← Book details Abinda Ake Gudu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 22 OF 74

Sashe 22

Abinda Ake Gudu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Da sauri yaja hannun abokinsa suka shiga mota. Gaddafi ya leko da kansa ta taga yana kallon Asmau kwance a kasan gefen titi. Motoci basu da yawa saboda har lokacin goma na safe bata yi ba. Gashi titin fita gari ne.

Annur ya fizgi motar da gudu Gaddafi yana rokonsa da su taimaka ko wane gari suka gani su sauketa a nan wani ya kaita asibiti. Tsaki da zagi Annur ya rinka yiwa abokinsa kafin ya juyo da motar suka dawo inda take. Ransa a bace yace Gaddafi ya shigo da ita. Kuma ya zauna a baya tare da ita saboda kada ta kai masa duka. Shi duk saurinsa ya isa party din abokinsa da za'ayi a Jos batare da sun sami matsala a hanya ba domin kuwa ko license na tuki basu dashi.

Da sauri Gaddafi ya taimakawa Asmau ya shigar da ita motar. Ciwo ya fara tsananta a gareta sai gumi take yi. Annur ya soma yiwa Gaddafi magana da turanci
"Tun farko da nasan haka zaka yi min da ban ce ka raka ni Jos dinnan ba. Amma babu komai zanyi maganinka. Hmmm yau 'yan matan Jos suna da manyan baki" ya karasa maganar yana wata shu'umar dariya.

"Kayi hakuri Annur ni kaina bansan meyasa ta bani tausayi ba. Ji fa yadda take gumi ko magana bata iyawa. Allah Ya tsinewa wanda yayi mata cikin nan dai"

Ciwon taji ya lafa mata ta kallesu tayi dan murmushi. Ga dukkan alamu Yassar zai girmesu duk su biyun. Ita ma turancin tayi musu wanda hakan yasa hankulansu dawowa gareta
"Wanda yayi min ciki ya rasu fatana Allah Ya jikansa. Ku kuma ina yi muku fatan shiriya daga Allah kada ku fada mummunan hali nan gaba."

Annur ya juyo kamar ba shine yake tuki ba yana kallonta da mamaki dan sauran mayen da yake duk ya tafi "wai dama ke ba mahaukaciya bace. Gaddafi kaga ka dauko mana masifa ko? Ke police ce ko 'yar mafiya?"

Kasa bashi amsa tayi saboda ciwo. Yana maida kansa titi saura kadan ya bugawa wani. A haka ya cigaba da tukin Gaddafi yana yi mata sannu. Sun isa wani gari yayi kokarin tsayawa su sauketa sai ya kula da 'yan sanda a gefen wurin. Dolensa ya sake taka mota yana ta sharara gudu. Basu tsaya a ko'ina ba sai da suka shigo garin Jos. A wannan lokacin ba karamin tausayin Asmau duka su biyun suke ji ba. Wai dama hake ake nakudar gaske ba ta fim ba. Idan taji ciwo tana addua sai taji suna tayata suna yi tare. Idan ka matso kusa da motar sai ka zata duk su ukun suke nakudar, sai sharba gumi suke yi kamar babu AC a motar . Bakin gate din wani asibiti da yayi musu kama da na gwamnati suka tsaya. Sai da Annur ya taimakawa Gaddafi suka fitar da ita daga motar. Tsoronsu daya kada a kamasu ayi tunanin ko sato ta sukayi ko suna da alaka da ita.

Cikin tsananin jin ciwo Asmau ta tambayi sunansu suka fada mata.
"Bansan daga ina kuke ba amma ina muku fatan alkhairi da shiriya don nasan iyayenku ba rayuwar da suke yi muku fata ba kenan. A duk inda kuke ku rinka tunanin lahirarku. Nagode sosai."

Daga haka ta lallaba ta karasa bakin gate din. Wannan karon sai da Gaddafi yayi da gaske Annur ya ja motar suka tafi.

