A'a nunar gwanda bagashi na nemo ki ba yanzu,
kwana biyu da ban gankiba sai naga kin dad'a kumbura, kazar turai jikin nan ya dad'a komawa tumatur sharaf."
baki Feeryal ta turo ta ce
"Ba Abba ya ce ya ce ki dai na fad'a min ba, ke da shi,
Ammie na kashe ki kira min mijin ta muyi hira."
"A waya kawai zaki ganshi ni kuma ina tare da shi a nan."
"Ai baki sani ba Hajja Umma kullum sai yabi jirgi yazo gurina,
ke kina can kina ta kan cewa masu aiki,
kuyi kaza kuyi kaza, kar ku saka gishiri da yawa a abincin almajiran nan fa ku sa musu magi ya ji."
dariya duk suka fashe da shi.
Aunty ta ce
"Au haka Hajja Umman take fad'a."
kai ta gyad'a tana dariya ta ce
"Kullum sai Abba ya shigo yace ta zauna ta huta ta barsu su suyi aikin, yana fita zata tashi taje bata zama tarika kai kawo ke nan, bata ko gajiya,
ai shiyasa Abba ya ce yafi so na ma, ita kullum bata hutu gata da masu aiki."
dariya Aunty tayi tana dungurin kanta.
Maryam da ta shigo ta tadda suna wayan ta leko cikin wayar Feeryal ta washe baki
"Aunty Maryam ina kika je ne?."
"Gidan su Haulat yanzu kuwa muke hiran ki da ita, tana tambaya ta yaushe zaki dawo."
"Ai nakusa dawowa, sai dai bana so na rabu da Ammie na ne."
tayi maganar tana dad'a kwanciya jikin Aunty.
"To ai sai ku dawo tare da Ammie'n naki."
cewar Maryam tana mata hararar wasa.
Wayar ta da ke rike a hannunta ne ya yi kara,
ganin Miemie ce ke kiran nata yasata d'agawa.
"Hello Miemie."
daga cikin wayar Miemie ta ce
"Feeryal yi sauri kizo kiji wani magana."
"Wacce magar Miemie?."
jin shiru yasata ciro wayar a kunne taga har ma ta kashe kiran.
ganin Aunty sun kama wani hirar da Hajja Umma sai ta fice zuwa sashin su Miemie.
Har ta kusa rabin isa sashin nasu kiran Miemie ya kuma shigowa wayar ta.
"Yauwa Feeryal tsaya ma kawai bazan zo."
"Ai gashi na fito ma bari na karaso."
"To tsaya-tsaya ma kawai bari ni na fito."
Miemie ta fad'a tare da katse kiran.
Feeryal ta sauke numfashi tana fad'in
"Oh Miemie."
Gefe ta matsa ta jikin wasu dogayen bishiyoyin fula da suke jere a gurin, tana jiran fitowar ta.
maganar da taji ta cikin bishoyoyin ne yasata juyawa da sauri ta d'an leko ta sakankanin flaws d'in.
karaf suka had'a ido da Ameerah da ke zaune da saurayin ta suna hira kan kujerun da suke cikin gurin.
saurayin ya mike da alama sun gama hirar zai tafi.
da sauri ta d'an matsa baya.
Tana tsaye har motar saurayin ya fita a gidan.
a razane ta waigo jin an buga kafad'ar ta ta baya.
Ameerah ta bita da kallon sama da kasa ta ce
"To sannu bakar munafuka, wacce munafurcin ne yakawo ki nan kika zo kina leka min saurayi,
Allah ya toni asirin ki saurayi na kike lekawa."
murya a sanyaye Feeryal ta ce
"Kiyi hakuri wlh bansan kuna nan ba, kuma ni ba lekensa nake yi ba."
"Karya kike yi leka shi kike yi ai ina kallon ki,
sai kin fad'a min uban da yasa kike lekashi, ko naci uban ki da duka anan, dama ina da cikin ki."
"Allah Ameerah ni ba leken sa nake ba, ban ma san kune a gurin ba."
Miemie da ke tahoto ta bud'e baki tana kallon yadda Ameerah ke d'agawa Feeryal murya ita ko sai magiya da kwantar da kai take kamar zatayi kuka.
da sauri ta karaso gurin ta na fad'in
"Ya ya akayi wai mene ne?."
da sauri cikin tsiwa Ameerah ta ce
"Kamata nayi tana leka min saurayi."
Feeryal tayi narai-narai da ido ta ce
"Allah ba leken sa nake ba magana naji na leka bansa su bane."
