Sashe 59
Abinda Ake Gudu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ranar Jumaa gidan Umma tun safe ya cika da jama'a duk da a katin an rubuta ba a gidan za'ayi kamun ba. Mutane sun rasa daga inda wasu ma suke zuwa. Abin mamaki sai ga Sagira matar Rabe da 'ya'yansu matan. Duk ta yamushe rayuwar kauye babu dadi. Umma batayi zaton zasu zo ba ganin da Asmau ta dawo an aika musu. Hajjo ce ma ta hana Asmaun zuwa Dakasoyen ta gaishe da Kawu Raben saboda shima ya dauke musu kafa. Gashi dai shine da laifi amma yafi kowa fushi.
Su Anti Lami da Yaya Abu duk sun iso da safe da yaransu har na gidan miji. Abu yayi kyau ko babu komai dai dangi ba'a canza su.
Lalle aka zauna yi mata ja da baki wanda aka bata lokaci wurin yinsa. Tasha zama kuwa don 'yan uwanta sun dage bazata cire da wuri ba sai ya fito sosai yadda za'a jima ana cin amarci.
Ana idar da sallar jumaa aka fara wanka don gidan Umma, Mama da na Jafar duk babu masaka tsinke. Itama Asmau kafin a kira la'asar tayi wankanta mai kwalliya Najah tazo ya fara aikinta. Fuska ta dauka don Naja ba daga nan ba. Kwalliyar ta nutsuwa ce ba'ayi mugun fentin nan na foundation ba da fuskar mutum take canzawa gabadayanta. Ana gamawa ta tashi tayi sallah aka sake gyarawa sannan ta saka kaya. Idan ka ganta a lokacin bazaka ce Asmau mai wankin bandaki bace a asibitin Jos. Tayi kyau ba kadan ba. A lokacin yawancin matan dake gidan sun tafi venue din. Yaya Abu ce ta kira Zubaida akan lallai su taho da amarya da wuri mutane sun soma cika a wurin. Ita har mamaki take yi wasu daga ina suka zo.
Wata mota ango Ishaq ya turo mai kyau ta daukar amarya zuwa wurin biki. Da suka isa ita da Walida da Zulaiha ne a motar. Safiyya tazo tace ta zauna domin ango yana hanya sai ya iso zata fito. Ta saki wani murmushin jindadi bayan Safiyya ta tafi. Zulaiha ta ce
"Hmm Asmau amare na dan kuka rana irin ta yau sai fara'a kike yi."
Allah Yasa dreban motar ya fita sai AC da aka ware musu. Walida tace "baki ga komai ba ita da Col. Ishaq nasu salon daban yake"
Asmau tayi fari da ido kawai tana murmushi. Motar tasu mai tint ce ta waje ba'a ganinsu sun jiyo kida daga wurin bikin yana tashi ga mata suna ta shige da fice. Wurin cike yake da sojoji masu gadi. Da farko ma taron ba'ayi niyar yi da maza ba. Sai Mami ta roka akan cewa ango zai zo da abokansa suyi hoto da amarya ya tafi. Shima da kyar ya yarda da zuwan. Shemau ce ta fada mata kalar kayan da amarya zata saka suka yi gaggawar nemawa ango wanda zai dace.
Bugu zuciyar Asmau ne ya karu da ta hango motar Jikamshinta. Wurin motoci bakwai ne suka shigo tare. Wai bikin da akace babu maza kenan. 'Yan kashe kwarkwarar ido da abokan arziki duk sun biyo shi.
Saitin motar da take Dahiru da ya tuko motarsa ya daidaita tasu yadda zasu fito tare. Ya hakimce a baya yana waya. Sai da ya gama ya fito ko'ina ya dauki kamshi.
Kofar inda take zaune yaje ya bude suka hada ido. Babu karya ya yarda yana son Matar Jikamshi. Duk abinda kake so kuwa dole kaga kyaunsa. Indai haka ne Jikamshi da Asmau sunyi kyau a yau ranar kamunsu. Wani hadadden lace ne peach a jikinta da ta samu tela yayi mata dinki na gani a fada. Doguwar riga ce amma tayi kyau sosai mai dogon hannu. Dankwalin rigar aka hada da wani yadi mai kyalkyali purple mara turowa akayi mata dauri. Sai tasa mayafi irin yadin aka makale mata shi daga tsakiyar daurin nata da pin. Takalminta mai tsini da jaka duk kalar mayafin ne. Ango ma shaddarsa irin mayafin nata ce amma fa ba mai kyalli ba. Ga hula har wani dan karkacewa tayi. Asmau tana gama fitowa aka fara daukar hotuna kamar me. Safiyya da Shemau ne masu tsari suka jera su MC din taro S.Kilishi ita ce ta sanar da shigowar ango da amarya. Suka taho suna taku daidai. Wuri ya kaure da sowa.
