Sashe 42
Bakon Munafuki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sai da suka shige cikin gidah sannan ya juya ya koma wajen abokin sa, abokin har yayi wajen mota yace da shi,
"Zo ka raka ni ciki "
"Okay tohm"
Sashen Hajiya Maryam suka nifa... Ba mutane sosai. Suka gaggaysa da su. Duk aka fita aka basu waje su da hajiyan. Ya sake durkusawa ya gayshe ta cike da girmamawa,
"Ango ango"
"Na'am hajjaju...." Ya faada a kunyace,
"Allah ya sa albarka da alkhairi kaji ko"
"Ameen hajia... Dama wajen ki na zo" ya fada yana lankwasa yatsu cike da kunyar data dabaibaye shi
"Toh Allah yasa muji alkhairi...."
"Aameen Hajiya.."
Abokin nasa ya mike ya basu waje ya fita.. hajiyan tace,
"Ina sauraron ka? Ko mu koma daaka yafu sirri?"
"Nanma ya isa hajia"
"Toh Allah yayi albarka"
"Aamin Hajiya... " Ya sauke nannauyar ajiyar zuciya,
"Ina sauraron ka...."
"Hajiya dama zuwa nayi na roke ki abisa abunda nake tafe dashi. Kuma ina fatan zaki duba zance na da tsanaki ki goyi bayana"
"Toh... Allah yasa muji alkhairi. Ina sauraron ka"
Hisham ya sake muskutawa yace,
"Dan Allah Hajiya ku dbi girman biyayyar da Maryam tayi muku"
"Wani lefin tayi?"
"Wallahi ba abunda tayi Hajiya. Zan iya ce miki tunda nake da ita Allah bata tabamun wani lefi wai dazesa naji haushin ta ba. Tana bani girma sosai. Kuma tanada nutsuwa da hankali ga biyayya. Don biyayyar cema ta amince zata aureni"
"Ina sauraron ka"
"Wato Hajiya nayi duba na tsanaki, Kuma na sassaurari wa'azi duk da ba wai nace abu ne mekyau ba kasancewar budurwa ma ca akai a mata zabin miji bazawara kuma a barta ta zaba da kanta"..
"Wannan zance naka haka yake"
"To Hajiya.... Magana ta gaskiya idan na amince aka daura aure na da Maryam wallahi wallahi wallahi na kwareta... Kuma Allah zai mata sakayya"
"SubhanAllahi meyasa kache haka hashimu? Bayan kowa yasan kai da ita kuna kaunar juna?"
"Wallahi hadin zance na ne na samu su baba nace da su soyaya mike ai muna waya da magana ta kafar sadarwa. Tabbas muna waya da magana ta kafar sadarwar amman karatu nake koya mata kuma wallahi amatsayin Yaya da kanwa muke maganar. Ni ne na sawa raina wani kuduri naji Ina son kasancewa da ita a inuwar aure. Na samu iyaye na da maganar sukace sai sun tabbatar idan tana sona.. da akayi maganar anan parlorn naki nema bata nuna ba haka bane tache eh munayi ta kuma amince. Wallahi hajiya na ha'inceta idan har aka daura auren nan gobe. Wallahi wallahi biyayya kawai takeyi amman ...
Bai karasa ba Hajiya ta girgiza kai kawai tace,
"Idan na fuskance ka so kake a fasa daura auren nan gobe idan Allah ya Kai mu?"
"Eh...."
"Me zaku gayawa mahaifan ku ?"
'wallahi Allah maryaam batada masaniyar dukkanin abunda na gaya miki. Ni na yanke shawara ta. Saboda zuciyata ta kasa nutsuwa. Banason Allah ya kamani akan abunda ba haka bane. Na mata kazafi na nuna da yardarta itw kuma tayi biyayya ta amince. Hajiya dan Allah ki saka baki kada a daura auren nan gobe idan Allah ya kai mu"
"Tirkashi..." Hajiya tafada tana mai sauke nannauyar ajiyar zuciya. Baki daya itama kanta ya kulle. Ta cigaba da cewa
"Ai idan kukayi auren zaku daidaita kanku hashimu .. zata so ka sannu ahankali " Ta fada cikin tabbatarwa, Ko kadan bata damu da ba daidai take fadan sunan nasa ba. Hisham ne take kiran sa da hashimu
Ya girgiza kai yana hada hannuwan sa yace,
"Wallahi bazan iya auren maryam ba hajia. Na amince a hadani da koma wacece acikin zuriyar kandemi amman banda Maryam ba zan shiga hakkin ta ba."
