Sashe 72
Abinda Ake Gudu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ma'u ta mike suka tafi. Mutumin dai basu sanshi ba amma sun fahimci labarin da ya kawo musu na cewa Zinaru zata sayar da gidan Zulaiha. Ma'u tace bari ta fada a cikin gida. Tare da Zulaihan suka fito. Tana ganinsa ta gane shi, lokacin da take tare da Gidado har dashi ake mata wulakanci kala kala wai shi mai 'ya. Yanzu kuwa russunawa yayi yana diban gaisuwa kafin ya sake mata bayanin abinda ya kawo shi. Zulaiha tayi masa godiya tace babu komai hukuma zata shiga zancen tana nuna Qasim. Garbebe ya dan tsaya yana jiran ihsani ladan kawo gulma yaga babu wanda yayi motsi cikinsu sai ya tafi kawai. Ko ba komai ya tarewa Zinaru hanyar samu.
Yana fita wata mota hadaddiya ta shigo gidan. Wani mutum ne a bayan motar dreba na jansa. Maigadi yana ta daga hannu saboda Alh Najib akwai kyauta. Kusa da inda Qasim, Ma'u da Zulaiha ke tsaye suna zancen hali irin na Gidado da Zinaru akayi parking motar ya fito. Da fara'asa ya mikawa Qasim hannu suka gaisa sannan ya gaisa da Ma'u da Zulaiha wadda ta kasa kallonsa ma.
Ciki ya shiga yace Alhaji na hanya zai jira shi ne. Bayan ya wuce Zulaiha ta tafi jikinta babu kwari. Ma'u tace "wannan Alhaji yaso aura mata fa taki yarda tun farko. Anti Zulaiha tayi masa wulakanci sosai gashi yanzu tana kunyarsa."
Qasim yace "rabon haihuwa yasa ta auri wancan. Kuma gara haka akan ta haifesu a titi. Tunda ba yau zan tafi ba sai ki fadawa Alhaji in shiga case din Gidadon nan"
"Ai kuwa zaiyi murna. Bari ya dawo anjima sai na fada masa".
*****
Cikin kwanaki biyu Zinaru da Gidado sun tattara komai nasu zasu bar gidan sannan yayi mata saki daya. Tayi ta rokon Zulaiha wai ko albarkacin yara ta yafe musu a mayar da auren. Ko kallon kirki basu samu ba daga gareta balle yan uwanta. Da kwanan titi gara na kauye a dole tayi shirin komaa garinsu wane kauye a cikin Taraba state. Bats sani ba mijinta da ta baro yana da rai ko ya mutu. Alhajin su Zulaiha yace lallai wasu daga cikin yayyenta maza su bi bayansu aga tushensu albarkacin yara.
Zinaru an sha kuka ga Amarya ma Garbebe ya karbar mata takardar saki. Su Humaira ko a jikinsu saboda irin mugun zaman da suka yi a hannun kakarsu da Babansu wanda bai san kowa ba sai kansa. Ganin idon Qasim ne ma yasa yabi Zinaru a son ransa ko a karkashin gada ya kwana indai zai sami ganyensa ya busa.
Alh Najib kuwa tunda yaji anyi saki ya sanar da Alhaji idan Zulaiha ta gama idda a fada mata har yanzu yana sonta. Yana da mata dai da yara hudu. Banda auren wuri shekarunta goma sha shida ta auri Gidado ko secondary bata gama ba.
*****
Sati biyu a tsakani aka taho nemawa Qasim auren Ma'u harda Col. Ishaq Jikamshi cikin tawagar su Alh Adamu. Wannan abu yayi dadi domin rashin auren Asmau bai sa sun kullaci juna ba. Daga zuwa kawo kudi Alhaji yace indai sun amince a kawo sadaki kawai a daura aure kada ayi ta wahalar da mutane. Haka kuwa akayi aka saka biki da tariya wata guda. Col. Ishaq ne ya kira Qasim da wannan albishir. Yayi murna sosai shikenan shima ya shiga sahun magidanta. Innarsa kuwa kamar tayi me don dadi. Allah Ya taumaketa danta yayi aure kuma ya auro yar mutumci irin wadda take so.