Kasa daga kafarta tayi taji kamar zata fadi wata mata mai uniform din masu shara da wanke bandaki ta tareta daga baya tana yi mata sannu. Daga nan bata san da yadda aka shigar da ita asibitin ba. Ko awa daya bata cika ba Allah Ya taimaketa ta haihu.

Tana jin wannan kukan na jarirai taji gabadaya damuwarta ta gushe burinta kawai taga abinda ta haifa. Nurse din da ta karbi haihuwar tace mata kin sami 'ya mace. Asmau tayi murmushi tare da dago kai ta kalli kyautar da Allah Yayi mata tana hamdala. Gata da 'yar Abubakar sai dai babu shi kuma babu iyayensu. Kaddara ta riga fata a kansu. Ba don haka ba da yanzu iyayensu za'a mikawa jaririyar.

A wani dan zani aka nade 'yar aka miko mata. Ta zuba ido tana kallonta. Sai kuma kuka ya kwace mata da ta tuna bata da wata hanyar kulawa da 'yar. Ko suturar da zata saka mata bata da ita. Wannan mai sharar tayi mata Allah Ya raya sannan ta fita daga dakin. Ba jimawa ta dawo da wasu tsofaffin riga da zani amma a wanke ta bawa Asmau fuskarta a sake.
"Ga wannan akwai ruwa a bandaki ki gyara jikinki sai ki saka. Idan kin fito sai ki fadi wa za'a kirawo a danginki."

Asmau kamar kada ta bata yarinyar haka take ji. A rayuwarta bata taba son wani kamar yadda take jin son jaririyarta ba. Tayi godiya ta karbi kayan ta wuce bandakin.

Bata dade ba ta fito aka kaita dakin hutu. Wani likita yazo ya dubata yace babu wata matsala amma sai da safe zasu sallameta. Ya bata takardar magungunan da zata siya. Bayan fitarsa mai sharar ta kara dawowa wurinta ta sake tambayarta ina 'yan uwanta saboda a bakin gate ta ganta ita kadai. Ya kamata a sanar dasu ko don su kawo mata abinci da kayan baby.

Asmau bata da amsar da ta wuce kuka. Matar sai ta kyaleta ta koma bakin aikinta. Ita kuma ta cigaba da kallon jaririyarta tana bacci. Ikon Allah, yarinyar kama take yi da Mama Yalwa. Asmau sai ta rantse duk 'ya'yan Mama babu mai kama da ita kamar wannan yarinyar. Dama duk sunfi kama da Alh Adamu. Da namiji ta haifa dama sunan Abubakar zata saka masa. Amma tunda mace ce zata saka sunan mahaifiyarsa kamar yadda suka yiwa juna alkawarin sai sun sakawa 'ya'yansu sunayen iyayensu. Da wannan tunanin ta danyi murmushi. Babbar matsalarta yanzu bata san ta ina zata fara ba? Bata da komai bata da kowa. Sannan bata san irin tarbar da za'ayi mata ba idan ta koma gidansu.

Wannan tunanin ya isheta ga kudin asibiti duk da na gwamnati ne tasan ko yaya za'a bukaci ta biya kudin wani abin. Hakan ne yasa tana ganin duhun dare yayi ga cikinta kamar anyi mata yasa don yunwa ta kwance dankwalinta ta goya jaririyar da shi sannan ta zura hijab dinta tayi waje. Gara ta gudu tun kafin ace ta kawo kudin da tasan bata da su. Ta kusa karshen barandar da zata kaita bakin gate ne taji muryar mai sharar nan tace "ba dai guduwa zakiyi ba".

*****
Hajjo ce ta farka daga bacci a gigice ta rinka juyi akan gado har ta tabbatar dai a dakinta take. Hawaye ne kwance a fuskarta sakamakon mafarkin da tayi da jikarta Asmau. Kuka ta ganta tana yi tana kiran Hajjon da ta taimaketa. Duk yadda taso ta kama hannun Asmau ya gagara har ta farka. Jikinta sai karkarwa yake ta tashi ta dauko mayafinta a gefen kujerar dakin ta tafi dakin Garzali. Ko agogo bata duba ba tayi sa'a ta same shi yana fesa turare da alama fita zaiyi.

