← Book details Auren Bare Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 69 OF 115

Sashe 69

Auren Bare Part 1 Complete Hausa Novel · about 9 min read

Aliyu ya jima yana tunanin mafita akan wannan cakuɗaɗɗan lamarin daya kunno mishi ɗago ƙwayar idanunshi yay ya zubasu akan agogon bangon dake manne a bangon ɗakin nashi ganin kusan 12 na dare yasashi miƙewa a center ɗakin ya tsaya tare da tube jallabiyar jikinshi ya rage dagashi se singlet tare da wandon jeans ɗin daya saka daga cikin jallabiyar.
Shafo kwantacciyar sumar dake saman kirjinshi yay tare da shafo shafaffan cikinshi wanda yay wani irin shafewa tamkar ba,a saka masa lomar abinci.
Yana kokarin nufar ƙofar bathroom ɗinshi yaji alamun ana murɗa handle ɗin kofar room ɗin nashi cakk ya tsaya tare da ɗora hannunshi bisa kirjinshi ya zubawa kofar idanu, Cikin siririyar muryarta wadda ta karo mata yanga da gwalli take rangaɗa sallama cikin ɗakin.
Can cikin makoshin sa yake amsa sallamar amman ƙasan ranshi mamaki ne fall.
Bayyanarta cikin ɗakin shiyafi basa mamaki musamman yadda tai shigar jikinta mai tsananin fisgar hankali da tunanin mutum mai lafiya, Gabanshi ta tsaya tana rau-rau da ƙwayar idanunta kamar wadda zatayi kuka kafin cikin shagwaɓa ta soma magana.
"Yaya sannu da zuwa dan Allah a ina ka tsaya yau?"
Haɗe ranshi yay tare daɗan jan tsuka kaɗan ya raɓeta ya wuce cikin bathroom tare da bugo kofa yanajin takaicin wannan shige masan datakeyi.
A maimakon ta fita seta gyara zama tana kara zame yar rigar dake jikinta ta bacci wadda batada maraba da fanÉ—arinka tsirara wadda ta baiwa Æ´an matasan kirjinta bayyana fili, ya kusan minti talatin a bayin kafin ya fito jikinshi É—aure da tawul yana É—igar da ruwa sam bai yi xaton tana É—akinba shi mutum ne mai alkunya baya kaunar bayyana tsiraicinshi agaban kowa wannan halinshine tun yana yaro domin ammi ko wanka zata masa sedai ta saka masa É—an wando inba hakaba kuwa yayita kuka kenan yana angane masa abinshi, Cikin hargagi kaÉ—an ya daka mata tsawa tare da bata umarnin ta fitar mai aÉ—aki.
Jiki babu laka taja kafafunta tabar É—akin tana haÉ—iyar miyau domin surar jikinshi bakaramin nutsar da ita tayi ba a kogin sha'awar shi.
Gaban kofar yaje ya zira mata key ya dawo gaban gado ya zauna ya dafe kanshi sam a halin yanzu bayada feeling bare ya samu damar yin sex sabida halin dayake ciki na wannan tension ɗin da usman ya sakashi yasan bai yiwa dija adalciba domin a yanzu tanada hakki akanshi bayaga nan kuma baisan irin nata karfin sha'awarba sedai kuma a yadda yake koda tsirara zata mai tofa baze taɓa jin komaiba sabida in rai na ɓace feeling gudawa yake.
Ganin dare yana kuma ja yasaka ya nufi gaban jerin kayanshi ya ɗauki jallabiya milk colour tare da ɗan guntun wando ya zira ya kuma komawa cikin toilet ya ɗauro alwala ya shinfiɗa darduma, yahau ya soma gabatar da sallolin nafila wadda a dukkan sujjadar ƙarshe seya jinkirta yana kaiwa ALLAH kukanshi akan wannan abun daya faɗo masa sama taka yana kuma jaddada neman zaɓin alkairin ALLAH acikin wannan lamari tare dayiwa ubangiji kirari da sunayensa kyawawa.
Har kusan karfe ukun dare yana saman sallaya bayan ya idar ya soma lazimun la'ilaha'illah'anta'subuhanaka'inni'kuntu'minazzalimin'!akan ALLAH ya fitar dashi daga cikin wannan matsala sabida wannan addu'a ta inganta ga bayi musamman waÉ—anda suke cikin damuwa in suna karantawa bazasu gusheba face ALLAH ya kawo musu mafita acikin dukkan matsalolinsu kuma ya fitar dasu daga cikinta.
Bayan ya kammala yay istigifari da hailala tare da salatin annabi s.a.w sannan ya shafa ya naÉ—e abin sallan ya koma saman gado ya kwanta akan hannunshi na dama bayan ya tofa addu'oinshi na kwanciya daya saba gabatarwa.
Babu jimawa bacci mai daÉ—i ya saceshi kuma babu laifi yaji kaso mafi yawa nadaga cikin damuwarshi ya fita yaji sakayau aranshi.
