← Book details Auren Bare Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 19 OF 115

Sashe 19

Auren Bare Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

_BAYAN KAMMALA TARO_
Zaune yake cikin offishinsa, asaman kujera irin wadda take kaÉ—a mutum tana juyashi batare dayay tsammani ba.Kiran masijanshi yayi tare da bashi umarni akan yaje yazo mashi da Salihu( baban nazir ) cikin mutuna biyar masinjan nashi ya shigo bayanshi baban nazir ne wanda wannan kiran na oga usman ya firgitashi addu,a yake kada Allah yasa oga usman yace.
Su hassana su daina kawo abinci kamfanin, sabida yaran suna bashi matukar tausayi ba É—an kaÉ—anba, sannan kuma su kansu sunajin daÉ—in taimakon abinci ko banxa ka huta shan lemo da burodi.
"Haba kaiko kamar ba namiji ba, daga aikawa kazo kazomin kana muzurai nanfa ba office É—in dodonku bane".
Muryar usman ta sauka cikin dodon kunnen baban nazir wanda tun zuwanshi daya rissuna yake faman tunani shi É—aya bai kuma É—agoba seda yaji muryar usman É—in data katse mishi tunaninshi.
Sosa kanshi yay kaÉ—an tare da kallon oga usman É—in tare da cewa.
"Ai oga bansaba jin kana kirana haka kurum bane harga Allah naji wani abu acikin zuciyata har ina addu,a Allah yasa ba dakatar da yarancan zakai ba".
YafaÉ—a kanshi tsaye sabida duk tunaninshi ya riga ya tafi akan hakanne.
Da hannu usman ya sallami masinjanshi dake tsaye awurin batare daya juya ba.
Sannan ya gyara muryanshi tare da kallon baban nazir.
"Malam salihu idan babu damuwa ina bukatar daka zauna akan É—aya daga cikin waÉ—annan kujerun mana".
YafaÉ—a tare da zube dukkan hannayenshi asaman teburin gabanshi yana kallon baban nazir da tausayawa.
Cikin sauri baban nazir ya miƙe tare da komawa saman emty chair ɗin dake cikin office ɗin wadda ta kasance ta silver, sannan ya mayar da hankalinshi kan oga usman ɗin.
Gyaran murya oga usman yayi tare da kallon baban nazir.
"Ai malam salihu ina zaton kai da kanka zakaje kana bada labarin halinmu kaf! bama ni kaɗai ba wallahi ko Aliyu da kuke ganinshi haka bani zaton ze iya wulaƙanta ɗan adam bare kumani, saboda me?, dukkaninmu bamusan me rayuwar zata kaimu gaba ba.to dan haka ina son ka cire kokonton wani abu daban acikin ranka wallahi ka ɗauka kamar nan ɗin kaima wajanka ne, sabida haka ina musu fatan nasara acikin sana'arsu ni babu ruwana da wani danyazo yaci arzikinmu nai masa ido ko bakin ciki,
Sabida haka ni ba wannan tasa na kiraka ba, daman tambayar ka zanyi idan babu damuwa.
Kasan madam É—ita se ahankali kwana biyu bata cika lafiyaba wallahi kullum problem É—ina abinda zamuci, na break na lunch dinner, kuma kaga dai rayuwar yadda take kuma kasan mata nan idan sunada juna biyu se addu,a shine nace idan babu damuwa kozaka tambayamin mamar yaran nan akan tabani guda É—aya inje gida da ita sabida ayyukan gidana da girki?".
Zubafe ta ketowa baban nazir wannan shine ga ƙoshi ga kwanan yunwa yasan ko ana yaki bayajin maman ƴan biyu zata bada yaranta aikatau sabida tunba yauba ake wannan mujadalar amman tace ita bata yardaba tafison ko tsakuwa a misali zataci tofa taci tare da yaranta.
"Ban musa makaba oga amman gaskiya mahaifiyarsu ce batada ra'ayin hakan amman zan tambayeta ko Allah zesaka ta yarda".
Cewar baban nazir wanda kawai yafaÉ—i hakane amman yasan hakan bamai yuwuwa bace.
Cikin ilimi tare da nazari usman yagama fahimtar baban nazir shi daman bawai matsuwa yay sosaiba tunda akwai masu aikin sedai kawai yadda yaga tsarin yaran da tsaftarsu yakeson ya daukesu ko girkine kodan ya sami kafar taimaka masu amman tunda abin bazai yuwuba kawai ze hakura.
"No Salihu karka matsa kanka amman pls dan Allah inason ka tabbatar min da tsaftarsu kawai sena dinga order dambun ma kawai is ok domin madam tana son dambun sosai".
Dariya baban nazir yay.
"Tabb oga ai wallahi ko madam baxata nunawa maman biyu tsaftaba amman kaima zaka tantance ko yadda kaga yaran da yadda komai nasu yake a tsaftace".
YafaÉ—a yana dariya shima usman É—in dariya kurum yay yana cewa"watakan dannafi yadda yasa ka haÉ—a harda madam É—ita lallai malam salihu ka rainani da yawa" yafaÉ—a yana kiran masijanshi.
Wata babbar kula wadda yake zuwa da abinci cikinta ya baiwa masinja sabida daman kwana biyu ba,a zuba komai cikinta sedai ai masa take away a waje,"Je wajan yarancan su bani dambu" yafaÉ—a wa masinja tare da buÉ—e locar ya fiddo sabbin kuÉ—i ya bashi"Kada ka tsaya amsar canji kaji kavar masu duka kace inji yayansu" yafaÉ—a yana dariya"Malam salihu ka iya tafiya kawai, bama seka je ka gaya mataba barshi na dinga siya kasanmu Æ´aÆ´an ammi Allah ya É—oro mana san dambu kaf É—inmu" yafaÉ—a yana fiddo wayarshi daga aljihun wandonshi sallama baban nazir ya mishi ya fita.shiko madam ya kira ya sanar mata maganar dambu aikuwa abinka da mai ciki tahau murna nan da nan tace zata aiko driver ya bata kasonta.

