← Book details Bakon Munafuki Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 8 OF 60

Sashe 8

Bakon Munafuki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Su kuma bangaren mazan yana daga can baya idan an fita daga kofar sashen na iyayen su matan da na su Amaal.Anan akayi musu nasu bangaren suma kamar yadda na su amaal din yake.

Sai da su dakunan su kowanne daki mutane biyu ne aciki. Dakin da ya zamana a bangaren su Amaal din maaikatane aciki su kuma dakin ya zamana na Yaya babba wato sadeeq . Babban da ga amb. Junaid..

°°Bayan wayewar gari sosai ainun. Amb. Junaid da kansa ya kikkira matan na sa awaya ya sanar musu shi fa tun asubah ya koma bangaren Hajiya. Dan haka achan zai karya kumallo zai kumayi wanka.

Ya nanata musu cewar idan sun ci abindin safen su hanzarta su yiyyi wanka su shrya don zasu zagaya gidajen yan uwa da basu shisshiga ba. Kasancewar daren jiya yaja sosai shysa basu shiga ko'ina ba.

Maaikata ne suka kakkai musu abincin karin kumallon. Duk abunda zasu bukata an tanadar musu. Wani abincin ma ko tabashi ba suyi ba.

Tuni kowannen su ya fara shiri. Masu shiga bandaki nayo wanka. Masu rage ciki nayi. Masu saka kaya da sauran su. Kowanne dai ya zama cikin shiri.

Hajiya. J ta shiga wajen Amaal dake tsaye tana bottling din buttons din doguwar rigar da ke jikin ta. Tundaga saman rigar har zuwa kasanta wasu manyan botira ne masu girma da kyakyali. Sai kananan botiran a hannun rigar ta da ake maqale su. Mayafin rigar ma ya sha adon botiran gefe da gefe.

"Wai baki gama ba amaal? Ni meyasa ne kike da shiririta? Kinfi so kullum dai ache keche da lefi? Sarkin makara. Kullum ke ake bari a karshe a shirin komai. Sanyin jikin ki yayi yawa. Matso nan ni na karasa saka miki."

"Hayateey kiyi hakuri." Ta fada hade da matsawa wajen mahaifiyar ta ta. Ta kama hannun rigar ta na sakala mata botiran

"Gyara sanyin jikin nan zaki Amaal.. Kinga dai abbiey din ku yace sai kun maimaita ss2-ss3 anan saboda university. Don haka doke ki zama mai shirya wa da wuri. Yanzun kin ga makaranta daya zai saka ku. Ba kamar can ba ne da makaranar ki daban. Nan yana cewa ba zakuyi karatu waje daya ba zaa fara sukar sa. Duk kuwa da su ne kecin zalin ki. Kinji ko?"

"Tohm Hayateey in shaa Allah. "

"Allah ya miki albarka. "

"Aamin Hayateey tare da ke."

"Yauwa muje naga sun fiffito su ma."

"Tohm."

Takalmi ta zura, kafafunta sanye cikin safa baka. Tana gaba mahaifiyar ta ta na biye da ita a baya sanye take ita cikin doguwar rigar leshi dinkin bubu ta rufa babban mayafi.

Suna fita harabar gidan da harararrakin haj hadiza da ruwaida suka fara cin karo. Sunata doka musu ita. Ciki harda tagomashin ta yaran su dake gefe suma sun dakko halin.

Haj hadiza tayi gaba tana jan dogan tsaki. Badan amb junaid yace lalle su tafi a ayari dukan su ba kar wanda yayi gaba yabar wani da tuni sun dade da tafiya.

"Shafaffy da mai." Ta fada hadi da waiwayawa baya ta sake bankama haj jameelah harara da amaal.

A haka suka karasa sashen Hajiya Maryam mahaifiyar su Amb. Junaid.

Tuni har wasu yan uwan sun sun zo wajen hajiyar dubada motoci dake faffake na alfarma...