Miemie ta ce
"To lallai saboda Feeryal d'in ta rasa aikin yi sai ta tsaya leken saurayi kamar wacce ta rasa samari,
ta ce ba leka miki saurayi tayi ba ai sai kiyi hakuri ki rabu da ita."
"Karya take lekashi take yi ai na ganta da ido na."
Ameerah tayi maganar cikin hayagaga.
Miemie ta ce
"To meye a jikin saurayin naki da za'a leka shi,
ana ta ce miki kiyi hakuri kina ta wani d'agawa mutane murya to ta kalla kiyi abin da zakiyi,
dalla wuce mu tafi, Feeryal tayi abin da zatayi."
"To idan zan mata abun da zan matan zaki hana ne,
kema bakifi karfin na had'a da ke ba bana son shishigi."
Miemie ta dalla mata harara ta ce
"Kar ki yadda kice zakiyi min ehe ni ba Feeryal bace kul in gaya miki,
kisan wad'an da kike wa rainin wayon ki, kar ki yadda kice zakiyi min,
dalla wuce mu tafi kin tsa tana gaya miki magana har kina bata hakuri."
taja nannu Feeryal fuuu suka kara gaba bata fasa mitar ba.
"Ki ci gaba da tsayu kowa yarika cin tuwo a kanki yana wanke kwanon, idan Ameerah ta gane kina tsoron ta to kin shiga uku bakisan wannan shegiyar bace, kin tsaya kina wani bata hakuri baki gaggaya mata magana ba, ita da saurayin nata."
"To me zan ce mata Miemie jiran ki fa nake wlh ni ba leken saurayin ta nake ba."
"Dalla ni ki daina min wannan maganar kayan haushin, kar kiyi baki ki iya rama waba, Ameerah da kike gani rashin mutuncinta ya wuce duk in da kike zato."
shuru tayi bata ce komai ba.
Kamar ko da yaushe Umma Karima ce zaune gaban bokanta, babu d'ankwali babu takalmi.
a gaban su wata tukunyar kasko ce tana tafarfasa ita kad'ai tamkar yana kan garwashin wuta.
boka Mali ya leka cikin tukunyar
cikin kazamyacciyar muryarsa ya kece da dariya
"Hahaha aiki na kan wakana sai dai har yanzu kin kasa samo cikon na uku har yanzu aikin ki bai cika ba,
bazaki tab'a samun yadda kike so ba har sai kin jefa duka ukun cikin tukunyar nan."
cikin damuwa Umma Karima ta ce
"Boka duk yadda zanyi nayi na kasa samu babu wata hanyar da za'a bi a cikita min aiki na in yaso sai na biya kawai."
Sandar tsafin sa ya buga kasa yayi wasu surkullensa kana ya zaro wata laya ya ce ya jefata cikin tukunyar nan,
wani irin kumfa had'e da bakin hayaki fuuu ya taso cikin tukunyar.
ya ce
"Duk sanda layar nan ta gama narkewa har idan baki samo cikon na ukun ba to aikin ki ya lalace, sai dai a fara daga farko."
da sauri ta ce
"A'a boka hakan bazama ta faruba ko ta halin kaka zan nemo bazan bari aikin shekara da shekaru ya tashi a banza ba."
"Hahaha kin yi tunani mai kyau maza ki tashi ki bazama nima."
Umma Karima ta mike a bujajan tayi waje bayan ta zazzage masa bakin jaka.......!
8
Sosai Aunty ta dage wajen koyawa Feeryal nau'ikan girki kala-kala, bata yadda ta barta kara zube kamar yadda wasu masu kud'in suke yi wa 'ya'yan su ba,
komai sai dai masu aiki suyi ba dai 'ya'yan su ba, suna ganin wai hakan gata ne da yawa sai sunyi aure suke had'uwa da kalu bale daban-daban a gidan auren.
duk da Aunty d'iyar masu kud'i ce bata taso cikin tarbiyyar irin wad'an can 'ya'yan masu kud'in ba.
shiyasa ta zage damtse wajen koyawa Feeryal abubuwa da dama da suka shafi cikin gida.
yawan zama da Miemie takeyi a sashin itama ta karu da wasu abubuwa da dama.
Aunty ce zaune a parlour tana video call da Hajja Umma.
jiya aka sami nasarar zakulo mutum biyu daga cikin tawagar 'yan d'aukar amarya, da hukuma suke ta kan bincike a kansu har yanzu.
Aunty tace
"Amma dai Hajja Umma babu wata matsala ko?
ni fa tun da naji ance an kuma kama wasu 'yan gidan sa duk a tsoro nake,
kar sauran da suke a b'oye suce zasu fito d'aukar fansa."