*****
Zuwa yanzu kowa yasan da cikin Asmau a cikin 'yan uwanta da nasa. Kulawa take samu ta kowane bangare kada Mami taji labari. Sosai take kaunarta yanzu.
Saura sati biyu bikin Qasim tana ta shirin zuwa Jos yana kallonta kawai. Ciki wata hudu ga laulayin da take fama amma ta dage da roko har da addua akan ya barta taje ko don Zulaiha. Sun gama rigimarsu yana ta shan kunu Amatullah tace masa tayi masa tuni zai kaita siyan takalmin makaranta na gudu. Da kyar ya yarda suka tafi da Asmau. A hanya aka shirya dama basa dogon fushi da juna. Sun gama siyayyarsu suna fitowa daidai inda suka ajiye mota suka hadu da wasu maza su biyu cikin shiga ta kamala kayansu ma iri daya. Daya ne ya kura mata ido har Col. Ishaq ya lura zaiyi masa magana Asmau ta kallesu. Baki ta bude cike da tsantsar mamaki.
"Annur, Gaddafi?"
ABINDA AKE GUDU🙆🏽60
Batul Mamman💖
Annur ya soma murmushi haka ma Gaddafi sannan yace "Antinmu wallahi da farko ban tabbatar kece ba. Alhamdulillah, Allah Ya kaddara zamu sake haduwa"
Gaddafi yace "an kusa shekara bakwai fa idan ma ba'ayi ba"
Asmau sai murmushi take da ta sake haduwa da 'yan samarin da suka taimaka mata lokacin da take nakudar Amatullah. Bata jin zata taba manta kammaninsu duk da a wancan lokacin suna tare da kuruciya sosai bata tunanin zasu kai shekara sha takwas ma. Jikamshinta ta kalla zata yi masa bayaninsu yace "kina fadan sunansu na gane ko su waye" shima fuskarsa da fara'a. Duk wanda ya taba taimakon Matarsa yana ganinsa da kima da daraja. Sannan bashi da mantuwar sunaye indai a tarihin rayuwarta ne.
Hannu ya mika musu suka gaisa yace shine mijinta. Fuskokinsu sun nuna jindadin wannan labari sosai. Col. Ishaq yace "ku shiga kuyi siyayyarku sai muje ku ga gidanmu saboda a cigaba da zumunci."
"Ai kuma mun fasa zamu dawo wani lokacin." Annur ne yayi maganar yana kallon Amatullah da alamar tambaya amma dai yayi shiru. Tasu motar suka shiga suka bi bayansu Asmau.
Col. Ishaq na tuki ta riko hannunsa daya tana murmushi.
"Nagode da ka gayyato su gida. Bani da abinda zan saka musu dashi da irin taimakon da suka yi min amma yadda ka karrama su kadai yasa naji dadi sosai."
Yayi mata murmushi "Matar Jikamshi, kin hadu da mutane da dama a rayuwarki wanda banda tsohuwar nan ta Azare kowanne cikinsu ya taka wata muhimmiyar rawa wurin nesanta rayuwarki daga lalacewa. Duk wanda ya taimakeki ni ya taimakawa dole na kyautata musu nima"
Tsohuwar da ya fada ta gane da Uwargida yake tayi 'yar dariya "Uwargida fa ta shiryu Jikamshina"
"Wani suna naji ta kiraki dashi shine raina ya baci."