"Ni bansan me zan fada ba hashimu. Bari a kira su gaba daya.. Duk hukuncin da suka yanke shine daidai.. Ungo dannomun lambar Nuraddeen." Ta Mika masa yar wayarta
Karba yayi ya kira mata Bappah Nuraddeen. Ta saka a kunne bugu bjyu ya dauka ta sheda masa ya tatttaro kan kowa suzo bangaren ta harda Amaal.
Ta kuma tashi ta shiga dakin mai gidan ta Alhaji Muhammad shima ta kirawo shi. Suka gaysa da Hisham ya zauna akan kujera. Hisham din na gaban su a zaune kansa akasa
Ba jimawa kuwa sai ga tuttulowar su gaaba daya. Ciki harda sarki Junaid da iyayen Hisham din. Gaba daya dai suka hallara
"Maimaita abunda kache hashimu"
"Hisham ne Hajia" Yusra ta fada tana dariya
Duk suka danyi Daria. Hisham din ya dan saci kallon mahafin sa. Muryar sa na dan rawa ya zayyane komai tun daga farko ya sake fada ya karkade da,
"Wallahi wallahi wallahi bazan iya auren maryaam ba. Idan na bari aka aura mata ni hakika na cuceta, Na ha'inceta, na zalunceta na kuma shiga hakkin ta kuma Allah ba zai bar ni ba. Tunda karya na hada na fada muku cikin tabbatarwa. Amma ita ta amince saboda ganin girman ku da tsananin biyayyar ta tace eh hakane muna soyayya. Wallahi Allah amatsayin Yaya da kanwa muke da ita tamkar na jini. Hasalima ni coaching dinta nake Ina koya mata wasu abubuwan na makaranta ta waya ko messages . Bappah, Baba, Kaka, Hajiya... Dan Allah ku gafarce ni.. ku karbi roko na kada ku aurawa Maryam ni gobe idan Allah ya kaimu wallahi kamar yadda na fadawa Hajiya yarinyar na batada masaniyar abunda nake gaya muku dai dai da rana daya batada daba mun complain na zaluntar ta da nayi ba nace muna soyayya har aka sa mana ranar aure ba, Bata taba nuna mun ba ai karya na shirya nace muna soyayya ba.. Dan Allah karku aurawa Maryam ni. Karku bata mata rayuwa ta auri wanda takewa kallon yayan ta na jini .... Ni Hisham na amince a aura mun wata daga cikin wannan zuriyar na kandemi goben idan Allah ya kai mu.. amman Dan ALLAH jar a aurawa maryam ni. A barta ta auri wani daban.. Dan Allah"
Duk sukayi shiru...Tamkar mafarki ko a kallon wasan kwaikwayo na talabijin. Alhaji Abubakhar ya mike cikin zafin nama ya tattare kasan hannun rigar sa jikake,
'Taasss.. Faaas, Chasss' Ya sharara masa maruka guda uku lafiyayyu a gefe da gefen fuskar sa.
"Mutumin banza... Daman sharri kayi mata ka cuce ta? "
Ya sake daga hannu zai sake marin sa Bappah Nuraddeen ya rike masa hannu. Sarki Junaid ma ya tashi ya janye Hisham daga wajen ya mayar da shi gefen da yake,
"Meye abun marin nasa? Haba Abubakhar? Idan ka bibiyama kila amaal dince ta nuna bata so" Cewar sarki junaid.
