Sashe 38
Abinda Ake Gudu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wani abu ne ya tokarewa Col Ishaq makoshi yaki sauka kasa. Wai ya taya shi addua. A zuciyarsa yace (Allah Yasa kada ta taba yi maka soyayya irin ta mace da namiji.). Abu daya ke yi masa yawo a ka shine kada Asmau ta juya masa baya. Wannan Qasim din wani sanyi ne gareshi mai sa mutum yaji dadin mu'amala dashi.
A fili kuwa murmushin yake yayi "ah to bari naje naga Amatullah sai na tafi. Dama ita nazo gani kewarta ta isheni" daga nan gefe ya matsa ya kira Yassar. Bai dade ba ya fito ya shigar dashi ciki. Ransa a bace da ya hango Asmau da Qasim yana taya Jikamshi kishi.
Bayan sun shiga ciki Qasim yayi ta yabon saukin kai irin na Col. Ishaq "kamar ba babban soja ba, ji yadda yake jana kamar ya dade da sanina"
"Uhmm" kawai Asmau tace a sanyaye.
"Asmau wace shawara kika yanke mana?"
Ta dago kai a hankali "Yaya Qasim ni dai da mun bar maganar nan"
"Kinga Asmau duk abinda kike gudu baki da tabbas a kansa. Yana iya faruwa ko kuma kiga bai faru ba. Haka nan ma masu aure na fuskantar matsaloli musamman mata daga dangin miji. Bance komai zai tafi mana daidai ba amma nayi alkawarin tsaya miki har karshen rayuwata"
Tausayinsa ta kara ji. Banda tsoronta na aure ko kadan bata jin son Qasim sai tausayinsa saboda yadda yake mata.
"Ka dan kara min lokaci, ban samu nayi maganar da Umma ba"
"To babu komai, shi garaje ai bashi da alkhairi. Duk yadda kuka yi ki sanar dani. Sannan zan kiraki idan na koma gida in sha Allah. Akwai keke da na siyowa Amatullah bari na dauko yana bayan mota"
"Nagode"
"Wai kin gode, mutum da 'yarsa? Shiga ciki bari na dauko"
Da sauri sauri tayi shige.
*****
Daga kallon kofa sai agogo Col. Ishaq yake yi tunda ya zauna hankalinsa baya tare dashi. Ji yake kamar ya koma wajen ya hana zancen. Hajjo ce take kokarin janshi da hira sai Amatullah tana bashi labarin Wushishi. Yassar kuwa kamar yaje ya dauko Asmau yake ji. Da ta shigo Jikamshi ya kafe ta yayi da ido ta kasa kallon inda yake kawai sai ta shige dakin Umma inda suke ta hada kaya ita da Ainau zata koma gidanta washegari.
Qasim ya shigo da keke mai kyau na yara. Amatullah sai tsalle da murna. Tana ta cewa ta gode kamar yadda Umminta ta koya mata. Hajjo ta dubi Col Ishaq "da kai da Qasim kuna shagwaba yarinyar nan da yawa. To ni ina nawa keken?"
Suna dariya Yassar yace "kada ki damu ni zan siyo miki irin mai katuwar tayar gaban nan na zamaninku"
Umma ta fito tayi godiya sannan Qasim yayi musu sallama ya fita. Sai da suka ji tashin motarsa Col Ishaq shima ya tashi yace da Amatullah ta kira Umminta su gaisa. Umma ta jinjina kai tunda ya shigo dazu ta kula ransa a bace yake yana dannewa. Gaskiya akwai matsala nan gaba sai dai fatan Allah Ya zabawa Asmau mafi alkhairi cikinsu.
*****
Tana kwance akan gado har wani zazzabi ke neman kamata saboda tunani Amatullah ta fada mata sakon babanta. Ta dan zaro ido "Baba Qasim ya tafi?"