Wanda har yakusan makara a sallar asubahi inda Allah ya soshi yanada agogon dake buga alarm wanda seda ya buga wajan sau uku sannan ya buɗe idanunshi waɗanda suka cika da bacci yana karanto addu'ar tashi daga bacci sannan ya miƙe ya nufi toilet seda ya watsa ruwa a jikinshi sannan ya ɗaura alwala ya fito agurguje ya sake sauya kaya wannan karon brown ɗin jallabiya ya saka tare da fesa turare mai kamshi wanda indai ze fita sallar asubahi yake amfani dashi.
Cikin sauri ya kashe ƙwan ɗakin ya fita a falo ya dakata yaɗan leƙa ɗakin dija ya buga mata seda yaji alamun tashinta sannan ya wuce masallacin cikin sauri.
Yana zuwa ana ƙoƙarin tada jam'i wanda yau alhaji babbane ma yake jan limancin sahu yabi aka tayar da sallar har aka idar bayan an sallame yaja baya tare da soma laziminshi wanda yawanci daman inya fita sallar asubahi baya komawa bacci harse ya kammala lazuminshi tare da azkar yay walha in yanada office ya fita in yana gida yaje ya kwanta abinshi, se wajan bakwai saura ya kammala sannan ya fito aikuwa harabar gidan babu kowa sabida safiyace hatta securties ɗin gidan suna can ɗakunansu sabida yadda aka tashi da yanayin sanyi.
Harya yakai kofar part É—in mahaifanshi maganar mama ta faÉ—o mishi aranshi.
"Ka kulamin da bebi ina sonta marainiyace ga amanar Æ´ata na baka karka cutarmin da ita"!.
Cak ya dakata yana sosa saman kanshi abin duniya ya haÉ—u yay mashi yawa.
Umarnin zuciyarshi yabi kai tsaye ya karya kwana ya fasa nufar sashen iyayenshi seyay na usman, abakin gate É—in ya tsaya yana wasi wasi kafin yay ta maza ya tura ya shiga ciki, seda ya danna knowking kusan sau uku kafin azo a buÉ—e mishi usman ne ya buÉ—e kofar tare daÉ—an bawa Aliyu hanya ya wuce cikin falon tsananin mamaki ya kama usman ba É—an kaÉ—an ba domin sam baiyi tunanin ganinshi a wannan lokacin ba.
Gaisawa sukai ta hanyar musabaha yana xama akan ɗaya daga cikin kujerun falon, tunda usman yay aure yaune zuwanshi na biyu ɓangaren usman ɗin.
"Ina wannan yarinyar take?"
Ya faÉ—a yana kallon usman wanda yake kokarin xama shima a kan kujerar dake fuskantar ta Aliyun.
"Tana É—akin dana sa aka kaita tun jiya bana zaton kota tashima amman kaje ka dubata man kaida matarka ga É—akin can".
Usman ya faÉ—a yana mikewa ya nufi É—akinshi yabar Aliyun a dashe a falon.
Miƙewa yayi tare dabin direction ɗin da usman yay mashi gaban kofar ɗakin data kwana yaje ya tsaya yana turawa ya buɗe ɗakin alamun bata saka key ba.
Sallama yayi a ƙasan bakinshi shuru yaji laluba makunnin ƙwan ɗakin yayi tare da kunnawa ya tsaya yana kallonta a kwance a kasan tiles tana baccinta masha Allah.
Tsira mata manyan idanunshi yay yana kallonta kafin ya ƙarasa gabanta ya tsugunna yana kiran sunanta.
"Ke!ke!! ke!!"
amman shuru kamar bata raye, jan ɗan yatsanta yayi guda na ƙafa wanda har wani tarar jini yay sabida janshi, wata irin birgima tayi tare da miƙa ta hantsila saman kafafunshi ta saka hannunta guda a ƙugunshi tacigaba da baccinta.
Wata iriyar ɓoyayyar kasalace ta rufe masa jikinshi wadda baitaɓa jin kamancin irinta ba.
Zama yayi daɓas a saman tiles ɗin tare da saka hannunshi guda ya ƙara jawota jikinshi sosai ya bata masauki mai kyau, yana mai tsira mata idanunshi yaga alamun sam bata ƙoshi da baccin ba kuma aranshi baya son tashinta sedai kuma dole ta tashi ɗin tunda sallah tana kanta.
Lalubar cikin kunnenta yay tare da buÉ—ewa yaÉ—an ja hijabin cikin kunnen nata ya tura harshensa yana É—an hura mata iskar dake cikin bakinshi kaÉ—an batare daya furta komaiba se iya wannan sakon dayake aika mata dashi.
Jin sauyin kamshi acikin kunnenta yasa ta soma buɗe idanunta tana kuma jin saukar iska cikin kunnenta, zumbur ta miƙe jinta asaman cinyar mutum kafin ta buɗe idanunta tarwai tana kallon ɗakin.
Zare bakinshi yay a kunnenta yaÉ—an tureta kaÉ—an yana kallonta fuska É—aure.
"Tashi kije kiyo alwala oya banson jira".
