← Book details Abinda Ake Gudu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 21 OF 74

Sashe 21

Abinda Ake Gudu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Rashida ma hawaye take yi tace "na yarda dake Asmau nasan amana ce a tsakaninmu.
Yaya Tagwai don Allah kiyi hakuri. Da zarar ta haihu zamu mayar da ita gaban iyayenta".

Ta juya wurin Asmau da take ta zubar da hawaye.
"Tashi ki koma dakinki. Bani mukullin Kemis din nasan ya kusa dawowa ya karba."

Su biyun Yaya Tagwai ta ke bi da kallo cike da mamaki." Mukullin wane kemis din ne?"

Rashida tayi shiru ita kuma Asmau ta tashi ta tafi dakinta.

"Nace mukullin wane kemis din ne?"

Rai a bace Rashida tayi mata bayanin tsarin da suke yi na zaman kemis da Sada.

Hannuwa ta shiga tafawa tana salati.
"Aahaf, ni nasan ba a banza ta barku ba. Yanzu hanyar samun naku ma tare kuke yin komai da ita. To na rantse sai ta bar gidan nan ko kunki ko kunso. Bazan koma Misau ba sai naga abinda ya turewa buzu nadi."

Asmau tana daki tana jin fadan Yaya Tagwai da muryar Rashida da Harira suna bata hakuri. Kuka take yi sosai tana cike da fargabar abinda zai faru a gaba.

Har kusan magariba Sada bai dawo ba. Dole Yaya Tagwai ta tashi ta koma gidan kanwarta saboda idan duhu yayi sosai ba gani take da kyau ba.

Gidan shiru har Sada ya dawo Rashida ta fada masa abinda ke faruwa. Ko zama baiyi ba ya wuce gidansu sai dai shima babu sa'a. Fada yasha sannan tace ya tashi ya bata wuri.

Haka suka kwana gidan kamar babu mutane. Asmau tasha kuka ga wani ciwon kai da ya kama ta.

Da safe Sada ya kirata suka kara kwantar mata da hankali yace zasu je gidan su sake bata hakuri. Har Kawu Usaini sun kira yace yana hanya zai zo a taru a bata baki. Batun zuwa kemis kuwa ranar babu ita.

Adaidaita sahun ya karbo bayan yaran sun tafi makaranta sannan suka fita shi da Rashida da Harira da ta kwana a gidan.

Ba suyi minti biyar da fita ba Yaya Tagwai ta shigo tare da kanin Sada mai suna Habu. Asmau na daki taji sallamarta. A tsorace ta fito ta bude mata kofa ta bata hanya ta wuce.

Yaya Tagwai ta soma kiran Sada, Asmau ta fada mata sun fita.

"To tunda saboda ke dama nazo ki fada min iyakar gaskiyarki. Shin cikin nan na Sada ne ko wani wanda ya sani?

Asmau ta girgiza kai tana hawaye.

"Alhamdulillahi tunda ba cikinsa bane ina so yanzu yanzu kafin su dawo ki fita ki bar gidan nan."

Gwiwa a kasa Asmau ta durkusa tana rokonta. Yaya Tagwai ta dubi Habu
"Kai da nazo da kai meye amfaninka ne? Ja min ita ka datse kofar gidan. Wallahi idan kika sake dawowa gidan nan sai na kirawo miki 'yan sanda. Haka kawai kin tsaface min yara basa jin maganar kowa sai taki. Kin gama karuwancinki zaki nemi bayin Allah ki hadasu da wahala. In dai cikin nan ba na dana bane to ki kama gabanki".

Asmau tana kuka tace "ki taimakeni don girman Allah. Bani da wurin zuwa idan na tafi."

Yaya Tagwai ta harareta "daga bishiya kika fado da zaki ce baki da wurin zuwa? Tun wuri ki koma gaban iyayenki."