___
_ADVERT👇_

_YERWA INCENSE AND MORE :(MASARAUTAR KAYAYYAKIN KAMSHI)_

_INA MA'ABOTA TURARE.. KADA KU MANTA SHI FA KAMSHI RAHAMA NE, KUMA TSAFTA CE. TSAFTA KUMA TABA CIKIN IMANI ...KU MATSO KUSA.. MUN KUMA ZUWA DA HAJAR KAYAYYAKIN *YERWA INCENSE AND MORE* DOMIN SAMUN ZAFAFAN TURARUKAN WUTA NA GIDA, KAYA, JIKI, TSUGUNNO, GASHI... AKWAI KHUMRAHS MASU DADI YAN BORNU, CHADI, SUDAN DAMA SENEGAL, AKWAI OIL PERFUMES, DA TURARUWAN MOPPING DANA WANKA DANA WANKI DANA GADO DA KUJERU DA BANDAKI DA DRAWER DA MOTOCI.. AKWAI MAN GASHI NA FESAWA ME SA KAMSHI DANA KITSO.. AKWAI KAYAYYAKIN KAMSHI DANA GYARAN JIKI SOSAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA.._

_ADIRESHI: KANO.. AMMA SUNA TURA KAYAN SU KO'INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE..._

_INGANCI KYAU RAHUSA DA DADEWA A GIDAH DA KAMSHI SAI KAYAYYAKIN TURAREN YERWA INCENSE AND MORE_

_NAMBAR WAYAR SU:08095215215, INSTAGRAM/THREADS/TWITTER: yerwaincense_and more_

_YOUR NUMBER ONE STOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS... THEY'VE GOT YOU AND YOUR HOME COVERED_

*_MATSO KIJI_*👂🏼👂🏼👂🏼👂🏼🔥🔥🔥🔥🔥🔥

*_KINA DA LABARIN 'YAN BIYAR DINNAN SARAKAN ZAQAQAN LABARAI SUN SAKE DAWO MUKU DA SABON SINQI SINQIN LABARANSU_*

_LABARAI NE MASU TSANANIN ZAQI DANDANO DA TSAYAWA A ZUCIYA_

_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_

*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*

FURAR DANKO
Billyn Abdul

-ZAFIN KAI
Mamuhgee

-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma

-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo

Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400

Pay at👇

1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim
Sai katura shedar biyanka anan👇

09032345899

Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070

VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k

_MUTANEN NIJAR KU TUNTUBI +22799643131_

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

*THANKS FOR CHOOSING US*🥰

Zafafa🫶🔥
[8/9, 1:37 AM] Hafsaat💞: _BM_

_NA:_

_NANA HAFSATU_

_09_

    Bakunan su dauke da sallama suka shiga babban parlorn Hajiya. Wasu daga cikin iyalin ta sun zo suna zazzaune.

Amb. Junaid na daga gefen hajiyan a a kasa yana zaune. Ya sanya hannun sa duka biyun yana yiwa kafafun hajiyan tausa.

Amsa sallamar yan parlorn suka yi naki daya. Domin a ranar ne mahaifin su zaa dawo da shi daga kasar south Korea inda aka kaishi don yo masa eani aiki a hakarkarin sa.

Dukkanin yaran na sa sun hallara da sauran yan uwa da 'ya'yayan su.suna tsammatar dawowar tasu

Hajiyan na zaune ne a babbar kujera me cin mutane uku.

Sai Babban wansu Alhaji Nuraddeen, 'Ya'yan yan uwa nace da shi, Bappah na kandemi, Sai kanin sa da ke binsa a kusa da shi, Honorable Minister of finance, Alhaji Jalaludden  Muhammad anace da shi Bappahn Hajiya... Sunan kanin hajiyar yachi mai rasuwa.

Sai ta ukun su wato mabiyar Alhaji Jalaludden... attorney general ce ta kasa, Justice Fateemah suna ce da ita (Gwaggon court)..

Sai Bappah Abdullahi. Wato farfesa/professor Abdullahi suna ce da shi Bappahn Istanbul. Saboda ya zauna a Istanbul.

Daga gefen wasu tumtum da suka sha kawaatuwa da wani irin kyalkyalin beza kuma Dr. Aisha ce a zaune ta mike kafafun ta. Gaban ta da kofin tangaran ne dauke da kunu aciki tana juya shi da sukarin data zuba.

  Baki daya dai yaran hajiyan sun hallara....

Su Hajiya hadiza suka karasa shjga cikin parlorn suka zaazauna. Daya bayan daya suka fara gaggaushe da juna..

Amj Junaid na daga gefen Hajiya shi dai yana mai cigaba da matsa mata kafafu.. wasun su sun amsa musu fuskokin su a sake wasu daga ciiki kuma fuskar nan tasu babu yabo babu fallasa.