Hajja Umma ta ce
"A'a babu komai insha'allah, wannan yaro Sadam Abokin Nasir Allah dai ya saka miki, yaron akwai kokari jiyan nan kusan da shi muka wuni a gidan nan da jami'an su, da daddare ya turo jami'an su biyu da folisawa biyu da Nasir ya turo
har muka waye gari yau da su,
har yanzu ma suna nan,
amma naji Alhaji yana cewa anan zasu cigaba da zama har zuwa a kare bincike."
Aunty ta sauke numfashi tare da cewa
"To Allah ya dad'a tsarewa."
"Amin ya Allah, wai ni kam ina kishiya take ne banji d'uriyar ta ba."
"Tana d'aki ai bata san muna waya da ke ba da kin ganta."
Aunty ta d'aga murya ta wala mata kira,
ta fito da sauri tana amsa kiran
"Taho ga Hajja Umma tana niman ki."
da sassarfa ta karaso inda Aunty take ta zauna gefen ta tare da kwantar da kanta a jikin ta, ido ta waro ta ce
"La Hajja Umma shine tun d'azu baki neme ni ba ko."
"A'a nunar gwanda bagashi na nemo ki ba yanzu,
kwana biyu da ban gankiba sai naga kin dad'a kumbura, kazar turai jikin nan ya dad'a komawa tumatur sharaf."
baki Feeryal ta turo ta ce
"Ba Abba ya ce ya ce ki dai na fad'a min ba, ke da shi,
Ammie na kashe ki kira min mijin ta muyi hira."
"A waya kawai zaki ganshi ni kuma ina tare da shi a nan."
"Ai baki sani ba Hajja Umma kullum sai yabi jirgi yazo gurina,
ke kina can kina ta kan cewa masu aiki,
kuyi kaza kuyi kaza, kar ku saka gishiri da yawa a abincin almajiran nan fa ku sa musu magi ya ji."
dariya duk suka fashe da shi.
Aunty ta ce
"Au haka Hajja Umman take fad'a."
kai ta gyad'a tana dariya ta ce
"Kullum sai Abba ya shigo yace ta zauna ta huta ta barsu su suyi aikin, yana fita zata tashi taje bata zama tarika kai kawo ke nan, bata ko gajiya,
ai shiyasa Abba ya ce yafi so na ma, ita kullum bata hutu gata da masu aiki."
dariya Aunty tayi tana dungurin kanta.
Maryam da ta shigo ta tadda suna wayan ta leko cikin wayar Feeryal ta washe baki
"Aunty Maryam ina kika je ne?."
"Gidan su Haulat yanzu kuwa muke hiran ki da ita, tana tambaya ta yaushe zaki dawo."
"Ai nakusa dawowa, sai dai bana so na rabu da Ammie na ne."
tayi maganar tana dad'a kwanciya jikin Aunty.
"To ai sai ku dawo tare da Ammie'n naki."
cewar Maryam tana mata hararar wasa.
Wayar ta da ke rike a hannunta ne ya yi kara,
ganin Miemie ce ke kiran nata yasata d'agawa.
"Hello Miemie."
daga cikin wayar Miemie ta ce
"Feeryal yi sauri kizo kiji wani magana."
"Wacce magar Miemie?."
jin shiru yasata ciro wayar a kunne taga har ma ta kashe kiran.
ganin Aunty sun kama wani hirar da Hajja Umma sai ta fice zuwa sashin su Miemie.
Har ta kusa rabin isa sashin nasu kiran Miemie ya kuma shigowa wayar ta.
"Yauwa Feeryal tsaya ma kawai bazan zo."
"Ai gashi na fito ma bari na karaso."
"To tsaya-tsaya ma kawai bari ni na fito."
Miemie ta fad'a tare da katse kiran.
Feeryal ta sauke numfashi tana fad'in
"Oh Miemie."
Gefe ta matsa ta jikin wasu dogayen bishiyoyin fula da suke jere a gurin, tana jiran fitowar ta.
maganar da taji ta cikin bishoyoyin ne yasata juyawa da sauri ta d'an leko ta sakankanin flaws d'in.
karaf suka had'a ido da Ameerah da ke zaune da saurayin ta suna hira kan kujerun da suke cikin gurin.
saurayin ya mike da alama sun gama hirar zai tafi.
da sauri ta d'an matsa baya.
Tana tsaye har motar saurayin ya fita a gidan.
a razane ta waigo jin an buga kafad'ar ta ta baya.