Bata rai yayi sosai Asmau ta rinka dariya. Itama ta tsani wannan sunan wai 'Yar Dabas. Tuna mata yake da zamanta a gidan da irin bakar wuyar da ta sha. Tana dariya yana kallon bakinta ya dan sassauta murya "I miss you"
"Gani a kusa da kai fa"
"Ba ke ba wadannan lips din nake nufi"
Ta danyi fari da ido yace "nagode Allah da Ya bani ke Matar Jikamshi. Komai naki ina so, har da wannan fari da idon"
Kamar wadda aka jeho sai jin muryar Amatullah sukayi a tsakaninsu tana daga bayan mota tace "Babana inyi maka fayi da ido nima na iya"
Shiru suka yi duk su biyun. Saboda tana ta aikin gwada sabon takalminta sun manta tana motar ma. Ta sake maimaita tambayar yace "Princess ba kyau ayi fari da ido"
Ta turo baki "Amma kacewa Ummi kana so tayi"
Tohhh yarinya zata kure babanta. Asmau kyalesu tayi don tasan halin Amatullah yanzu ta rinka jan zancen da wata sabuwar tambayar kenan.
Sake tunani yayi sannan yace mata "baki ji abinda na fada bane sosai, cewa nayi akwai abu a saman idonta ina so tayi fari da idon sai ya fadi"
Amatullah ta koma ta zauna tana cewa "auuu ashe banji ba. Amma dai na iya fayin inyi maka?"
Rike dariyarsa yayi yace mata ta bari su je gida yanzu tuki yake yi. Shi da Asmau suka hada ido suka yi murmushi. Dole ne su rinka kiyaye abinda suke yi a gaban Amatullah don wayo ne da ita. Sai kaga kamar bata kula da abu ba sai zance ya tashi ta maido dashi.
Kyakkyawar tarba suka yiwa su Gaddafi. A nan suke bata labarin yadda rayuwarsu ta canja bayan haduwa da ita da suka yi harda komawarsu asibiti nemanta. A yanzu basu dade da dawowa daga Jami'ar Madinah ba inda sukayi degree. Asmau taji dadi da ta kasance silar shiriya garesu. Sunyi hira sosai da Col. Ishaq aka nuna musu Amatullah a matsayin yarinyar da ta haifa. Da zasu tafi duk su biyun sunyi mata alkhairi na kudi wanda su Asmau suka nuna rashin amincewarsu. Gaddafi yace sun dauketa kamar 'yarsu ne don Allah kada a mayar da hannun kyauta baya.
Haka su rabu cikin mutunta juna har nambobinsu na waya Col. Ishaq ya karba.
A hanyarsu ta komawa shagon ne Annur ya cewa Gaddafi "gaskiya mijin Antinmu yana da kirki sosai. Kuma ko ba'a fada ba ba karamin so yake mata ba. Yarinyar nan Amatullah nake tausayi. Nan gaba zata ji babu dadi idan ta gane yadda aka haifeta. Aure wannan sai kaga yazo da matsala saboda bata da uba"
Gaddafi yana tuki yace "haka ne amma komai na Allah ne. Gashi cikin ikonsa mamanta ma tayi aure. Nifa saboda labarinta kasan na gama tsorata da harkar mata. Haka kawai shaidan ya gifta tsakaninmu na nazo na mutu na bar 'yar mutane da ciki. Idan ban tuba ba me zan fadawa Allah"
"Shiyasa hakan da muke zaune yafiye min komai, idan mun tashi aure sai mu nema ya zamana babu wannan doguwar soyayyar ayi komai idan anyi auren"
Dariya Gaddafi yayi "nifa na sami wata sai munje gida zan baka labari. Ban riga na fada mata ba sai munyi shawara da kai"
Annur yayi dariya "na dade da gano ku ai, jira nake naji yadda za'ayi abin ban sani ba. Ba Noor kake so ba?"
Mamaki ne ya bayyana a kan fuskar Gaddafi. Tabbas kanwar abokinsa yake so amma ko ita bata sani ba. Annur ya bashi goyon baya sosai yace ai yana kula da yadda baya iya boye son nata idan ya ganta.
"Kai kuma wa ka samo mana?"