_Qamshi qamshi yana tashi, 'yan mata zamu kamun amarya_
_Yaune muke shirin kamu...amarya_
_Asmau amarya zo gamu...amarya_
_Ki hakuri da zancenmu, kinsan aure yana kanmu_
Kafin mai wakar ta karaso gaban ango da amarya tuni 'yan mata sun fito ana ta rausayawa. Jajimaji kenan, idan ta bude baki ko Sangandali sai dai taja baya. Haka ta cigaba da waka har amarya da ango suka zauna.
Bayan Hajiya YBK ta bude taro da addua aka shiga biki da gaske. Su Bilkisu da tawagar gidan Hajiya Lubabatu da 'yan Jikamshi ankonsu iri daya ne da nasu Ainau. Ga su Amatullah yau anyi kwalliya itama ta fito sosai. Yaran su Shemau da nasu Sadiya 'yan uwan Abubakar kowa fa yayi kyau.
An bukaci dangin ango su fito fesawa amarya turare sai gasu mata biyar ne harda Mami kowacce da tsadadden turare a hannunta suka zo a rinka fesawa. Biki yayi biki mata sun sha rawa. A cikin taron mata 'yan taya ango da amarya murna sun gwangwaje. Saboda yawansu ba sunan kowa zaka iya kamawa ba. Akwai su Maman Afrah, Tash, Jatma, Zahida, Mrs G, Sadiya Jegal, Ibtihal, Shukriya, Ummu Rauda, Maman Sadiq, Ummu Aslam, Mrs Ambursa, Hauwa Ag, Mum Little, Farha, Jammu, Mardiya, Shafa, Ruqayya, Tafeesu, Ummi BK, Didi, Mjay, Zahra BB, Biebie Isah, Temseey, Khadija Candy.....(wai abin da yawa ni mai rubutu naji hannuna zai tsinke nace wallahi sauran ma duk ina sonku har raina).
Taro kam ya kayatar. Anci an sha an kuma rausaya. Ana cikin daukar hotuna ne Mama Yalwa tazo zasu dauka ita da Asmau da ango. Suna hada ido da Asmau suka tuna abu daya suka fara kuka lokaci guda. Duk wanda yasan wadannan matan yasan kukan me suke yi. Allah Ya jikan Abubakar, mutuwarsa ce tasa har aka zo rana irin wannan. Suna yi ana tayasu har su Umma. Suwaiba karamar kanwarsa ce ta iya daurewa tana basu baki. Col. Ishaq duk kishi irin nasa ya dauke kai a yau. Abubakar wani bangare ne na rayuwar Asmau da bazai gogu ba.
Haka aka kare taron kowa ya tafi gida cikin farinciki da annashuwa. 'Yan gulma basu sami abin fada ba sai san barka domin taro ya burge kowa.
*****
Washegari sai shabiyun rana zaa daura aure. Asmau tun dare ta kasa baccin kirki. Yaushe zata manta ranar aurenta na farko da ango ya rasu. Ji tayi gabadaya bata da kuzari har gari ya waye.
Col. Ishaq kuwa jin kansa yake kamar anyi masa wani albishir mai kyau. Farar shadda ya saka harda babbar riga. Anyi mata aiki da zare ruwan goro saboda haka hularsa da takalmi harda agogon hannunsa ruwan goron ne. Masallacin Hotoro ya dauki jama'a wadanda suke son shaida wannan babbar rana. Su Jafar da Yassar suna kan gaba, ga Kawu Garzali da wani abin mamaki Kawu Rabe yazo yana ta ra6e ra6e. Bisa amincewar Hajjo da sauran 'yan uwansu Alh Adamu Matawalle shine waliyin amarya. ASP Qasim ma gayya guda yazo da ita daga abokan aiki zuwa makusantansa a Shanono. Ga su Sada suma ba'a barsu a baya ba.
Ango sai faraa yake yana gaisawa da jama'a. Har hoto suka yi da Qasim suka gaisa a mutunce. Shabiyu nayi Liman ya bukaci wakilin angon da waliyin amarya. An daura auren Col. Ishaq Muhammad Jikamshi da Asmau Shu'aib Yahya akan sadaki dubu sittin.