Ameerah ta bita da kallon sama da kasa ta ce
"To sannu bakar munafuka, wacce munafurcin ne yakawo ki nan kika zo kina leka min saurayi,
Allah ya toni asirin ki saurayi na kike lekawa."
murya a sanyaye Feeryal ta ce
"Kiyi hakuri wlh bansan kuna nan ba, kuma ni ba lekensa nake yi ba."
"Karya kike yi leka shi kike yi ai ina kallon ki,
sai kin fad'a min uban da yasa kike lekashi, ko naci uban ki da duka anan, dama ina da cikin ki."
"Allah Ameerah ni ba leken sa nake ba, ban ma san kune a gurin ba."
Miemie da ke tahoto ta bud'e baki tana kallon yadda Ameerah ke d'agawa Feeryal murya ita ko sai magiya da kwantar da kai take kamar zatayi kuka.
da sauri ta karaso gurin ta na fad'in
"Ya ya akayi wai mene ne?."
da sauri cikin tsiwa Ameerah ta ce
"Kamata nayi tana leka min saurayi."
Feeryal tayi narai-narai da ido ta ce
"Allah ba leken sa nake ba magana naji na leka bansa su bane."
Miemie ta ce
"To lallai saboda Feeryal d'in ta rasa aikin yi sai ta tsaya leken saurayi kamar wacce ta rasa samari,
ta ce ba leka miki saurayi tayi ba ai sai kiyi hakuri ki rabu da ita."
"Karya take lekashi take yi ai na ganta da ido na."
Ameerah tayi maganar cikin hayagaga.
Miemie ta ce
"To meye a jikin saurayin naki da za'a leka shi,
ana ta ce miki kiyi hakuri kina ta wani d'agawa mutane murya to ta kalla kiyi abin da zakiyi,
dalla wuce mu tafi, Feeryal tayi abin da zatayi."
"To idan zan mata abun da zan matan zaki hana ne,
kema bakifi karfin na had'a da ke ba bana son shishigi."
Miemie ta dalla mata harara ta ce
"Kar ki yadda kice zakiyi min ehe ni ba Feeryal bace kul in gaya miki,
kisan wad'an da kike wa rainin wayon ki, kar ki yadda kice zakiyi min,
dalla wuce mu tafi kin tsa tana gaya miki magana har kina bata hakuri."
taja nannu Feeryal fuuu suka kara gaba bata fasa mitar ba.
"Ki ci gaba da tsayu kowa yarika cin tuwo a kanki yana wanke kwanon, idan Ameerah ta gane kina tsoron ta to kin shiga uku bakisan wannan shegiyar bace, kin tsaya kina wani bata hakuri baki gaggaya mata magana ba, ita da saurayin nata."
"To me zan ce mata Miemie jiran ki fa nake wlh ni ba leken saurayin ta nake ba."
"Dalla ni ki daina min wannan maganar kayan haushin, kar kiyi baki ki iya rama waba, Ameerah da kike gani rashin mutuncinta ya wuce duk in da kike zato."
shuru tayi bata ce komai ba.
Kamar ko da yaushe Umma Karima ce zaune gaban bokanta, babu d'ankwali babu takalmi.
a gaban su wata tukunyar kasko ce tana tafarfasa ita kad'ai tamkar yana kan garwashin wuta.
boka Mali ya leka cikin tukunyar
cikin kazamyacciyar muryarsa ya kece da dariya
"Hahaha aiki na kan wakana sai dai har yanzu kin kasa samo cikon na uku har yanzu aikin ki bai cika ba,
bazaki tab'a samun yadda kike so ba har sai kin jefa duka ukun cikin tukunyar nan."
cikin damuwa Umma Karima ta ce
"Boka duk yadda zanyi nayi na kasa samu babu wata hanyar da za'a bi a cikita min aiki na in yaso sai na biya kawai."
Sandar tsafin sa ya buga kasa yayi wasu surkullensa kana ya zaro wata laya ya ce ya jefata cikin tukunyar nan,
wani irin kumfa had'e da bakin hayaki fuuu ya taso cikin tukunyar.
ya ce
"Duk sanda layar nan ta gama narkewa har idan baki samo cikon na ukun ba to aikin ki ya lalace, sai dai a fara daga farko."
da sauri ta ce
"A'a boka hakan bazama ta faruba ko ta halin kaka zan nemo bazan bari aikin shekara da shekaru ya tashi a banza ba."
"Hahaha kin yi tunani mai kyau maza ki tashi ki bazama nima."
Umma Karima ta mike a bujajan tayi waje bayan ta zazzage masa bakin jaka.......!
8