"Walahi daidai da minti daga maryaam bata taba nuna mun batason aurena ba. Ba kuma taba cewa ai karya nayi mata ba ba soyayya mike ba. Wallahi Allah " Hisham ya fada cikin tabbatarwa
"Yo ai ni gaba daya ma na rasa abunda zance..."Bappah Nuraddeen ya fada yana tallabe habar sa cike da damuwa
Amaal dake gefen Hajiya jamila sai raba idanuwa take. ita da tai tasan kalau fa suka rabu da shi ya rakata har kofar shiga sashen su.
Haka dai akayita maganar ana neman bakin zaren. Dakyar dai aka hakura kan ba zaa daura auren da Amaal din ba ganin yadda Hisham yake zubar da hawaye sosai kan inde aka daura to wallahi ya shiga hakkin ta kuma Allah ba zai barshi ba.
Ana cikin maganganun ne Hajia maryam tace
"Wai har yanzu dan yaye be kira waya ba an san inda yake? Tukunna ma yana Ina jama'a?"
Duk sukaita tofq albarkacin bakunan su. Yusra dake gefe tace,
"Na kira aminin sa. Habibi Talba yace Hamma Al-mustapha ya tafi Manchester England"
Bappah jalaludden ya bude baki yace,
"Ina?"
"Manchester"
Ya dubi hajia Jidda mahaifiyar su yusra yace,
"Ya gaya miki me?"
"A'ah..."
"To me yaron nan yake nufi?"
"Bappah Al-mustapha ba zai iya zama ana auren amaal ba. Shi yasa ya tafi." Aayaan ya fada cikin tabbatarwa.
"Wai yaron nan dama yana kan bakan sa?"
Hajia maryam tace,
"Ni kallon sa kawai nake... Ya bude baki yayi mata magana yaki sai zurfin ciki. Yadda yake nuna mata kamar yafu kowa tsanar ta a duniya. Bayan tun tana zanin goyo yake kaunar ta."
"Wai Al-mustapha dai namu?" Bappah junaid ya tambaya yana zare idanu,
"Shi dai...Muma rufe mana yake. A nasa haukan ba zamu gane ba. Tun muna Buckingham muka sani. Hotunan ta tun tana karama har na wanda ta girma, ko a'ina ya same su oho, yana nan dasu."
"Ammw yaron nan sakarai ne"
Ita dai Amaal jin su take tamkar a mafarki. Duk abubuwan da suke fada yana shifa ya futa ta dayan kunnen na ta. Al-mustapha kuma? Kai gaskia ba dai ita ba. A duniya ba wanda ya tsane ta sama da shi
"Ni ma na lura yana son ta sosai... Wanda ya zauna anan dinnan ko ranar da muke nan duka?" Hisham yake tambayar Aaayan.
"Shi dai. Ai mugun gara ne dab wahala. Wai shi sharukan baban soyayya ya hakura ya bar ma ka."
Sika saka dariya baki daya... Bappah Abdullahi yace,
"Kuma ba shine ba shida lafiya bane bayasan damuwa sosai?"
"Shine . Can daya Wawa. Ku rabu da shi ya karaci zaman sa acan idan yaga dama ma kar ya waiwayo gidah gaba daya" bappah jalaludden ya fada cikin halin ko in kula
"Ba za'ai haka ba Yaya.. da kai da kaya ai duk mallakar wuya me... Abunda yayi Al-mustapha shi yayi Amaal "sarki junaid ya fada
"Ba fa za'ai abundq kake tunani ba. Ni ba sakarai bane. Ba zaa shiga hakkin yarinya ba "
"Ni na amince tunda 'da na ne" sarki Junaid ya fada
"Ni kuma ban amince ba tunda 'ya ta ce" Cewar Bappah Jalaludden
Yan parlorn suka saka dariya baki daya. Bappah Nuraddeen yace
"Mutane sunzo dai ko'ina gari ya cika idan baa daura aure gobe ba da matsala. Idan Kuma akwai wata hanyar da za abi to tun yanzu a sanar musu a daren nan kan an fasa daurin aure gobe "
"Zaa daura aure inshaa Allahu .. hjsham da ne awaje na. Kuma ya roki alfarma dole zan cika masa .. wa kake so acikin zuriyar kandemi ka fada gobe da yardar Allah sai a daura muku aure kaji?"