"Eh ya tafi kuma ya kawo min keke mai kyau"
"Kinyi masa godiya ko"
"Nayi masa Ummi"
"Muje kiyi wasa kafin lokacin bacci yayi"
******
Baya falo da ta fito sai ta saka takalmi ta fita waje.
Tsaye yake a jingine da motarsa yana danna waya ta hasko fuskarsa. Kamar mai taka kwai haka Asmau ta karasa gabansa.
"Ina wuni"
Muryarta tana masa dadi, wani irin sonta yake kara ji yana shigarsa. Sai dai kishi yasa ya kasa amsa gaisuwar.
"Asmau wallahi ina da kishi sosai. Kada ki bari na kara ganinki a yanayi irin na yau. I can't take it"
Ta kara sunkuyar da kai da jin furucinsa.
"Kinga ki dago kanki ki kalleni magana zamuyi"
Mayafinta tasa ta rufe fuskarta gabadaya. kunyarsa take ji.
"Kina so na bude fuskar ne da kaina?"
Ta girgiza kai da sauri
"To ki bude da kanki kafin hakurina ya kare"
Hannu tasa ta bude fuskar tare da dagowa a hankali. Fuskarshi ta bata tsoro saboda babu digon wasa
"Jiranki da nayi a falo dazu yana cikin lokutan da bazan manta ba a rayuwata. Zuciyata bazata juri ki hadani da wani ba"
"Don Allah kayi hakuri" tace idonta na kawo ruwa.
"Ki fada min ni dashi waye ya fara nuna miki so"
"Kai ne" ta amsa masa jiki a sanyaye. Bata son bata masa rai ko kadan saboda yadda take sonsa.
"Alhamdulillah, da ya rigani zan ci girma na bar masa ke don bazan iya tarayya da wani akanki ba. Ina da kishi mai zafi wanda ban taba sanin kaina dashi ba sai yau. Amma tunda na riga shi sai dai shi ya hakura. Ina sonki kuma bana jin zan iya hakura dake."
Shiru tayi tana kallon kasa. Tun bayan rasuwar Abubakar ta cire rai da sake samun soyayyar wani da namiji sai gashi yanzu har mutum biyu ne suke sonta. Mutum biyun da take matukar son daya, dayan kuma take ganin girmansa. Duk su biyun kuma tana jin kunyar nuna musu bata sonsu a yadda take ganin ba karamin darajata suka yi ba da suke sonta da aure.
Col Ishaq yana kallo yadda ta shiga rudani. Kamar yadda ya fada mata da ace Qasim ya rigashi to zai hakura ne indai ya tabbatar da gaske yake sonta. A yanzu kuwa yana da yakinin shi Asmau take so kuma ya riga saboda haka yana nan daram sai yaga abinda ya turewa buzu nadi. Shi kishin kara masa so da kaunarta yayi ma.
"Kamar kwana nawa kike bukata na baki ki sallame shi"
Ji karfin hali ta ayyana a ranta. A fili tace "bangane ba"
"Kin gane, karin bayani kike nema dai. Bansan iya matakin da kuka kai ba ke dashi shiyasa zan baki lokaci kuyi rabuwar arziki. Shima don na fahimci kamar yana da halin kirki ne."
"Ya kake so nayi? Kaima na fada maka babu zancen aure a raina shima kuma hakan na sanar dashi"
"Idan babu zancen aure a ranki kin tanadi yadda zakiyi da soyayyata wadda yanzu ma na fara nuna miki ita. Idan bakiyi wasa ba nan gaba kadan saboda yadda zan rinka yakin neman sonki da kanki zaki ce gobe a daura mana aure"
Dariya tayi, shi a komai sai ya saka wasa tace"kai Jikamshi"
"Allah kuwa Asmau" shima ya mayar mata da murmushi.
"Ni da ban taba cewa ina sonka ba. Amma kana da confidence a kaina"
Kansa ya shafa yana kallonta. Baya gajiya da kallon Asmau ko kadan.