"Kaji lokacin da Amatullah tace min Uncle Annuy? Daga lokacin na kudurtawa zuciyata ita zan jira. Yadda Col. Ishaq ya wankewa Antinmu bacin rai na rayuwa haka nake fatan nayi mata nan gaba"
Gaddafi yana tuki yana dariya "haba dai Annur kayi mata tsufa wallahi. Shekararka kusan ashirin da biyar fa. Ka bari ta sami yaro daidai ita"
Yana fita wata mota hadaddiya ta shigo gidan. Wani mutum ne a bayan motar dreba na jansa. Maigadi yana ta daga hannu saboda Alh Najib akwai kyauta. Kusa da inda Qasim, Ma'u da Zulaiha ke tsaye suna zancen hali irin na Gidado da Zinaru akayi parking motar ya fito. Da fara'asa ya mikawa Qasim hannu suka gaisa sannan ya gaisa da Ma'u da Zulaiha wadda ta kasa kallonsa ma.
Ciki ya shiga yace Alhaji na hanya zai jira shi ne. Bayan ya wuce Zulaiha ta tafi jikinta babu kwari. Ma'u tace "wannan Alhaji yaso aura mata fa taki yarda tun farko. Anti Zulaiha tayi masa wulakanci sosai gashi yanzu tana kunyarsa."
Qasim yace "rabon haihuwa yasa ta auri wancan. Kuma gara haka akan ta haifesu a titi. Tunda ba yau zan tafi ba sai ki fadawa Alhaji in shiga case din Gidadon nan"
"Ai kuwa zaiyi murna. Bari ya dawo anjima sai na fada masa".
*****
Cikin kwanaki biyu Zinaru da Gidado sun tattara komai nasu zasu bar gidan sannan yayi mata saki daya. Tayi ta rokon Zulaiha wai ko albarkacin yara ta yafe musu a mayar da auren. Ko kallon kirki basu samu ba daga gareta balle yan uwanta. Da kwanan titi gara na kauye a dole tayi shirin komaa garinsu wane kauye a cikin Taraba state. Bats sani ba mijinta da ta baro yana da rai ko ya mutu. Alhajin su Zulaiha yace lallai wasu daga cikin yayyenta maza su bi bayansu aga tushensu albarkacin yara.
Zinaru an sha kuka ga Amarya ma Garbebe ya karbar mata takardar saki. Su Humaira ko a jikinsu saboda irin mugun zaman da suka yi a hannun kakarsu da Babansu wanda bai san kowa ba sai kansa. Ganin idon Qasim ne ma yasa yabi Zinaru a son ransa ko a karkashin gada ya kwana indai zai sami ganyensa ya busa.
Alh Najib kuwa tunda yaji anyi saki ya sanar da Alhaji idan Zulaiha ta gama idda a fada mata har yanzu yana sonta. Yana da mata dai da yara hudu. Banda auren wuri shekarunta goma sha shida ta auri Gidado ko secondary bata gama ba.
*****
Sati biyu a tsakani aka taho nemawa Qasim auren Ma'u harda Col. Ishaq Jikamshi cikin tawagar su Alh Adamu. Wannan abu yayi dadi domin rashin auren Asmau bai sa sun kullaci juna ba. Daga zuwa kawo kudi Alhaji yace indai sun amince a kawo sadaki kawai a daura aure kada ayi ta wahalar da mutane. Haka kuwa akayi aka saka biki da tariya wata guda. Col. Ishaq ne ya kira Qasim da wannan albishir. Yayi murna sosai shikenan shima ya shiga sahun magidanta. Innarsa kuwa kamar tayi me don dadi. Allah Ya taumaketa danta yayi aure kuma ya auro yar mutumci irin wadda take so.
*****
Zuwa yanzu kowa yasan da cikin Asmau a cikin 'yan uwanta da nasa. Kulawa take samu ta kowane bangare kada Mami taji labari. Sosai take kaunarta yanzu.