*****
Asmau na zaune kowa yayi wanka ana ta shirin tafiya gidan Umma inda zasu zauna saboda baki masu son ganin amarya. Tamkar wadda aka zarewa laka haka take jin jikinta. Ga faduwar gaba da ta kwana dashi. Tana kwance text ya shigo wayarta ta dauka a firgice. Kalma daya ta gani daga Jikamshi wadda ta saka ta kuka sosai.
*Alhamdulillah.*
Su Sabira suka zuba mata ido har dakin ya fara cika da su Ainau da Zulaiha suna ta tambayarta me aka yi mata. Shemau rai a bace tace "ku kyaleta tayi kukan nan. Tun daren jiya take neman yinsa. Ni nayi mamaki ma da kika jira sai yanzu. Ace mutum bashi da sana'a sai ta zubar da hawaye."
Tana kukan tace "Anti Shemau an daura fa"
La'ila ha ilallah....shine abinda Shemau ke fada tana tafa hannuwa.
"Amaryar zamani da kanta take sanar da aurenta"
Wani hawayen ne ya zubowa Asmau bata ji haushin yayarta ba tace "na zata shima mutuwa zaiyi, tun jiya gabana ke faduwa"
Jikin Shemau yayi sanyi bata san abinda ke ran kanwarta ta ba kenan taje ta rungumeta. Ainau ma ta matso ta rungumeta suka soma kuka. Sabira da Zulaiha aka bari da rarrashinsu.
Sai da suka saka Asmau yin nafila godewa Allah sannan tayi wanka ta shirya suka tafi. Shigarsu gidan ke da wuya Yassar ya shigo yace ga ango a waje zasu dauki hoto da amarya. Umma tana cikin mutane ta girgiza kai tana murmushi. Wannan ango bashi da dama. Bare an daura aure ai shikenan kuma.
Dakin da suke zaune da su Rashida Mimi taje ta kirawota. Yawanci sallah masu rakata sukeyi sai ta nemi takwararta Ma'u ta rakata. Mayafi tasa ta rufe fuska haka suka fito. Ashe tawaga guda ce domin harda su Jafar da Qasim. Ita dai duk kunya ta isheta haka akayi hotunan ta kasa sakewa. Shima bai matsa mata ba. Ko don idon mutane ya raga mata.
Qasim tun fitowarsu idanunsa suka fada kan Ma'u. Yarinya ce kyakkyawa suna kama da Zulaiha sosai. Itama ta kula da kallon da yake mata sai ta sunkuyar da kanta cike da kunya. A take yaji wani abu a ransa game da ita. Sun gaisa da Asmau zata shiga ciki ya kalli Col. Ishaq. "Ango don Allah a bani dama zan roki amarya alfarma. Ta dan daga kai suka hada ido da Jikamshi yace "bari na matsa ga mutane can zamu gaisa. Idan kun gama sai kuyi mana jagora mu dauka dasu Hajjo"
"Godiya nake yallabai, idan tarkona ya kama zan fada maka don kune masu nema"
Su Anti Lami da Yaya Abu duk sun iso da safe da yaransu har na gidan miji. Abu yayi kyau ko babu komai dai dangi ba'a canza su.
Lalle aka zauna yi mata ja da baki wanda aka bata lokaci wurin yinsa. Tasha zama kuwa don 'yan uwanta sun dage bazata cire da wuri ba sai ya fito sosai yadda za'a jima ana cin amarci.
Ana idar da sallar jumaa aka fara wanka don gidan Umma, Mama da na Jafar duk babu masaka tsinke. Itama Asmau kafin a kira la'asar tayi wankanta mai kwalliya Najah tazo ya fara aikinta. Fuska ta dauka don Naja ba daga nan ba. Kwalliyar ta nutsuwa ce ba'ayi mugun fentin nan na foundation ba da fuskar mutum take canzawa gabadayanta. Ana gamawa ta tashi tayi sallah aka sake gyarawa sannan ta saka kaya. Idan ka ganta a lokacin bazaka ce Asmau mai wankin bandaki bace a asibitin Jos. Tayi kyau ba kadan ba. A lokacin yawancin matan dake gidan sun tafi venue din. Yaya Abu ce ta kira Zubaida akan lallai su taho da amarya da wuri mutane sun soma cika a wurin. Ita har mamaki take yi wasu daga ina suka zo.
