Sashe 67
Auren Bare Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Jin tattausan hannunshi mai azababban ƙamshi datayi a saman bakinta shiya kuma ƙarawa jikinta rawa da kyarma akan wanda yake tun fitowarta.
Kafin taji dirin tsaiwarshi a bayanta hannunshi guda ɗaya ya saka ya riƙo tsakiyar ƙugunta irin riƙon nan na tsauri tare da jiyo da ita saitinshi tana fuskantarshi.
Wata azababbiyar faÉ—uwar gaba mai cike da firgici zulumi tsoro sune sukai mata dirar mikiya fiye dana da, Rintse idanunta tayi tana addu'a cikin ranta inda xaka kula lokacin zakaga kirjinta yana tsalle kamar ze faso ya fito waje sabida tsabar kaÉ—uwar datayi
Kallonta yake sosai ta cikin hasken farin watan daya haska tsakar gidan, batare daya É—auke idanunshi daga kanta ba.
Yace mata.
"zomu wuce".
Still hannunshi na riƙe da ƙugun nata, yana cigaba da kallonta se yanzu yake ƙara ganin ƙarancin shekarunta sosai.
Zumɓuro bakinta tayi gaba kamar yadda ta saba yima mama shagwaɓa duk da yadda takejin tsoronshi amman bai hanata turo bakin gaba ba, tana dira ƙafafunta ƙasa.
"Ni bazan bika ba dan Allah ka barni da mamammu".
Shiiiiiiiiiiiiii yace mata da bakinshi tare da jan hannunta da ƙarfi ya fitar da ita har zuwa soro.
Abakin ƙofar waje ta kuma takurewa tare da tsayawa waje ɗaya alamun bazata bishi ba.
"Karki ɓatamin lokaci wallahi in baki shige mun tafiba ranki ze ɓaci,Wayace ki zaɓi aurena shasha sha kawai".
Hawayene ya zubo mata cike da tsoro ta bi bayanshi tana ayyana shikenan tayi bankwana da gidansu tayi bankwana da mamanta da Æ´an biyunta, abakin kofar gida ta kifa kanta tana cigaba da kukan datake yi.
Ganin yayi tafiyarshi ya barta a wajan yasa tabi bayanshi salo salo kamar wadda ƙwai ya fashewa acikinta,tana ayyana Allah sarki sadiya ko sallama basuyi ba.
Lokacin data ƙarasa gaban mota usman yana wajan driver yama tada motar su kawai yake jira, azuciye Aliyu ya buɗe motar ya shige yabarta awajan cikin sakin fuska usman ya leƙo da kanshi.
"Ƙanwata buɗe gidan baya mu wuce kinji daina kuka zan ɗauko mama na kawo maki ita har gida".
Cike da sauri ta balle marufin ta shiga tana gyara hijabinta, domin batada zaɓin daya wuce haka sabida tariga tasan ƙaddarar aurenta ce tazo mata da hakan, duk da karancin shekarunta amman tasan kaddara kuma tana yarda da ita sabida gwajin imanin bayi ce.
Cikin nutsuwa yay revars tare da jan motar ya fita daga cikin layin da ita,lokacin gari yay tsit sabida taran darema ta wuce gakuma walƙiya da akeyi sosai iska mai ƙura tana kaɗawa alamun hadarin garin gab yake da zubar da ruwa, kasancewar garin yanayin damuna ne.
Tafiyar mintuna goma daga layinsu bebi zuwa kan titi usman yay, lokacin da motar xata bar layin seda bebi tai kuka harda shashsheƙa,tana jin missing ɗin anguwarsu har wajan gawayin shahid ta kalla tana share hawayenta.
"Yanzu kai abinda kaimin tsakanin ka da girman ALLAH kayimin adalci kenan?".
Aliyu ya faɗa cikin ƙasa da murya wadd ta shaƙe kamar zeyi kuka!.
Cikin sauri usman ya kunna redion motar sabida bayason Bebi taji abinda zasu faÉ—i.
Ware redion yay da ƙarfi yana tukinshi batare daya tankawa Aliyun ba.
"Adalcin kenan kuma bana shakka sabida alkairi na ƙulla ba sharri ba, sannan kuma da sannu zakazo min da buhun godiya nan bada jimawa ba".
Cikin ƙufula ya kuma duban usman a karo na biyu.
