← Book details Abinda Ake Gudu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 46 OF 74

Sashe 46

Abinda Ake Gudu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Sosai Haj Lubabatu taji tausayin Ishaq. Duk sallah bata fasa yi masa adduar samun rabo saboda yadda yake son yara. Da suna kanana har goya masa kannensa tana yi saboda yadda yake mata nacin zaiyi raino. Sai ayi goyon ya zauna a falo ko baki tayi baya jin kunya.
"Dole kayi aure shine cikar dan Adam. Kayi addua kamar yadda nake maka. Allah Ya kawo maka mace tagari" ya amsa da amin amma ba don yana tunanin zai kara son wata bayan Asmau ba. Shi fa bashi da raayin auren da babu soyayya. Kuma soyayyarsa ta kare a wurin Matar Jikamshi.

Ya kai hannu kan giya zai canja yaji Bilkisu ta dora nata a saman nasa ta kankame. Ya dan kalleta ya kula kuka take yi a hankali. Yace "nine ko, nasa Maminki kuka"

Muryarta na rawa tace "a'a Uncle don Allah kada kaki auren Ummin Amatullah"

Murmushi kawai yayi yana kwanar shiga asibitin motar Musaddiq tana bayansa.
"Allah Yayi miki albarka kinji. Ki cire duk abinda kika ji dazu daga ranki.... Wai ma wa ya koya miki labe? Bari mu dawo yau sai kinyi tsallen kwado"

Da guntun hawayenta tayi murmushi. Hajiya ma murmushin tayi. Taji dadi da fushinsa bai shafi 'ya'ya ba.

Boot dinsa ya bude ya fito da ledoji biyu cike da tarkacen kayan kwadayi na yara sai katon din ziza. Yana tasowa daga office ya siyo kafin ya wuce gida. Bilkisu tazo taya shi dauka sai ga su Ismail da sauri kowa ya dauki abu daya cikin su mazan. Ya kawar da kansa gefe don yasan suna neman shiri ne. Abinda bazasu samu kenan a nan kusa ba.
*****

Shi da Hajiya ne a gaba sai Bilkisu da ta jero tare da Mami da Safiyya tana tambayar Mamin kannenta. Sun kusa zuwa dakin suka ga wata mace ta fito daga wani daki da hijab dinta har gwiwa tana kuka. Col. Ishaq bai san lokacin da ya isa gabanta ba da sauri ba hankali a tashe yace "Matar Jikamshi menene?"

Asmau kuka take yi kawai "Amatullah ce ta sake samun attack. Likita zan kira"

Shima a rude yake yace "koma wurinta bari na kira likitan"

Kasa komawa dakin tayi tabi bayanshi da gudu tana ta zubar da hawaye. Duk sunji tausayin Asmau da yadda ta gigice. Dakin da suka ga ta fito Hajiya tace "mu shiga mu jirasu"

Mami ta bude kofar suka shiga da sallama. Mama Yalwa ce a tsaye kan Amatullah tana ta kakari. Safiyya na jin yadda take kakarin ta matsa kusa da gadon da sauri tace "wannan ba attack din asthma bane. Ba kuji yadda take numfashin ba, majina ce a kirjinta"

Mama Yalwa tana jin haka ta saka bakinta a hancin Amatullah ko kyama babu ta rinka zuke mata tana tofarwa. Tana kaunar Safina fiye da sauran jikokinta sosai saboda yarinya ce mai tattare da tabo mai muni a rayuwarta. Bayan zina mace aka fi gani da nason zunubin duk da cewa dole idan anyi akwai namijin da suka yi tare. To amma namijin sai ya tsira daga aibatawar mutane saboda shi ba'a ganewa a jikinsa. Idan ya karyata babu yadda za'ayi dashi. Sharrin zuciya ya cutar da Abubakar wanda yayi sanadin cutar da Asmau. Gashi a karshe Safina ita ce abin ya kare a kanta. Mama ta dan share hawayenta sai ga Amatullah ta ware saboda hancinta ya bude.