_DAGA WAJANSU HASSANA_
Lokacin da masinjan usman ya kai musu flaks É—in sosai sukai mamaki ganin dalla dallan kuÉ—in daya zaro ya miko musu tsorata..........

*MATA DA MAZA ƳAN KASUWAR DAKESON NA TALLATA MUSU HAJARSU A SAMAN SHAFUKAN LITTAFINA CIKIN FARASHI MAI SAUKI ZASU IYA NEMA NA TA NAN 08142105218*

*MASU SON LITTATTAFAINA DANA KAMMALA KAMARSU*

*ÆŠAN MAJALISSA*
*HASKE*
*KOBA SO*
*RABON WANI*
*DA IZZATA*

*DUKKANSU AKAN FARASHIN NAIRA DUBU ÆŠAYA,1000 IDAN KUMA ÆŠAI ÆŠAI KIKE BUKATA 300 DOCUMENT A HADE SE KARATU ZAKI TUNTUBEN ANAN 08142105218 DOMIN KI BIYA KI MORE KARATU*
11/14/21, 3:06 PM - Allah Akbar: *AUREN BARE !!*🌹
{ _HOT LOVE_ }

NA
*AUTAR MANYA*

_HOME OF QAULITIES WRT ASS..._

*23&24*

Cikin mamaki mai ɗauke da tsoro hassana ta dubi masinjan ayayin dayake Miƙo musu kuɗin hannunshi tare da cewa,"Gashi inji oga usman yace ku zuba masa dambun, amman kada a saka yaji".Karɓar flaks ɗin hassanar tayi ta soma zuba masa harse da ta cikashi damƙam har baki sannan ta rufe, kuɗin ta amsa a hannunshi ta ƙirga iya wanda tasan yakai adadin na dambun ne sannan ta mikawa masinjan ragowar canjin, wanda shi harya soma tafiya tai saurin binshi, sakato yayi tare da cewa"Ai yace kada na karɓi ragowar na baku duka", ɗan jim kaɗan tayi tare da kallonshi"A,a dan Allah kace masa yabarshi sabida mamammu zata mana faɗa idan taga kuɗin ya haura".tafaɗa tana miƙa masa kuɗin kana ta koma wajan sana'arsu, miƙawa hussaina kuɗin tayi tana mata bayani, zaro idanu hussaina tayi tare da cewa,"Lallai wannan mutumin yau soyake mama tai yanka yanka damu kenan",dariya sukai atare "Aidaman shiyasa nayi saurin dakatar dashi tun wuri" cewar hassana wadda ta mike zuwa wajan zubawa wani alala.
Shiko masinjan usman yana komwa office ya tarar da ogan nashi yana amsa waya, dakatawa yayi harya kammala sannan ya rissuna ya mika mishi tare da cewa...........
"Oga wallahi fafur sunƙi karɓar kuɗin wai mamansu zata musu faɗa idan taga kuɗin ya haura, wallahi oga babu yadda banyi dasu ba, amman sunƙi amsa".
Yakai maganar yana rissunar da kanshi a ƙasa.
Ƴar dariya kaɗan usman ya sauke tare da jinjina wannan lamarin.
Daman ana samun yara masu tarbiyar nan har yanzu? tabbas duk lalacewar zamani ba'a taɓa haɗuwa a zama ɗaya dole akwai nagari sannan kuma akwai ɓata gari.
Sau tari wasu yaran tsananin babu takansa su sallama kansu wa mazan banza domin su sami abinda zasu ci, wasu kuwa tsabar kwaÉ—ayine ke rufe musu idanu, harsu faÉ—a halaka, wasu kuwa laifin iyayen sune.
Amman su waÉ—annan yaran kana kallonsu, dai kasan bamasu wadata bane, amman daga gani sunada tarbiya sannan kuma mahaifiyarsu a tsaye take domin ganin ta basu tallafi ta ko'ina.