Tsayuwar kirki ta kasa cikin tsawa tace yazo ya kama karnukansa zata fita.

"Hajjo ina zaki je da yamman nan. Biyar da rabi fa".

Harararsa tayi fuska a murtuke don kada ya kawo mata wargi "inda ka aike ni zani. Kaga kada ka bata min lokaci wuce muje".

Suna fitowa yayiwa karnukan fito suka yo kansa Hajjo ta samu ta fice. Don sauri kafarta har zafi take yi mata taji takun mutum kamar ana binta da gudu. Duk da a tsorace take haka ta dake bata juya ba take magana
"Rabe wallahi yau ko me zaka ce sai naje wurin Bara'atu. Ba kai ka haifa min Shu'aibu ba shiyasa baka san ciwon iyalinsa ba."

Garzali yayi yar dariya
"Ni ne Hajjo. Raka ki zanyi. Nima rashin mu'amala dasu ba karamin damuna yake yi ba."

Tayi murmushi "Allah Yayi maka albarka" daga nan ta bashi labarin mafarkin Asmau da tayi suna tafiya.

*****
Tun kafin azahar Zubaida ta iso garin Kano ta samu mai tasi suna ta yawo a unguwar Hotoro basu gane gidan ba. Gajiya yayi ya sauketa bayan ya karbi dubu biyu a hannunta. Har zai tafi sai ya dawo saboda ta bashi tausayi yace ta sami mai adaidaita sahu sunfi sanin layukan cikin unguwa.

Tayi sa'a kuwa ta sami wani ta fada masa inda take nema. Da ya kula bakuwa ce a garin ya tsula mata kudi sai dai bata damu ba. Biyan bukata yafi dogon buri. Kusan dubu talatin ta dauko a cikin kudin da Uwargida ta bawa Yaya Babba.

A cikin layin mai adaidaita sahun ya nuna mata gidan kwamishina. Tayi masa godiya ta bashi kudinsa. Daga nan tasan Asmau tace gidansu babu nisa. Wata tsohuwa ta hango da wani mutum a bakin gate din wani gida tayi saurin karasawa kafin su shiga.

Sallama ta rinka yi musu suka juya suna kallonta a tare. Riga da siket ne a jikinta sun dameta sosai ga katuwar jakar kaya sai wani siririn mayafi da ta rataya a wuya. Da murmushi a fuskarta ta dan rissina ta gaishesu sannan tace "don Allah gidan Umma nake nema. Umman Asmau".

Garzali ya sake kallon Zubaida sannan yace "nan ne".

Ko jiransu batayi ba ta shige ciki tana kwalawa Asmau kira. Yassar da yake shanya ne ya fara ganinta bai san lokacin da ya saki wandon da yake kokarin dorawa a igiya a kasa ba ya nufota. Zubaida na ganinsa ta saki murmushi.
"Tabbas nan ne gidan don naga kamarku. Kai ne Yasir ko?"

Kallon rashin sani yake mata yace "a'a sunana Yassar"

Zubaida tace "hakane kaini wurin Asmau".

Hanyar falon ya nuna mata sai ya kula da Hajjo da Kawu Garzali. Har dan tsorata yayi sai yaga Hajjo tana hawaye
"Zo nan Yassar, zo naji duminka a jikina"

Ji yayi kamar mafarki yake ya fara tunanin gudu Garzali ya damko wuyan rigarsa ya hada shi da jikin Hajjo. Kuka ta fashe dashi na takaicin yadda jikanta yake nuna tsoro da fargabar ganinta har yana neman gudu. Tana rike da hannuwansa tace "kuyi hakuri Yassar. Ku yafewa wannan tsohuwar".
Chapter 22 · 0% Book details