"Asmau kina sona. Nima ina sonki. So bana bukatar sai kinyi ta maimaitawa da baki. Akwai lokacin da zaki rinka fada da kanki"
Ita kam Jikamshi yana bata mamaki. Sai ya fadi magana ya kuma dake abinsa.
"Ki shiga ciki bana son kina shakar kurar nan. Kada ki manta da abinda nace. Idan kin sallame shi zan turo iyayena a fara maganar aurenmu"
Magana taso yi ya sanya yatsansa akan lebensa alamun tayi shiru.
"Idan rokona zakiyi akan Qasim kada ki bata bakinki. Nan da sati biyu idan baki sanar dani yadda kuka yi ba ki zaki ga magabatana sunzo. Ki kula min da kanki da princess dina. Yau duk kin rikita min lissafi na kasa bata kulawa yadda ya kamata"
"Ni babu ruwana."
"Harda tsakinki. Sai da safe"
"Allah Ya bamu alkhairi"
Tana kallo ya shiga mota ya zauna sannan itama ta juya.
"Matar Jikamshi"
Cak ta tsaya amma bata juyo ba sai murmushi da take yi.
"I love you"
Hannuwa tasa ta rufe fuskarta cike da kunya tayi hanyar gida a kunyace.
******
Daurewa kawai Col. Ishaq yayi har suka karashe hirar cikin wasa. Da ya rage shi kadai yana tuki tunani yake kada iyayen Asmau su bawa Qasim ita saboda sunfi sanin shi sannan abokin Abubakar ne. Saurin kawar da tunanin yayi daga ransa. A zatonsa ya gama soyayya akan Badar sai gashi lokaci guda Asmau ta wargaza masa tunani.
Yana zuwa gida dakin Hajiya ya wuce. Bayan sun dan taba hira ya sanar da ita zancen Asmau. Tayi mamaki sosai don bata taba hasko hakan ba. Bilkisu da tayi niyar fada mata kuma ranar tun a hanya yaja mata kunne. Shiru tayi na dan lokaci kafi tace
"Kai yanzu kana tunanin sai ka aureta ne kawai zaka iya kyautata rayuwarta da ta Safina?"
"Hajiya nifa ba don in kyautata musu kawai nake son aurenta ba. Ina sonta ne tsakani da Allah"
Ko kunyar yace yana son mace baiyi a gabanta. Tayi iya kokarinta wurin nuna masa kunyar dan fari amma duk baya biye mata. Yanzu me ya kawo zancen soyayya a gabanta.
"Bazan zama irin iyaye marasa karbar kaddara ba musamman da na san komai game da ita. Kai ba yaro bane da zan ce baka san abinda ya kamata ba. Amma ka jira nayi shawara da 'yan uwana dana mahaifinka. Kasan zancen duniya baya buya. Gara su sani tun kafin ayi auren sabo gudun gutsiri tsoma"
Murmushi yayi ya nuna mata tsantsar farincikinsa. "Hajiya nagode da kika fahimce ni. Ina fata ko sun nuna rashin amincewa don Allah kada ki hanani aurenta don wallahi bakiji yadda nake jinta a zuciyata ba"
Haj Lubabatu ta kawar da kanta gefe a kunyace. Ya cigaba da cewa "idan tayi murmushi ji nake kamar...."
"Kai tashi ka bani wuri zancen ya isa haka" ta fada amma kafin ya tashi ita tayi gaba. Dariya yayi dama tsokanarta yaso yi.
Sai da ya gama shirin bacci ya dauko wayarsa zai kira Asmau yaga missed calls da bakuwar number har uku. Ya kira numbar ga mamakinsa sai yaji muryar Qasim. Sun sake gaisawa yace ya karbi numbarsa a wurin Yassar ne don su rinka gaisawa. Hira suka dan taba cikin mutunta juna. Suna yin sallama ya kira Asmau.
Ta dauka kafin tayi magana yace cikin muryar shagwaba "Matar Jikamshi kin cuce ni"
Gyara zama tayi a dan tsorace." Me nayi kuma"?