Jin tattausar muryarshi cikin dodon kunnenta ya bata tabbacin masifaffe yazo kenan.
Bata tsaya tunani akan lamarin komaiba ta mike jikinta yana rawa tabar saman cinyar tashi tana maibin umarninshi sabida sanin halin faÉ—anshi bakaramin kokari tayiba kafin ta iya haÉ—a ruwa tai tsarki tayo alwala ta fito.
Darduma ta tarar ya shinfiÉ—a mata shikuma yana zaune a gefen gado ya zuba tagumi yana kallon kofar bayin.
Harta hau saman dardumar bai É—auke idanunshi akanta ba, haka ta tayar da sallar cikin nutsuwa ta idar tana addu'a ta shafa.
Sannan ta juyo gareshi.
"Barka da safiya".
TafaÉ—a tana yin kasa da kanta.
Bai amsa mata ba illah tashi tsaye dayay.
"Muje ciki amman bakida kayan dazaki sauya?".
Yafaɗa yana kallon yadda take ƙunshe jiki acikin hijabin daya ɗan soma datti sabida farine.
Girgiza kanta tai tare da yin ƙasa dashi alamun batada.
"Bana son magana daka malama kimin magana yadda nai miki".
"Eh babu anan suna motar uncle usman".
TafaÉ—a cikin rawar murya domin itafa a tsorace take dan wallahi inda zata sami hanya sedai aga wayam tayi wajan mama.
"Okey muje ko".
YafaÉ—a yana ratseta ya wuce.
Amaimakon ta bishi seta tsaya tana kallon kanta ke yanzu bebi ahaka zaki bishi dubeki kamar ba Æ´ar mama ba kaca kaca dake ko bra babu ajikinki.
Harya kai falo yaga bata biyoshi ba a zuciye ya koma É—akin.
"Malama waini akanki xan ƙare dalla fito mu wuce wajan ammi".
Rau-rau tai mar da idanu zatayi masa kuka!.
"Nidai Allah bazan fita ahaka ba jiba fa kamar wata bakauya ka É—aukomin kayana a wannan motar ta jiya"
Tsayawa yay yana kallonta kamar wani dolo yana hango tsabar kuruciya a tare da ita.
Tsaki yaɗanja sannan ya fita a ɗakin da ƙyar ya sami mai gadi ya bashi makullin motar yaje ya ɗauko mata jakar kayan nata wanda shi badan wani abu yake yin haka ba kawai baison ta ɓata masa lokacinshine.
Har lokacin falon babu kowa da alamun usman yana can suna baccinsune harara ya ɓalɓawa wajan ɗakin usman yana ayyana ɗan iska kai kana can hankali kwance ni kabarni da raino.
Kofar É—akin ya tura ya shiga tan nan yadda ya barta a tsaye.
Aje mata jakar yay agabanta tare da zaman jiranta a gefen gado.
Amai makon ta É—auki kayan taje bayi ta kintsa ai ina bebi akwai hauka seta tsugunna gaban jakar seda taiwa komai filla filla babu bra ko É—aya bare kuma pant wanda tasan mantuwa mama tayi.
doguwar rigar atamfa ja ta É—auka sannan ta É—auki zani falle guda ta nufi gaban madubin É—akin tube hijabin jikinta tayi sannan ta É—aga rigar jikinta ta É—aura wannan zanin na hannunta.
Duk abinda take yana kallonta sedai ya zuba mata idanu ne kawai yana kallon kalar nata shirmen yarinyar yaga alama batada kunyar tsiraici agaban uban kowa aikwa da matsala.
Juyowa tayi ganin idanunshi akanta yasa gabanta ya faÉ—i.
Tasan babu kyau mace ta bayyana jikinta agaban namiji amman ai wannan mijinta ne kuma mama tace mata dan miji yaga jikinka ba haram bane ba.
Gabanshi tazo ta tsaya.
"Zaka zugemin ziff É—ina sannan kuma mama bata sakomin bra ba kuma bani da pant".
Tsira mata idanu yay kurum yana ayyana Aliyu kaga ta kanka.
Batare daya ce mata komaiba ya mike ya karbi rigar hannunta.
Ya xage mata ziff É—in sannan ya mika mata ta amsa agabanshi ta É—aga hannu ta zira rigar sannan ta juyo masa farin bayanta tass tana cewa ya zage mata ziff É—in se asannan ya fahimci abinda take nufi.
ÆŠora hannunshi yay saman bayanta ya zuge mata ziff É—in garin sauri har yana haÉ—awa da fatar wajan wadda ta sakata saurin zabura ta daka tsalle da ihun zafi ta rungumeshi.
Dan itafa tafa manta da wanda take tare sabida zafin dataji.
Murza kanta take a saman kirjinshi tana furta.
"Dafa zafi kaimin wallahi bazan yarda ba Allah kuwan........tanayi tana kukan data jima tanayi na kewar mamanta.
Wayyo bebi kin kashe Aliyu wani irin yanayi yakejin kansa aciki mai wuyar misaltuwa................
Chapter 69 · 0% Book details