Hisham yayi shiru can ya daga kai yana kakaro murmushi yace,
"Duk wadda aka bani Bappa "
"Zo ka raka ni ciki "
"Okay tohm"
Sashen Hajiya Maryam suka nifa... Ba mutane sosai. Suka gaggaysa da su. Duk aka fita aka basu waje su da hajiyan. Ya sake durkusawa ya gayshe ta cike da girmamawa,
"Ango ango"
"Na'am hajjaju...." Ya faada a kunyace,
"Allah ya sa albarka da alkhairi kaji ko"
"Ameen hajia... Dama wajen ki na zo" ya fada yana lankwasa yatsu cike da kunyar data dabaibaye shi
"Toh Allah yasa muji alkhairi...."
"Aameen Hajiya.."
Abokin nasa ya mike ya basu waje ya fita.. hajiyan tace,
"Ina sauraron ka? Ko mu koma daaka yafu sirri?"
"Nanma ya isa hajia"
"Toh Allah yayi albarka"
"Aamin Hajiya... " Ya sauke nannauyar ajiyar zuciya,
"Ina sauraron ka...."
"Hajiya dama zuwa nayi na roke ki abisa abunda nake tafe dashi. Kuma ina fatan zaki duba zance na da tsanaki ki goyi bayana"
"Toh... Allah yasa muji alkhairi. Ina sauraron ka"
Hisham ya sake muskutawa yace,
"Dan Allah Hajiya ku dbi girman biyayyar da Maryam tayi muku"
"Wani lefin tayi?"
"Wallahi ba abunda tayi Hajiya. Zan iya ce miki tunda nake da ita Allah bata tabamun wani lefi wai dazesa naji haushin ta ba. Tana bani girma sosai. Kuma tanada nutsuwa da hankali ga biyayya. Don biyayyar cema ta amince zata aureni"
"Ina sauraron ka"
"Wato Hajiya nayi duba na tsanaki, Kuma na sassaurari wa'azi duk da ba wai nace abu ne mekyau ba kasancewar budurwa ma ca akai a mata zabin miji bazawara kuma a barta ta zaba da kanta"..
"Wannan zance naka haka yake"
"To Hajiya.... Magana ta gaskiya idan na amince aka daura aure na da Maryam wallahi wallahi wallahi na kwareta... Kuma Allah zai mata sakayya"
"SubhanAllahi meyasa kache haka hashimu? Bayan kowa yasan kai da ita kuna kaunar juna?"
"Wallahi hadin zance na ne na samu su baba nace da su soyaya mike ai muna waya da magana ta kafar sadarwa. Tabbas muna waya da magana ta kafar sadarwar amman karatu nake koya mata kuma wallahi amatsayin Yaya da kanwa muke maganar. Ni ne na sawa raina wani kuduri naji Ina son kasancewa da ita a inuwar aure. Na samu iyaye na da maganar sukace sai sun tabbatar idan tana sona.. da akayi maganar anan parlorn naki nema bata nuna ba haka bane tache eh munayi ta kuma amince. Wallahi hajiya na ha'inceta idan har aka daura auren nan gobe. Wallahi wallahi biyayya kawai takeyi amman ...
Bai karasa ba Hajiya ta girgiza kai kawai tace,
"Idan na fuskance ka so kake a fasa daura auren nan gobe idan Allah ya Kai mu?"
"Eh...."
"Me zaku gayawa mahaifan ku ?"
'wallahi Allah maryaam batada masaniyar dukkanin abunda na gaya miki. Ni na yanke shawara ta. Saboda zuciyata ta kasa nutsuwa. Banason Allah ya kamani akan abunda ba haka bane. Na mata kazafi na nuna da yardarta itw kuma tayi biyayya ta amince. Hajiya dan Allah ki saka baki kada a daura auren nan gobe idan Allah ya kai mu"
"Tirkashi..." Hajiya tafada tana mai sauke nannauyar ajiyar zuciya. Baki daya itama kanta ya kulle. Ta cigaba da cewa
"Ai idan kukayi auren zaku daidaita kanku hashimu .. zata so ka sannu ahankali " Ta fada cikin tabbatarwa, Ko kadan bata damu da ba daidai take fadan sunan nasa ba. Hisham ne take kiran sa da hashimu
Ya girgiza kai yana hada hannuwan sa yace,
"Wallahi bazan iya auren maryam ba hajia. Na amince a hadani da koma wacece acikin zuriyar kandemi amman banda Maryam ba zan shiga hakkin ta ba."