Saura sati biyu bikin Qasim tana ta shirin zuwa Jos yana kallonta kawai. Ciki wata hudu ga laulayin da take fama amma ta dage da roko har da addua akan ya barta taje ko don Zulaiha. Sun gama rigimarsu yana ta shan kunu Amatullah tace masa tayi masa tuni zai kaita siyan takalmin makaranta na gudu. Da kyar ya yarda suka tafi da Asmau. A hanya aka shirya dama basa dogon fushi da juna. Sun gama siyayyarsu suna fitowa daidai inda suka ajiye mota suka hadu da wasu maza su biyu cikin shiga ta kamala kayansu ma iri daya. Daya ne ya kura mata ido har Col. Ishaq ya lura zaiyi masa magana Asmau ta kallesu. Baki ta bude cike da tsantsar mamaki.
"Annur, Gaddafi?"
ABINDA AKE GUDU🙆🏽60
Batul Mamman💖
Annur ya soma murmushi haka ma Gaddafi sannan yace "Antinmu wallahi da farko ban tabbatar kece ba. Alhamdulillah, Allah Ya kaddara zamu sake haduwa"
Gaddafi yace "an kusa shekara bakwai fa idan ma ba'ayi ba"
Asmau sai murmushi take da ta sake haduwa da 'yan samarin da suka taimaka mata lokacin da take nakudar Amatullah. Bata jin zata taba manta kammaninsu duk da a wancan lokacin suna tare da kuruciya sosai bata tunanin zasu kai shekara sha takwas ma. Jikamshinta ta kalla zata yi masa bayaninsu yace "kina fadan sunansu na gane ko su waye" shima fuskarsa da fara'a. Duk wanda ya taba taimakon Matarsa yana ganinsa da kima da daraja. Sannan bashi da mantuwar sunaye indai a tarihin rayuwarta ne.
Hannu ya mika musu suka gaisa yace shine mijinta. Fuskokinsu sun nuna jindadin wannan labari sosai. Col. Ishaq yace "ku shiga kuyi siyayyarku sai muje ku ga gidanmu saboda a cigaba da zumunci."
"Ai kuma mun fasa zamu dawo wani lokacin." Annur ne yayi maganar yana kallon Amatullah da alamar tambaya amma dai yayi shiru. Tasu motar suka shiga suka bi bayansu Asmau.
Col. Ishaq na tuki ta riko hannunsa daya tana murmushi.
"Nagode da ka gayyato su gida. Bani da abinda zan saka musu dashi da irin taimakon da suka yi min amma yadda ka karrama su kadai yasa naji dadi sosai."
Yayi mata murmushi "Matar Jikamshi, kin hadu da mutane da dama a rayuwarki wanda banda tsohuwar nan ta Azare kowanne cikinsu ya taka wata muhimmiyar rawa wurin nesanta rayuwarki daga lalacewa. Duk wanda ya taimakeki ni ya taimakawa dole na kyautata musu nima"
Tsohuwar da ya fada ta gane da Uwargida yake tayi 'yar dariya "Uwargida fa ta shiryu Jikamshina"
"Wani suna naji ta kiraki dashi shine raina ya baci."
Bata rai yayi sosai Asmau ta rinka dariya. Itama ta tsani wannan sunan wai 'Yar Dabas. Tuna mata yake da zamanta a gidan da irin bakar wuyar da ta sha. Tana dariya yana kallon bakinta ya dan sassauta murya "I miss you"
"Gani a kusa da kai fa"
"Ba ke ba wadannan lips din nake nufi"
Ta danyi fari da ido yace "nagode Allah da Ya bani ke Matar Jikamshi. Komai naki ina so, har da wannan fari da idon"
Kamar wadda aka jeho sai jin muryar Amatullah sukayi a tsakaninsu tana daga bayan mota tace "Babana inyi maka fayi da ido nima na iya"
Shiru suka yi duk su biyun. Saboda tana ta aikin gwada sabon takalminta sun manta tana motar ma. Ta sake maimaita tambayar yace "Princess ba kyau ayi fari da ido"
Ta turo baki "Amma kacewa Ummi kana so tayi"
Tohhh yarinya zata kure babanta. Asmau kyalesu tayi don tasan halin Amatullah yanzu ta rinka jan zancen da wata sabuwar tambayar kenan.