Ta sake cewa Habu yaja Asmau sai ya kasa saboda tausayinta da yaji. Yaya Tagwai tace
"Idan baki fita ba zan sa iyayensu su zare hannuwansu daga kansu. Idan baki sani ba ina so kisan cewa ina da wannan ikon da kannena".

Jin haka Asmau ta juya zata shiga dakin ta debo 'yan kayanta. Yaya Tagwai ta tsare kofar dakin. "Bazan bari ki sake shiga ba bare ki kunna wani tsafin nima naji ina sonki. Fita tun kafin nayi yekuwa a unguwar nan nace ke mayya ce".

Habu ma sai da yasa baki akan ta bari ta dauko kayanta amma taki. Haka ta ja hannun Asmau daga ita sai kayan jikinta Allah Yasa da mayafi tayi waje da ita ko takalmi babu. Kuka take yi sosai amma a haka Yaya Tagwai ta ja hannunta har suka bar layin. Sai da suka yi nisa ta jefa mata naira dari biyu.
"Matsiyaciya sai ki dauka ki kara gaba wasu masu tsautsayin su dauke ki amma ba gidan 'ya'yana ba. Allah Ya isa idan kika dawo."

Kukan Asmau ba karamin tausayi ya bawa Habu ba amma yana kallo tayi gaba Yaya Tagwai ta kama hannunsa suka koma gidan Sada.

*****
A gidansu Sada ne Baaba Ta Annabi ta fada musu tun dazu Yaya Tagwai ta tafi gidan nasu. Suna jin haka suka kama hanyar gida hankali a tashe. Suka yi rashin sa'a titin da ya biyo wata mota ta lalace ta hada uban goslow.

Kusan tsalle Rashida tayi da suka iso gida ta fito daga dan sahun. Tana shiga ta tarar da Yaya Tagwai tana yin boli boli da kayan Asmau. Kuka ta saka tana tambayarta ina take Habu yace ta tafi.

Sada na jin haka cikin fada ya tambaye shi hanyar da tabi ya kwatanta masa. Tare suka bi hanyar ko zasuyi sa'ar ganinta. Sai dai sunfi awa biyu suna nema daga baya wani yace ta shiga wata bus amma bai san inda bus din tayi ba.

Da suka dawo gida Rashida ya gani a tsakar gidan ta rungume kayan jariran da Asmau take tarawa tana ta kuka. Yaya Tagwai tace "idan kin gaji kya yi shiru. Irin wannan kuka da kike yi sannan ace ba aikin asiri bane."

Ayatul Kursiyyu ta shiga karantawa tana tofawa Rashida a ka wai maganin sihiri. Sada ya dagata ya shigar da ita daki tana ta kuka. Habu da Harira kuwa sai kallo. Yaya Tagwai ko a jikinta. Tasan komai daren dadewa zasuyi mata godiya saboda ta rabasu da masifa.

*****
Yaya Babba ke bacci harda minshari Zubaida ta samu ta lallaba da kyar ta fito daga gidan.

A iya watannin da tayi duk shegantakar karuwanci 'yar tsohuwar nan ta koya mata. Tun tana nuna bata so har ta hakura tana biye mata saboda a rage matakan tsaron da aka saka mata. Bata taba yarda wani yayi amfani da ita ba. Tace sai ta koma gidan Uwargida. Yaya Babba bata damu ba ita dai aikin da aka sakata tayi.

Tunda tazo gidan sai yau ta samu damar fita. Kullum tana tunanin Asmau. Bata sani ba ko ta haihu yanzu.

Gidan Uwargida ta tafi da niyyar idan Asmau tana nan su gudu tare. Daga bakin kofa ta hadu da wata cikin matan gidan.

"Zuby kin dawo?" Ta fada tana kallon irin shigar Zubaidan da yadda ta kara cikowa.

Zubaida ta rage murya
"Shiga ki kirawo min Asmau bakuwar nan. Don Allah kiyi sauri ga wannan kada ki fadawa Mama kin ganni." Dari biyar ta bawa matar ta karba sannan tace "wannan bakuwar baki dade da tafiya ba ta gudu. Har an sami wasu bakin biyu bayan tafiyarta."