Alhaju Jalaludden wanda shine babban Yayan su bayan Alhaji Nuraddeen. Mikewa yayi yana gyaran zaman babbar rigar jikin sa.

Amb junajd ya daga idanu ya dube shi alokacin ya kai kansa ga agogo yana son yaga lokaci

Wata harara mai tattare da tsantsar tsana da kyamata ya zuba wa amb junaid. Ya karasa wajen hajiyar tasu ya zauna daga gefe har yana mirje yatsun amb junaid dake maya tausa abisa sani kuma ya take sun.

"Hajiya ni zan dan fita..."

Hajiya bacci ya fara fusgar ta. Da sauri ta dan bude idanun ta,

"Iyye? Magana ake?"

"Jalaludden ne hajiya..."

"Ina zakaje kuma?"

"Zan dan futa ne Hajiya na shawo iska....."

"Ba zaka jura su dawo ba?"

"A kofar gidah zan dan huta . Nan din ne acike."

"Toh shikenan Allah yayi albarka."

"Aamin Hajiya."

Mikewa yayi daga zaman da yayi a gefen ta. Ya fuce da sauri. Yana fita.Alhaji Nuraddeen yabu bayan sa.

Professor Abdullahi ya daga idanu ya dube su ya mayar kasa kawai yana jujjuya kai. Kasan makoshi yake furta,

"Allah ya kyauta...."

Amb junaid baki daya jkkin sa sai ya sake masa sanyi. Ya rasa wacce iriyar wutar kiyayyayar ce ke sake ruruwa a zukatan yan uwan na sa dake suke uwa daya uba daya.

"Junaidu kaga yadda nake renovating asibitina kuwa?" Cewar gwaggo indom wato dr Aisha.

Ta karkato masa kan iPad din nata yana kalla... Murmushi yayi sosai. Kafin ya mike ya koma inda take zaune ya saka hanu ya karbu ipad din yana zooming hotunan asibitin farfajiya da cikin sa..

Ma shaa Allah Allah yasa an fara a sa'a..Allah ya temaka Amin."

"Aamin suka hada baki."

Suna dai zazzaune baki daya wasu na magana wasun su na daddanna wayoyin hannun su ya yin da wasu ke kallon shirin da ake haskawa a talabijin na tashar Aljazeera.

"Zo nan takwara ta ...." Hajiya Maryam ta kira Amaal da ke gefen mahaifiyar ta a zaune.

"Tohm Hajiya.." Ta mike da sauri ta nufi wajen hajiyan ta tsugunna

Hajiyan ta kamo hannun ta ta rike cikin nata tana mai duban idanun ta,

"Sannu takwara... Je ga daki can zaki ga magogin goro a gefen gado ki dakko mun."

"Tohm Hajiya."

Tashi tayi da sauri ta nufi dakin ta dakko ta kawowa Hajiya.

"Bari na goga miki."

"Allah yayi albarka..."

"Ina safwanu mai gidan nawa?" Hajiya ta tambaya tana duban inda sauran yaran suke a zazzaune..

Hajiya hadiza ta dashare baki. Da dazu da hajiyan ke yiwa Amaal magana ita kadai sai kumbura fuska take amman da ke hajiyan ta tambayi nata dan yanzu sai washe hakora take kaman gonar auduga..

"Kai tashi Hajiya na kiran ka.."

"Kyale shi idan ya na hutawa... Ga kuma Abubakari, ga Na'eelah nan ga ...."

"Najwa..." Haj Hadiza ta amsa ta tanata murmushi ita ga mai tarin 'ya'ya..

"Ga kuma biyu kyautar Allah ...Ikram da Ikhlas.." Ta saka yatsa tana mai nuni da yan biyun Hajiya Ruwaida

Hajiya Ruwaida ma sai kuma fuskar ta ta gauraye da farin ciki.

Duk dai Hajiya ta kamo sunayen su daya bayan daya tana musu wasa. Duk kuwa da dattijuwa ce me kamewa, batada rikicin tsufa sannan bata wasa da jikoki irin wasan nan da yake wuce gona da iri. Tana da matukar kwarjini shi yasa ko jikokin nata suke nutsuwa idan suna tare da ita..

"Ku tashi mu lalleka a gaysa." Cewar amb. Junaid daya mike daga inda yake a zaune.

Ya isa wajen Hajiya ya durkusa cikin girmamawa yace,

"Hajiya bari mu shisshiga gidajen a gaysa."
Chapter 8 · 0% Book details