Sake tunani yayi sannan yace mata "baki ji abinda na fada bane sosai, cewa nayi akwai abu a saman idonta ina so tayi fari da idon sai ya fadi"
Amatullah ta koma ta zauna tana cewa "auuu ashe banji ba. Amma dai na iya fayin inyi maka?"
Rike dariyarsa yayi yace mata ta bari su je gida yanzu tuki yake yi. Shi da Asmau suka hada ido suka yi murmushi. Dole ne su rinka kiyaye abinda suke yi a gaban Amatullah don wayo ne da ita. Sai kaga kamar bata kula da abu ba sai zance ya tashi ta maido dashi.
Kyakkyawar tarba suka yiwa su Gaddafi. A nan suke bata labarin yadda rayuwarsu ta canja bayan haduwa da ita da suka yi harda komawarsu asibiti nemanta. A yanzu basu dade da dawowa daga Jami'ar Madinah ba inda sukayi degree. Asmau taji dadi da ta kasance silar shiriya garesu. Sunyi hira sosai da Col. Ishaq aka nuna musu Amatullah a matsayin yarinyar da ta haifa. Da zasu tafi duk su biyun sunyi mata alkhairi na kudi wanda su Asmau suka nuna rashin amincewarsu. Gaddafi yace sun dauketa kamar 'yarsu ne don Allah kada a mayar da hannun kyauta baya.
Haka su rabu cikin mutunta juna har nambobinsu na waya Col. Ishaq ya karba.
A hanyarsu ta komawa shagon ne Annur ya cewa Gaddafi "gaskiya mijin Antinmu yana da kirki sosai. Kuma ko ba'a fada ba ba karamin so yake mata ba. Yarinyar nan Amatullah nake tausayi. Nan gaba zata ji babu dadi idan ta gane yadda aka haifeta. Aure wannan sai kaga yazo da matsala saboda bata da uba"
Gaddafi yana tuki yace "haka ne amma komai na Allah ne. Gashi cikin ikonsa mamanta ma tayi aure. Nifa saboda labarinta kasan na gama tsorata da harkar mata. Haka kawai shaidan ya gifta tsakaninmu na nazo na mutu na bar 'yar mutane da ciki. Idan ban tuba ba me zan fadawa Allah"
"Shiyasa hakan da muke zaune yafiye min komai, idan mun tashi aure sai mu nema ya zamana babu wannan doguwar soyayyar ayi komai idan anyi auren"
Dariya Gaddafi yayi "nifa na sami wata sai munje gida zan baka labari. Ban riga na fada mata ba sai munyi shawara da kai"
Annur yayi dariya "na dade da gano ku ai, jira nake naji yadda za'ayi abin ban sani ba. Ba Noor kake so ba?"
Mamaki ne ya bayyana a kan fuskar Gaddafi. Tabbas kanwar abokinsa yake so amma ko ita bata sani ba. Annur ya bashi goyon baya sosai yace ai yana kula da yadda baya iya boye son nata idan ya ganta.
"Kai kuma wa ka samo mana?"
"Kaji lokacin da Amatullah tace min Uncle Annuy? Daga lokacin na kudurtawa zuciyata ita zan jira. Yadda Col. Ishaq ya wankewa Antinmu bacin rai na rayuwa haka nake fatan nayi mata nan gaba"
Gaddafi yana tuki yana dariya "haba dai Annur kayi mata tsufa wallahi. Shekararka kusan ashirin da biyar fa. Ka bari ta sami yaro daidai ita"