"Wannan dan sandan saurayin naki wallahi yana da mutumci. I feel guilty nace ki rabu dashi gashi har yana min waya."
Ta dan murmusa "to ko na barshi kai ka janye"
A fili kuwa murmushin yake yayi "ah to bari naje naga Amatullah sai na tafi. Dama ita nazo gani kewarta ta isheni" daga nan gefe ya matsa ya kira Yassar. Bai dade ba ya fito ya shigar dashi ciki. Ransa a bace da ya hango Asmau da Qasim yana taya Jikamshi kishi.
Bayan sun shiga ciki Qasim yayi ta yabon saukin kai irin na Col. Ishaq "kamar ba babban soja ba, ji yadda yake jana kamar ya dade da sanina"
"Uhmm" kawai Asmau tace a sanyaye.
"Asmau wace shawara kika yanke mana?"
Ta dago kai a hankali "Yaya Qasim ni dai da mun bar maganar nan"
"Kinga Asmau duk abinda kike gudu baki da tabbas a kansa. Yana iya faruwa ko kuma kiga bai faru ba. Haka nan ma masu aure na fuskantar matsaloli musamman mata daga dangin miji. Bance komai zai tafi mana daidai ba amma nayi alkawarin tsaya miki har karshen rayuwata"
Tausayinsa ta kara ji. Banda tsoronta na aure ko kadan bata jin son Qasim sai tausayinsa saboda yadda yake mata.
"Ka dan kara min lokaci, ban samu nayi maganar da Umma ba"
"To babu komai, shi garaje ai bashi da alkhairi. Duk yadda kuka yi ki sanar dani. Sannan zan kiraki idan na koma gida in sha Allah. Akwai keke da na siyowa Amatullah bari na dauko yana bayan mota"
"Nagode"
"Wai kin gode, mutum da 'yarsa? Shiga ciki bari na dauko"
Da sauri sauri tayi shige.
*****
Daga kallon kofa sai agogo Col. Ishaq yake yi tunda ya zauna hankalinsa baya tare dashi. Ji yake kamar ya koma wajen ya hana zancen. Hajjo ce take kokarin janshi da hira sai Amatullah tana bashi labarin Wushishi. Yassar kuwa kamar yaje ya dauko Asmau yake ji. Da ta shigo Jikamshi ya kafe ta yayi da ido ta kasa kallon inda yake kawai sai ta shige dakin Umma inda suke ta hada kaya ita da Ainau zata koma gidanta washegari.
Qasim ya shigo da keke mai kyau na yara. Amatullah sai tsalle da murna. Tana ta cewa ta gode kamar yadda Umminta ta koya mata. Hajjo ta dubi Col Ishaq "da kai da Qasim kuna shagwaba yarinyar nan da yawa. To ni ina nawa keken?"
Suna dariya Yassar yace "kada ki damu ni zan siyo miki irin mai katuwar tayar gaban nan na zamaninku"
Umma ta fito tayi godiya sannan Qasim yayi musu sallama ya fita. Sai da suka ji tashin motarsa Col Ishaq shima ya tashi yace da Amatullah ta kira Umminta su gaisa. Umma ta jinjina kai tunda ya shigo dazu ta kula ransa a bace yake yana dannewa. Gaskiya akwai matsala nan gaba sai dai fatan Allah Ya zabawa Asmau mafi alkhairi cikinsu.
*****
Tana kwance akan gado har wani zazzabi ke neman kamata saboda tunani Amatullah ta fada mata sakon babanta. Ta dan zaro ido "Baba Qasim ya tafi?"
"Eh ya tafi kuma ya kawo min keke mai kyau"
"Kinyi masa godiya ko"
"Nayi masa Ummi"
"Muje kiyi wasa kafin lokacin bacci yayi"
******
Baya falo da ta fito sai ta saka takalmi ta fita waje.