"Daman haka zakace man, sabida kai kasan baka cikin case tayaya zan dubi abba nace masa nayi aure bai sani ba? tayaya zan fuskanci ammi, dan Allah kai akaran kanka kayimin adalci kenan kariga ka sakani acikin sarƙa wadda batada mabuɗi".
Dariya usman yay har yana dukan sitiyarin motar shi sannan ya kalli Aliyu wanda yake faman sababi yana jin ransa yakai ƙololuwar ƙarshe a ɓaci sannan yace.
"Karka damu mai afkuwa ta riga ta afku sedai muyi maku fatan addu'a ALLAH ya kawo ƙazantar ɗaki, haba ƙanina ka tambayeni shawara tare da hanyar warwareta nikuma naga wannan auren shi kaɗaine masalaha sabida ceton maraici kagafa in suka mata auren nan sun cuceta kuma kanada kamasho tunda kaine sila, Yanxu ko daka aureta ai magana ta ƙare, nina san abba yasan ciwon haihuwa baze taɓa cewa ka rabu da ita ba koda yay faɗan ma na lokacine amman ze huce, amman duk da haka yanzu zamu soma kaita wajan ammi semuji mizata ce".
Tunma kafin usman ya idda numfashinsa Aliyu ya kuma cafke maganar usman cikin hargagi da masifar dake ranshi wadda yake dannewa.
"Miya ruwanka dani, danna zo maka da shawara ina ruwanka da haɗani aure da ita ina ruwanka da shiga hurumina wallahi nai dana sanin gaya maka halin danake ciki kuma wallahi bada ban ƙimar wancan dattijon ba wallahi dase na saketa sedai kai ka aureta".
Ta inda yake shiga bata nan yake fitaba baƙaramin tsoro hakan ya bawa usman ba baitaɓa tunanin ƙanin nashi nada faɗa irin hakaba har suka ƙarasa gida yana masifa kamar ze ari baki.
Harda cewa usman ya cuce shi yaje ya auro masa ƴar cikinshi ko uban me ze ɗauka ajikinta oho yarinyar da ko wankan tsarki ƙilanma bata iya ba masifa tijara babu irin wadda baiyi a motarnan ba wanda har tsoro seda ya tsirgawa usman.
Inda Allah ma ya taimaka sun kunna redio yana da tabbacin bebin bazataji maganar dasuke ba ammn yasan inda taji abinda ALIN ke faÉ—a seta fishi shiga halin tsorata da zulumi.
Bai bar usman ya ƙarasa parking ba ya ɓalle marufin motar ya fice azuciye.
Cikin rawar jiki shima usman É—in ya balle nasa side É—in yabishi seda usman ya haÉ—a da gudu sabida Aliyu badai sauriba, yana ayyana yau na É—ebo ruwan dafa kaina
Hannu ya saka ya janyo kafaɗun Aliyu wanda harya kusan kaiwa ƙofar part ɗinshi.
Yadda kalar idanunshi suka sauya launin kala yay matuƙar razana usman sabida sunyi wani irin girma tare da ja kamar gauta wanda ko ba,a faɗa maka ba kasan yana cikin tsananin damuwa da fushi.
Sanin kanshine in Aliyu na cikin fushi ko ammi bata kulashi harse ya sauka, dan haka cikin sanyin jiki usman ya saki kafaÉ—un sa tare da komawa wajan motar ya rabu dashi har zuwa gobe.
Tsaki yaja da ƙarfi tare da banko gate ɗinshi ya shige batare dako ya juya wajan usman ɗin ba.
Yana son ko a iya wannan daren ne ya nunawa usman kuskurenshi na wannan shiga hanci da ƙudundunen daya masa wanda baƙaramin haushi usman ɗin ya bashi ba.
Haka ya ƙarasa cikin part ɗinshi azuciye kota kan ɗakin dija bai biba ya haura ɗakinshi ya faɗa saman gadonshi yana dafe kanshi dake barazanar tarwatse mashi bai shirya haɗa maganar daze fuskanci ammi ba, yana son dogon tunani da nazari kafin ya ƙaddamar da komai, zumbur ya miƙe zuwa gaban frij ɗin dake manne cikin ɗakin nashi budewa yay tare da ɗaukar gorar ruwan faro mai sanyi ya kafa a makoshinsa wanda ya bushe ƙaraf babu ko alamun miyau acikinshi seda ya shanye tass ya wurgar da gorar ya kuma ɗaukar wata ya shanye tass sannan ya mike yana rangaji kamar ɗan maye ya kuma faɗawa gadonshi ya shiga duniyar tunanin mafita?