"Oga ga dambun fa".
Yaji muryar masinjan a saman dodon kunnenshi.
ÆŠagowa yayi fuskarshi É—auke da murmushi kamar koda yaushe sannan ya dubi masinjan nashi.
"Ok ka ajemin saman frij nagode kaje da ragowar canjin kasayi wani abun".
Cikin rawar jiki masinjan ya dubi usman tare da rissunawa sosai gabanshi.
"Kai oga bansan dame zan maka godiya ba, amman ina roƙon Allah daya saka maka da mafificin alkairinshi amin nagode ƙwarai".
DaÉ—ine ya kama usman na wannan godiya murmushi ya saki tare da É—agawa masinjan hannu batare daya ce mashi komiba.
Aikin dake gabanshi ya cigaba dayi batare daya kumabi takan zancen Æ´an biyuba, amman yana ji aranshi tabbas ze duba lamarin yaran yanajin ze tallafesu da wani abun.
Ya jima a office É—inshi yana aiki har aka kira sallah, bai samu fita masjid ba amman yayi acikin office É—inshi sannan ya É—auki flate ya zubo dambun da masinjanshi ya aje masa shi bisa frij,
Tun kafin ma ya kai lomar cikin bakinshi yaji wani sihirtaccen kamshi mai É—aukar hankali ya shiga cikin hancinshi.
Wani irin ƙamshin attaruhune tare dasu albasa, ga gyaɗa tabi lafiyar saman dambun ga wadataccen zogale malam, tuni usman ya soma haɗiyar miyau jikinshi yana mazari, ya koma saman raising chair, ya zauna kana ya ɗora ƙafafunshi ɗaya kan ɗaya, ya fara da bisimillah a cikin bakinshi sannan ya ɗauko spoon ya soma ɗibar dambun.
Wayyooo! tuni usman ya soma mazari kunnenshi ya soma rawa at list usman seda yay flate biyu na dambun da ƙyar madam ɗinshi ma ta samu ɗan kaɗan wai hakan ma sabida darajar cikin jikinta ne yasaka ya rage mata shi,Sosai yaji daɗin dambun seyace idan ba ammi ba babu wadda takai wannan matar iya dambu,ruwa ya buɗe yasha tare da hamdala ga sarki Allah kana ya koma gaban aikinshi yana ayyana yadda ze ringa bada kuɗin nashi na mussaman sabida matukar daɗin da dambun yayi mashi.

Wajan karfe ukun rana Allah ya taimaki su hassana dambun nasu ya ƙare tas! har ana nema shima alalen babu laifi ya kare yau ɗin sedai baikai dambun kasuwaba.
Na baban nazir dasuke ware mashi hassana ta É—auko tana kallon hussaina"Tomu yanzu yaya zamuyi da dambun baban nazir kinga har mun tashifa bai zoba", cikin kulawa hussaina ta dubeta tare da cewa"Ki bawa mai gadi idan ya fito seya bashi kawai" wannan shawarar ta karba haka ta kaiwa mai gadi dambun baban nazir sannan ta koma wajan Æ´ar uwarta suka haÉ—a kayansu, aka suka É—ora kulolin har zuwa bakin gate yau sun É—anyi jinkirin samun abin hawa, kafin kuma Allah ya basu iko wani yazo sukai ciniki suka hau suka wuce gida.
Chapter 19 · 0% Book details