Sai a lokacin suka gaisa dasu Haj Lubabatu. Mama tace "Hajiya duk wadannan yaranki ne? Masha Allah"

Hajiya ta dan murmusa "ya mai jikin?"

Mama tace " gata nan duk ta ruda mu." Ta kalli Safiyya "nagode miki kinji. Ya sunanki ne?"

Safiyya ta fadi sunanta kenan su Asmau suka shigo tare da likita. Ga mamakinsu a zaune Amatullah take ta jingina da pillow. Asmau taji wani sanyi a ranta sannan ta matsa kusa da Amatullah tana mata sannu. Likitan ya dubata ya tabbatar harda mura tayi mata mugun kamu. Magunguna yace zai turo nurse ta kawo musu.

Bayan fitar likitan Asmau ta gaishe da su Mami. Cikin su babu sa'anta duk sun girmeta. Sun amsa mata fuskokinsu babu yabo babu fallasa. Col. Ishaq yana tsaye daga wurin kofa. Idonsa kyam akan Asmau har 'yan uwansa suka fuskanci yadda suke jifan juna da kallo. Ita duk kunya ma take ji musamman saboda su Hajiya da Mama.

Amatullah ce ta kurawa Ismail ido tace "kai da Babana iyinku daya. Kaima sunanka Jikamshina?" saboda irin kamaninsa da Ishaq.

Ya Salam, Asmau ji tayi kamar kasa ta tsage ta shige. Allah Ya taimaketa ma Amatullah bata ce irin yadda Ummia ke fada ba. Don kadan daga aikinta ne yin hakan.Col. Ishaq kansa yau yaji kunya karo na farko a rayuwarsa game da fadin magana a gaban kowaye batare da yaji komai ba.

Su Musaddiq sai kallon kallon kallo ana dan murmushi. Ismail kuwa yace mata "nima babanki ne 'yan mata" ya karasa wurin gadon da murmushinsa.
Ta kalli Col Ishaq tayi masa gwalo " Babana kaga nayi sabon baba ko. Ni yanzu na dena yin baba da kai"

Yace "subhanallahi me nayiwa princess dina haka. Kai Ismail tashi ka bani wuri mu sasanta ni da 'yata"

'Yar dramarsu tasa mutanen dakin dariya. Amatullah tayi saurin rike hannun Ismail tace "yanzu baka wasa dani sosai sai da Ummi na. Nima ga sabon Baba nayi"

Asmau ta rasa abin cewa. Tsiyar yaro mai surutu fa kenan. Yau Amatullah ta gama bata kunya.

Safiyya tace "amma da baban nan naki da Ummi basu kyauta ba. Yanzu ga sabo nan mun baki. Amma kiyi hakuri Babanki so yake ku koma gidansa sai ku rinka wasan tare kullum shiyasa yake yi da Umminki"

Kana gani kasan Amatullah taji dadin wannan zancen tace "Ummi kuje kuyi wasa da Babana to idan kun gama mu koma gidansa."

Yau kam ta kai karshen jin kunya, shi kuma Col. Ishaq saboda shawarar da ya yanke ta rabuwa da ita shiyasa yau bai bada amsar da zata karasa bata kunya ba.

Hajiya da Mama Yalwa sai sunkiyar da kai suke. Ita Mama harda mamakin dama son Asmau sojan nan yake bata sani ba.

Ismail ji yayi ta shiga ransa. Dama yana son 'ya mace gashi duk maza gareshi.
"Ki kyale wancan Baban kawai kinga a gidana zan siyo miki kayan wasa da alawa"

Tace "ai Ummi ma tana siya min. Ta hanani kwadayi. Kuma bana yi sai tace min Allah Yayi miki albayka"

Yarinya karama sai basu sha'awa take yi. Mami kallon Asmau take yi. Yanzu mace mai kamannin kamala irin haka ace a waje ta haihu. Kai wannan duniya mai rudin bayin Allah.

Amatullah ta sake cewa "sabon Babana in kayanta maka Allahu?"