Kafin taji dirin tsaiwarshi a bayanta hannunshi guda ɗaya ya saka ya riƙo tsakiyar ƙugunta irin riƙon nan na tsauri tare da jiyo da ita saitinshi tana fuskantarshi.
Wata azababbiyar faÉ—uwar gaba mai cike da firgici zulumi tsoro sune sukai mata dirar mikiya fiye dana da, Rintse idanunta tayi tana addu'a cikin ranta inda xaka kula lokacin zakaga kirjinta yana tsalle kamar ze faso ya fito waje sabida tsabar kaÉ—uwar datayi
Kallonta yake sosai ta cikin hasken farin watan daya haska tsakar gidan, batare daya É—auke idanunshi daga kanta ba.
Yace mata.
"zomu wuce".
Still hannunshi na riƙe da ƙugun nata, yana cigaba da kallonta se yanzu yake ƙara ganin ƙarancin shekarunta sosai.
Zumɓuro bakinta tayi gaba kamar yadda ta saba yima mama shagwaɓa duk da yadda takejin tsoronshi amman bai hanata turo bakin gaba ba, tana dira ƙafafunta ƙasa.
"Ni bazan bika ba dan Allah ka barni da mamammu".
Shiiiiiiiiiiiiii yace mata da bakinshi tare da jan hannunta da ƙarfi ya fitar da ita har zuwa soro.
Abakin ƙofar waje ta kuma takurewa tare da tsayawa waje ɗaya alamun bazata bishi ba.
"Karki ɓatamin lokaci wallahi in baki shige mun tafiba ranki ze ɓaci,Wayace ki zaɓi aurena shasha sha kawai".
Hawayene ya zubo mata cike da tsoro ta bi bayanshi tana ayyana shikenan tayi bankwana da gidansu tayi bankwana da mamanta da Æ´an biyunta, abakin kofar gida ta kifa kanta tana cigaba da kukan datake yi.
Ganin yayi tafiyarshi ya barta a wajan yasa tabi bayanshi salo salo kamar wadda ƙwai ya fashewa acikinta,tana ayyana Allah sarki sadiya ko sallama basuyi ba.
Lokacin data ƙarasa gaban mota usman yana wajan driver yama tada motar su kawai yake jira, azuciye Aliyu ya buɗe motar ya shige yabarta awajan cikin sakin fuska usman ya leƙo da kanshi.
"Ƙanwata buɗe gidan baya mu wuce kinji daina kuka zan ɗauko mama na kawo maki ita har gida".
Cike da sauri ta balle marufin ta shiga tana gyara hijabinta, domin batada zaɓin daya wuce haka sabida tariga tasan ƙaddarar aurenta ce tazo mata da hakan, duk da karancin shekarunta amman tasan kaddara kuma tana yarda da ita sabida gwajin imanin bayi ce.
Cikin nutsuwa yay revars tare da jan motar ya fita daga cikin layin da ita,lokacin gari yay tsit sabida taran darema ta wuce gakuma walƙiya da akeyi sosai iska mai ƙura tana kaɗawa alamun hadarin garin gab yake da zubar da ruwa, kasancewar garin yanayin damuna ne.
Tafiyar mintuna goma daga layinsu bebi zuwa kan titi usman yay, lokacin da motar xata bar layin seda bebi tai kuka harda shashsheƙa,tana jin missing ɗin anguwarsu har wajan gawayin shahid ta kalla tana share hawayenta.
"Yanzu kai abinda kaimin tsakanin ka da girman ALLAH kayimin adalci kenan?".
Aliyu ya faɗa cikin ƙasa da murya wadd ta shaƙe kamar zeyi kuka!.
Cikin sauri usman ya kunna redion motar sabida bayason Bebi taji abinda zasu faÉ—i.
Ware redion yay da ƙarfi yana tukinshi batare daya tankawa Aliyun ba.
"Adalcin kenan kuma bana shakka sabida alkairi na ƙulla ba sharri ba, sannan kuma da sannu zakazo min da buhun godiya nan bada jimawa ba".
Cikin ƙufula ya kuma duban usman a karo na biyu.
"Daman haka zakace man, sabida kai kasan baka cikin case tayaya zan dubi abba nace masa nayi aure bai sani ba? tayaya zan fuskanci ammi, dan Allah kai akaran kanka kayimin adalci kenan kariga ka sakani acikin sarƙa wadda batada mabuɗi".