Tsaye yake a jingine da motarsa yana danna waya ta hasko fuskarsa. Kamar mai taka kwai haka Asmau ta karasa gabansa.
"Ina wuni"
Muryarta tana masa dadi, wani irin sonta yake kara ji yana shigarsa. Sai dai kishi yasa ya kasa amsa gaisuwar.
"Asmau wallahi ina da kishi sosai. Kada ki bari na kara ganinki a yanayi irin na yau. I can't take it"
Ta kara sunkuyar da kai da jin furucinsa.
"Kinga ki dago kanki ki kalleni magana zamuyi"
Mayafinta tasa ta rufe fuskarta gabadaya. kunyarsa take ji.
"Kina so na bude fuskar ne da kaina?"
Ta girgiza kai da sauri
"To ki bude da kanki kafin hakurina ya kare"
Hannu tasa ta bude fuskar tare da dagowa a hankali. Fuskarshi ta bata tsoro saboda babu digon wasa
"Jiranki da nayi a falo dazu yana cikin lokutan da bazan manta ba a rayuwata. Zuciyata bazata juri ki hadani da wani ba"
"Don Allah kayi hakuri" tace idonta na kawo ruwa.
"Ki fada min ni dashi waye ya fara nuna miki so"
"Kai ne" ta amsa masa jiki a sanyaye. Bata son bata masa rai ko kadan saboda yadda take sonsa.
"Alhamdulillah, da ya rigani zan ci girma na bar masa ke don bazan iya tarayya da wani akanki ba. Ina da kishi mai zafi wanda ban taba sanin kaina dashi ba sai yau. Amma tunda na riga shi sai dai shi ya hakura. Ina sonki kuma bana jin zan iya hakura dake."
Shiru tayi tana kallon kasa. Tun bayan rasuwar Abubakar ta cire rai da sake samun soyayyar wani da namiji sai gashi yanzu har mutum biyu ne suke sonta. Mutum biyun da take matukar son daya, dayan kuma take ganin girmansa. Duk su biyun kuma tana jin kunyar nuna musu bata sonsu a yadda take ganin ba karamin darajata suka yi ba da suke sonta da aure.
Col Ishaq yana kallo yadda ta shiga rudani. Kamar yadda ya fada mata da ace Qasim ya rigashi to zai hakura ne indai ya tabbatar da gaske yake sonta. A yanzu kuwa yana da yakinin shi Asmau take so kuma ya riga saboda haka yana nan daram sai yaga abinda ya turewa buzu nadi. Shi kishin kara masa so da kaunarta yayi ma.
"Kamar kwana nawa kike bukata na baki ki sallame shi"
Ji karfin hali ta ayyana a ranta. A fili tace "bangane ba"
"Kin gane, karin bayani kike nema dai. Bansan iya matakin da kuka kai ba ke dashi shiyasa zan baki lokaci kuyi rabuwar arziki. Shima don na fahimci kamar yana da halin kirki ne."
"Ya kake so nayi? Kaima na fada maka babu zancen aure a raina shima kuma hakan na sanar dashi"
"Idan babu zancen aure a ranki kin tanadi yadda zakiyi da soyayyata wadda yanzu ma na fara nuna miki ita. Idan bakiyi wasa ba nan gaba kadan saboda yadda zan rinka yakin neman sonki da kanki zaki ce gobe a daura mana aure"
Dariya tayi, shi a komai sai ya saka wasa tace"kai Jikamshi"
"Allah kuwa Asmau" shima ya mayar mata da murmushi.
"Ni da ban taba cewa ina sonka ba. Amma kana da confidence a kaina"
Kansa ya shafa yana kallonta. Baya gajiya da kallon Asmau ko kadan.
"Asmau kina sona. Nima ina sonki. So bana bukatar sai kinyi ta maimaitawa da baki. Akwai lokacin da zaki rinka fada da kanki"
Ita kam Jikamshi yana bata mamaki. Sai ya fadi magana ya kuma dake abinsa.