Dahiru yace mata "karatu ake cewa ba kayatu ba"

Tuni ta bata rai "kayatu fa nace ba kayatu ba"

Daki ya kaure da dariya. Col. Ishaq yana kallon yadda 'yan uwansa duk suka mayar da hankali gareta. Murmushi yayi yana fatan ko nan gaba idan ya roki alfarmar a bari tazo gidansu ta yini wurin Hajiya bazasu yi mata gori ba. Ido suka hada da Asmau tayi murmushi sai taga ya dan sunkuya kamar zai duba waya. Bata kawo komai a ranta ba.

Ismail ya samu shiga wurin Amatullah yace "karanta min a kunnena ni kadai kada su ji"

Ta fito da ido da mamaki "Ummi fa tace mai yada mai yada dan wuta, mai ji mai ji kafiyi." Nan dariya aka yi suka ce to sai ya kiyaye yarinya tasan rada babu kyau.

Daga kai yayi ya kalli Asmau ta danyi murmushin jin kunyarsa. Su Mami suma mamakinta suke yi. Ga dai ta yadda ta haifi 'yar nan amma ga dukkan alamu tana da tarbiya sosai. Tunda ta bude baki ta fara karanto sunayen Allah gudu biyar da tsallake. Musaddiq ji yayi inama 'yarsa ce. Ga muryarta akwai dadi tana yi kamar da addu'a
"YA RAHMANU YA ALLAH-AMIN
YA RAHIMU YA ALLAH-AMIN
YA MALIKU YA ALLAH-AMIN...."

Haka tayi ta yi har karshe. Mami ta y kurawa Asmau ido, yarinyar bata da makusa sai abinda tayi a baya. Idan har aurenta zai sa dan uwanta ya dawo mata kamar da, to zata amince da auren nan. Sai dai fa dole su shirya da jin surutu da gorin 'yan uwa da sauran mutane.
Copied By
HAYATU BABA ZUBAIRU
(admin
Arewa hausa novels
Novels villa
Duniyan novels
Hayat hausa novels
Hausa novels and fashion
And
Cool novel, makeup and cooking)

WHATSAPP NO:
+2347039625239

ABINDA AKE GUDU🙆🏽46

Batul Mamman💖

Surutun Amatullah ke tashi a dakin da masu biye mata. Tsakani da Allah ta shiga zuciyar Ismail. A ransa ji yake ina ma yarinyar nan ta cika 'ya kamar kowa. Ta tashi har karshen rayuwarta bazata taba jin wata magana mai muni game da haihuwarta ba. Col. Ishaq kuwa Asmau har ta gaji da kallon inda yake tsaye. Duk iya yinta ta kasa yin sa'ar kallonsa a daidai lokacin da yake kallonta. Shi kuma yana sane yake dauke kansa daga gareta idan yaga ta dago nata kan. Duk son da yake mata dole ya rabu da ita indai tsakaninsa da Allah yana son farincikinta. Duk wani tanadi da yake yi mata da Amatullah maganar Ismail ta rusa komai. Zaiyi kokarin taimakonta ta kowane fanni na rayuwa musamman karatu da tace tana son komawa. A shirye yake ya dauki nauyin hakan idan bazai kawo matsala tsakaninta da wanda ta aura ba. Ko kawai ya hada kudi ya bata a matsayin gudunmawar aure. Shi kadai yake ta tunaninsa har su Umma suka shigo ita da Anti Bintu da Shemau.

Ba haka su Mami suka tsammaci ganin dangin Asmau ba. Gashi dai suna da rufin asiri sannan ga hadin kai. Wani abin mamaki wai harda babar wanda yayiwa Asmau ciki ake jinyar Amatullah. Mamakinsu bai karu ba sai da Alh Adamu ya shigo. Mutum mai fara'a jan mutane a jiki. Ya gaisa da kowa sannan ya zauna yana tsokanar Amatullah. Lokacin dakin ya cika sosai shiyasa Haj Lubabatu tace su tashi su tafi.
Chapter 46 · 0% Book details