Zubaida tayi wani murmushi cike da jindadi."Alhamdulillah nasan taji shawarata ta koma gidansu."

Daga nan ta dauki jakar kayanta ta juya ita ma. Matar ta biyota tana tambayar ina zata je Zubaida tayi gaba ko kulata bata yi ba.

Daga nan bata zame ko ina ba sai tasha ta nemi motar Kano. Basu dade ba motar ta cika suka hau titi. Indai bata manta ba Asmau tace sunan umguwarsu Hotoro layin kwamishina Adamu. Gidansu zata nema don tasan in Allah Yaso yadda Asmau ke bata labarin Umma zasu riketa har ta sami mijin aure. Ta dan yi murmushi "ko me Asmau ta haifa" ko meye ma zata tayata raino tunda dai taji shawararta ta koma gida. Allah Yasa dai ta gane gidan.
ABINDA AKE GUDU🙆🏽24

Batul Mamman💖

Zuciyar Asmau banda zafi babu abinda take yi. Ji take kamar ta haye tsakiyar titi mota tayi gaba da ita kowa ya huta. A tunaninta babu sauran mai kaunarta a duniya. Tana wannan jan kafar ne taji kwandastan wata hayis yace Hajiya zaki hau? Kai ta gyada tare da shiga motar da bata san inda suka nufa ba.

Sunyi tafiya mai dan nisa wasu na sauka wasu na hawa kwandastan nan yana ta tambayarta kudin mota hankalinta baya wurin saboda kukan da take yi. Wata mata ce a kusa da ita ta dan taba ta sai ta kula da yadda kafafun Asmau suka yi futu-futu ko takalmi bata dashi. A tsorace matar ta ja jikinta gefe ta karewa kodaddun kayan jikinta kallo. Daga murya tayi iya karfinta tace
"mahaukaciya ce"

Nan da nan hankalin jama'a ya dawo kanta aka fara cewa za'a sauka. Dreban hayis din ya hau yiwa kwandasta fadan ya dauko musu mahaukaciya. Tsayawa yayi suka janyo hannunta aka fitar da ita daga motar. Bakincikin da take ji ya hanata magana. Wai yau ita ake yiwa kallon mahaukaciya.

Tana kallo motar tayi gaba sannan ta kula da cewa inda take ya danyi wajen gari babu gidaje sosai. Ga wani irin ciwon baya da mara da ya taso mata lokaci guda. Runtse idonta kawai tayi tana tafiya zafin kwalta yana kona mata kafa sai ji tayi an taka burki da karfi motar tayi wata irin kara.

A razane ta bude idonta. Wata mota ta gani mai kyau ashe da tana tafiya ta dan hau titi bata sani ba. 'Yan samari biyu ne suka fito suna ta zaginta ta uwa ta uba. Dukkansu bata jin akwai wanda ya shekara ashirin sai tsayin kafa kawai. Kayan jikinsu sun nuna yaran sun fito daga gidan arziki sai dai daga yanayin maganarsu ta kula a buge suke.

Wanda ya danfi tsahon yayo kanta kamar zai doketa dayan yayi saurin rike masa hannu
"Haba Annur, duba da kyau mahaukaciya ce. Tunda Allah Yasa bamu tabata ba kawai zo mu ware".

Mai suna Annur ya ja tsaki "da ka barni na mareta. Haka kawai zata janyo mana makara a wurin party din. Sai an gama zabe fine chicks din"

Ciwo ne ya sake kwasarta tayi kasa tana rike baya. Jajayen idanunta da suka rine don kuka ta daga tana kallonsu tace
"don Allah ku taimaka min"

Wanda ya hana a mareta yace "kai Annur it seems matar nan haihuwa zata yi".

"Gaddafi bazan tsaya a wurin nan ba. Kaima kasan yanzu haka an fara nemanmu a gida. Allah Ya kawo wani amma ba mu ba. "
Chapter 21 · 0% Book details