"Ki shiga ciki bana son kina shakar kurar nan. Kada ki manta da abinda nace. Idan kin sallame shi zan turo iyayena a fara maganar aurenmu"
Magana taso yi ya sanya yatsansa akan lebensa alamun tayi shiru.
"Idan rokona zakiyi akan Qasim kada ki bata bakinki. Nan da sati biyu idan baki sanar dani yadda kuka yi ba ki zaki ga magabatana sunzo. Ki kula min da kanki da princess dina. Yau duk kin rikita min lissafi na kasa bata kulawa yadda ya kamata"
"Ni babu ruwana."
"Harda tsakinki. Sai da safe"
"Allah Ya bamu alkhairi"
Tana kallo ya shiga mota ya zauna sannan itama ta juya.
"Matar Jikamshi"
Cak ta tsaya amma bata juyo ba sai murmushi da take yi.
"I love you"
Hannuwa tasa ta rufe fuskarta cike da kunya tayi hanyar gida a kunyace.
******
Daurewa kawai Col. Ishaq yayi har suka karashe hirar cikin wasa. Da ya rage shi kadai yana tuki tunani yake kada iyayen Asmau su bawa Qasim ita saboda sunfi sanin shi sannan abokin Abubakar ne. Saurin kawar da tunanin yayi daga ransa. A zatonsa ya gama soyayya akan Badar sai gashi lokaci guda Asmau ta wargaza masa tunani.
Yana zuwa gida dakin Hajiya ya wuce. Bayan sun dan taba hira ya sanar da ita zancen Asmau. Tayi mamaki sosai don bata taba hasko hakan ba. Bilkisu da tayi niyar fada mata kuma ranar tun a hanya yaja mata kunne. Shiru tayi na dan lokaci kafi tace
"Kai yanzu kana tunanin sai ka aureta ne kawai zaka iya kyautata rayuwarta da ta Safina?"
"Hajiya nifa ba don in kyautata musu kawai nake son aurenta ba. Ina sonta ne tsakani da Allah"
Ko kunyar yace yana son mace baiyi a gabanta. Tayi iya kokarinta wurin nuna masa kunyar dan fari amma duk baya biye mata. Yanzu me ya kawo zancen soyayya a gabanta.
"Bazan zama irin iyaye marasa karbar kaddara ba musamman da na san komai game da ita. Kai ba yaro bane da zan ce baka san abinda ya kamata ba. Amma ka jira nayi shawara da 'yan uwana dana mahaifinka. Kasan zancen duniya baya buya. Gara su sani tun kafin ayi auren sabo gudun gutsiri tsoma"
Murmushi yayi ya nuna mata tsantsar farincikinsa. "Hajiya nagode da kika fahimce ni. Ina fata ko sun nuna rashin amincewa don Allah kada ki hanani aurenta don wallahi bakiji yadda nake jinta a zuciyata ba"
Haj Lubabatu ta kawar da kanta gefe a kunyace. Ya cigaba da cewa "idan tayi murmushi ji nake kamar...."
"Kai tashi ka bani wuri zancen ya isa haka" ta fada amma kafin ya tashi ita tayi gaba. Dariya yayi dama tsokanarta yaso yi.
Sai da ya gama shirin bacci ya dauko wayarsa zai kira Asmau yaga missed calls da bakuwar number har uku. Ya kira numbar ga mamakinsa sai yaji muryar Qasim. Sun sake gaisawa yace ya karbi numbarsa a wurin Yassar ne don su rinka gaisawa. Hira suka dan taba cikin mutunta juna. Suna yin sallama ya kira Asmau.
Ta dauka kafin tayi magana yace cikin muryar shagwaba "Matar Jikamshi kin cuce ni"
Gyara zama tayi a dan tsorace." Me nayi kuma"?
"Wannan dan sandan saurayin naki wallahi yana da mutumci. I feel guilty nace ki rabu dashi gashi har yana min waya."
Ta dan murmusa "to ko na barshi kai ka janye"