Dariya usman yay har yana dukan sitiyarin motar shi sannan ya kalli Aliyu wanda yake faman sababi yana jin ransa yakai ƙololuwar ƙarshe a ɓaci sannan yace.
"Karka damu mai afkuwa ta riga ta afku sedai muyi maku fatan addu'a ALLAH ya kawo ƙazantar ɗaki, haba ƙanina ka tambayeni shawara tare da hanyar warwareta nikuma naga wannan auren shi kaɗaine masalaha sabida ceton maraici kagafa in suka mata auren nan sun cuceta kuma kanada kamasho tunda kaine sila, Yanxu ko daka aureta ai magana ta ƙare, nina san abba yasan ciwon haihuwa baze taɓa cewa ka rabu da ita ba koda yay faɗan ma na lokacine amman ze huce, amman duk da haka yanzu zamu soma kaita wajan ammi semuji mizata ce".
Tunma kafin usman ya idda numfashinsa Aliyu ya kuma cafke maganar usman cikin hargagi da masifar dake ranshi wadda yake dannewa.
"Miya ruwanka dani, danna zo maka da shawara ina ruwanka da haɗani aure da ita ina ruwanka da shiga hurumina wallahi nai dana sanin gaya maka halin danake ciki kuma wallahi bada ban ƙimar wancan dattijon ba wallahi dase na saketa sedai kai ka aureta".
Ta inda yake shiga bata nan yake fitaba baƙaramin tsoro hakan ya bawa usman ba baitaɓa tunanin ƙanin nashi nada faɗa irin hakaba har suka ƙarasa gida yana masifa kamar ze ari baki.
Harda cewa usman ya cuce shi yaje ya auro masa ƴar cikinshi ko uban me ze ɗauka ajikinta oho yarinyar da ko wankan tsarki ƙilanma bata iya ba masifa tijara babu irin wadda baiyi a motarnan ba wanda har tsoro seda ya tsirgawa usman.
Inda Allah ma ya taimaka sun kunna redio yana da tabbacin bebin bazataji maganar dasuke ba ammn yasan inda taji abinda ALIN ke faÉ—a seta fishi shiga halin tsorata da zulumi.
Bai bar usman ya ƙarasa parking ba ya ɓalle marufin motar ya fice azuciye.
Cikin rawar jiki shima usman É—in ya balle nasa side É—in yabishi seda usman ya haÉ—a da gudu sabida Aliyu badai sauriba, yana ayyana yau na É—ebo ruwan dafa kaina
Hannu ya saka ya janyo kafaɗun Aliyu wanda harya kusan kaiwa ƙofar part ɗinshi.
Yadda kalar idanunshi suka sauya launin kala yay matuƙar razana usman sabida sunyi wani irin girma tare da ja kamar gauta wanda ko ba,a faɗa maka ba kasan yana cikin tsananin damuwa da fushi.
Sanin kanshine in Aliyu na cikin fushi ko ammi bata kulashi harse ya sauka, dan haka cikin sanyin jiki usman ya saki kafaÉ—un sa tare da komawa wajan motar ya rabu dashi har zuwa gobe.
Tsaki yaja da ƙarfi tare da banko gate ɗinshi ya shige batare dako ya juya wajan usman ɗin ba.
Yana son ko a iya wannan daren ne ya nunawa usman kuskurenshi na wannan shiga hanci da ƙudundunen daya masa wanda baƙaramin haushi usman ɗin ya bashi ba.
Haka ya ƙarasa cikin part ɗinshi azuciye kota kan ɗakin dija bai biba ya haura ɗakinshi ya faɗa saman gadonshi yana dafe kanshi dake barazanar tarwatse mashi bai shirya haɗa maganar daze fuskanci ammi ba, yana son dogon tunani da nazari kafin ya ƙaddamar da komai, zumbur ya miƙe zuwa gaban frij ɗin dake manne cikin ɗakin nashi budewa yay tare da ɗaukar gorar ruwan faro mai sanyi ya kafa a makoshinsa wanda ya bushe ƙaraf babu ko alamun miyau acikinshi seda ya shanye tass ya wurgar da gorar ya kuma ɗaukar wata ya shanye tass sannan ya mike yana rangaji kamar ɗan maye ya kuma faɗawa gadonshi ya shiga duniyar tunanin mafita?