"Ni bansan me zan fada ba hashimu. Bari a kira su gaba daya.. Duk hukuncin da suka yanke shine daidai.. Ungo dannomun lambar Nuraddeen." Ta Mika masa yar wayarta
Karba yayi ya kira mata Bappah Nuraddeen. Ta saka a kunne bugu bjyu ya dauka ta sheda masa ya tatttaro kan kowa suzo bangaren ta harda Amaal.
Ta kuma tashi ta shiga dakin mai gidan ta Alhaji Muhammad shima ta kirawo shi. Suka gaysa da Hisham ya zauna akan kujera. Hisham din na gaban su a zaune kansa akasa
Ba jimawa kuwa sai ga tuttulowar su gaaba daya. Ciki harda sarki Junaid da iyayen Hisham din. Gaba daya dai suka hallara
"Maimaita abunda kache hashimu"
"Hisham ne Hajia" Yusra ta fada tana dariya
Duk suka danyi Daria. Hisham din ya dan saci kallon mahafin sa. Muryar sa na dan rawa ya zayyane komai tun daga farko ya sake fada ya karkade da,
"Wallahi wallahi wallahi bazan iya auren maryaam ba. Idan na bari aka aura mata ni hakika na cuceta, Na ha'inceta, na zalunceta na kuma shiga hakkin ta kuma Allah ba zai bar ni ba. Tunda karya na hada na fada muku cikin tabbatarwa. Amma ita ta amince saboda ganin girman ku da tsananin biyayyar ta tace eh hakane muna soyayya. Wallahi Allah amatsayin Yaya da kanwa muke da ita tamkar na jini. Hasalima ni coaching dinta nake Ina koya mata wasu abubuwan na makaranta ta waya ko messages . Bappah, Baba, Kaka, Hajiya... Dan Allah ku gafarce ni.. ku karbi roko na kada ku aurawa Maryam ni gobe idan Allah ya kaimu wallahi kamar yadda na fadawa Hajiya yarinyar na batada masaniyar abunda nake gaya muku dai dai da rana daya batada daba mun complain na zaluntar ta da nayi ba nace muna soyayya har aka sa mana ranar aure ba, Bata taba nuna mun ba ai karya na shirya nace muna soyayya ba.. Dan Allah karku aurawa Maryam ni. Karku bata mata rayuwa ta auri wanda takewa kallon yayan ta na jini .... Ni Hisham na amince a aura mun wata daga cikin wannan zuriyar na kandemi goben idan Allah ya kai mu.. amman Dan ALLAH jar a aurawa maryam ni. A barta ta auri wani daban.. Dan Allah"
Duk sukayi shiru...Tamkar mafarki ko a kallon wasan kwaikwayo na talabijin. Alhaji Abubakhar ya mike cikin zafin nama ya tattare kasan hannun rigar sa jikake,
'Taasss.. Faaas, Chasss' Ya sharara masa maruka guda uku lafiyayyu a gefe da gefen fuskar sa.
"Mutumin banza... Daman sharri kayi mata ka cuce ta? "
Ya sake daga hannu zai sake marin sa Bappah Nuraddeen ya rike masa hannu. Sarki Junaid ma ya tashi ya janye Hisham daga wajen ya mayar da shi gefen da yake,
"Meye abun marin nasa? Haba Abubakhar? Idan ka bibiyama kila amaal dince ta nuna bata so" Cewar sarki junaid.
"Walahi daidai da minti daga maryaam bata taba nuna mun batason aurena ba. Ba kuma taba cewa ai karya nayi mata ba ba soyayya mike ba. Wallahi Allah " Hisham ya fada cikin tabbatarwa
"Yo ai ni gaba daya ma na rasa abunda zance..."Bappah Nuraddeen ya fada yana tallabe habar sa cike da damuwa
Amaal dake gefen Hajiya jamila sai raba idanuwa take. ita da tai tasan kalau fa suka rabu da shi ya rakata har kofar shiga sashen su.
Haka dai akayita maganar ana neman bakin zaren. Dakyar dai aka hakura kan ba zaa daura auren da Amaal din ba ganin yadda Hisham yake zubar da hawaye sosai kan inde aka daura to wallahi ya shiga hakkin ta kuma Allah ba zai barshi ba.
Ana cikin maganganun ne Hajia maryam tace
"Wai har yanzu dan yaye be kira waya ba an san inda yake? Tukunna ma yana Ina jama'a?"
Duk sukaita tofq albarkacin bakunan su. Yusra dake gefe tace,
"Na kira aminin sa. Habibi Talba yace Hamma Al-mustapha ya tafi Manchester England"
Bappah jalaludden ya bude baki yace,
"Ina?"
"Manchester"
Ya dubi hajia Jidda mahaifiyar su yusra yace,
"Ya gaya miki me?"
"A'ah..."
"To me yaron nan yake nufi?"
"Bappah Al-mustapha ba zai iya zama ana auren amaal ba. Shi yasa ya tafi." Aayaan ya fada cikin tabbatarwa.
"Wai yaron nan dama yana kan bakan sa?"
Hajia maryam tace,
"Ni kallon sa kawai nake... Ya bude baki yayi mata magana yaki sai zurfin ciki. Yadda yake nuna mata kamar yafu kowa tsanar ta a duniya. Bayan tun tana zanin goyo yake kaunar ta."
"Wai Al-mustapha dai namu?" Bappah junaid ya tambaya yana zare idanu,
"Shi dai...Muma rufe mana yake. A nasa haukan ba zamu gane ba. Tun muna Buckingham muka sani. Hotunan ta tun tana karama har na wanda ta girma, ko a'ina ya same su oho, yana nan dasu."
"Ammw yaron nan sakarai ne"
Ita dai Amaal jin su take tamkar a mafarki. Duk abubuwan da suke fada yana shifa ya futa ta dayan kunnen na ta. Al-mustapha kuma? Kai gaskia ba dai ita ba. A duniya ba wanda ya tsane ta sama da shi
"Ni ma na lura yana son ta sosai... Wanda ya zauna anan dinnan ko ranar da muke nan duka?" Hisham yake tambayar Aaayan.
"Shi dai. Ai mugun gara ne dab wahala. Wai shi sharukan baban soyayya ya hakura ya bar ma ka."
Sika saka dariya baki daya... Bappah Abdullahi yace,
"Kuma ba shine ba shida lafiya bane bayasan damuwa sosai?"
"Shine . Can daya Wawa. Ku rabu da shi ya karaci zaman sa acan idan yaga dama ma kar ya waiwayo gidah gaba daya" bappah jalaludden ya fada cikin halin ko in kula
"Ba za'ai haka ba Yaya.. da kai da kaya ai duk mallakar wuya me... Abunda yayi Al-mustapha shi yayi Amaal "sarki junaid ya fada
"Ba fa za'ai abundq kake tunani ba. Ni ba sakarai bane. Ba zaa shiga hakkin yarinya ba "
"Ni na amince tunda 'da na ne" sarki Junaid ya fada
"Ni kuma ban amince ba tunda 'ya ta ce" Cewar Bappah Jalaludden
Yan parlorn suka saka dariya baki daya. Bappah Nuraddeen yace
"Mutane sunzo dai ko'ina gari ya cika idan baa daura aure gobe ba da matsala. Idan Kuma akwai wata hanyar da za abi to tun yanzu a sanar musu a daren nan kan an fasa daurin aure gobe "
"Zaa daura aure inshaa Allahu .. hjsham da ne awaje na. Kuma ya roki alfarma dole zan cika masa .. wa kake so acikin zuriyar kandemi ka fada gobe da yardar Allah sai a daura muku aure kaji?"
Hisham yayi shiru can ya daga kai yana kakaro murmushi yace,
"Duk wadda aka bani Bappa "