Wata mota ango Ishaq ya turo mai kyau ta daukar amarya zuwa wurin biki. Da suka isa ita da Walida da Zulaiha ne a motar. Safiyya tazo tace ta zauna domin ango yana hanya sai ya iso zata fito. Ta saki wani murmushin jindadi bayan Safiyya ta tafi. Zulaiha ta ce
"Hmm Asmau amare na dan kuka rana irin ta yau sai fara'a kike yi."
Allah Yasa dreban motar ya fita sai AC da aka ware musu. Walida tace "baki ga komai ba ita da Col. Ishaq nasu salon daban yake"
Asmau tayi fari da ido kawai tana murmushi. Motar tasu mai tint ce ta waje ba'a ganinsu sun jiyo kida daga wurin bikin yana tashi ga mata suna ta shige da fice. Wurin cike yake da sojoji masu gadi. Da farko ma taron ba'ayi niyar yi da maza ba. Sai Mami ta roka akan cewa ango zai zo da abokansa suyi hoto da amarya ya tafi. Shima da kyar ya yarda da zuwan. Shemau ce ta fada mata kalar kayan da amarya zata saka suka yi gaggawar nemawa ango wanda zai dace.
Bugu zuciyar Asmau ne ya karu da ta hango motar Jikamshinta. Wurin motoci bakwai ne suka shigo tare. Wai bikin da akace babu maza kenan. 'Yan kashe kwarkwarar ido da abokan arziki duk sun biyo shi.
Saitin motar da take Dahiru da ya tuko motarsa ya daidaita tasu yadda zasu fito tare. Ya hakimce a baya yana waya. Sai da ya gama ya fito ko'ina ya dauki kamshi.
Kofar inda take zaune yaje ya bude suka hada ido. Babu karya ya yarda yana son Matar Jikamshi. Duk abinda kake so kuwa dole kaga kyaunsa. Indai haka ne Jikamshi da Asmau sunyi kyau a yau ranar kamunsu. Wani hadadden lace ne peach a jikinta da ta samu tela yayi mata dinki na gani a fada. Doguwar riga ce amma tayi kyau sosai mai dogon hannu. Dankwalin rigar aka hada da wani yadi mai kyalkyali purple mara turowa akayi mata dauri. Sai tasa mayafi irin yadin aka makale mata shi daga tsakiyar daurin nata da pin. Takalminta mai tsini da jaka duk kalar mayafin ne. Ango ma shaddarsa irin mayafin nata ce amma fa ba mai kyalli ba. Ga hula har wani dan karkacewa tayi. Asmau tana gama fitowa aka fara daukar hotuna kamar me. Safiyya da Shemau ne masu tsari suka jera su MC din taro S.Kilishi ita ce ta sanar da shigowar ango da amarya. Suka taho suna taku daidai. Wuri ya kaure da sowa.
_Qamshi qamshi yana tashi, 'yan mata zamu kamun amarya_
_Yaune muke shirin kamu...amarya_
_Asmau amarya zo gamu...amarya_
_Ki hakuri da zancenmu, kinsan aure yana kanmu_
Kafin mai wakar ta karaso gaban ango da amarya tuni 'yan mata sun fito ana ta rausayawa. Jajimaji kenan, idan ta bude baki ko Sangandali sai dai taja baya. Haka ta cigaba da waka har amarya da ango suka zauna.
Bayan Hajiya YBK ta bude taro da addua aka shiga biki da gaske. Su Bilkisu da tawagar gidan Hajiya Lubabatu da 'yan Jikamshi ankonsu iri daya ne da nasu Ainau. Ga su Amatullah yau anyi kwalliya itama ta fito sosai. Yaran su Shemau da nasu Sadiya 'yan uwan Abubakar kowa fa yayi kyau.
An bukaci dangin ango su fito fesawa amarya turare sai gasu mata biyar ne harda Mami kowacce da tsadadden turare a hannunta suka zo a rinka fesawa. Biki yayi biki mata sun sha rawa. A cikin taron mata 'yan taya ango da amarya murna sun gwangwaje. Saboda yawansu ba sunan kowa zaka iya kamawa ba. Akwai su Maman Afrah, Tash, Jatma, Zahida, Mrs G, Sadiya Jegal, Ibtihal, Shukriya, Ummu Rauda, Maman Sadiq, Ummu Aslam, Mrs Ambursa, Hauwa Ag, Mum Little, Farha, Jammu, Mardiya, Shafa, Ruqayya, Tafeesu, Ummi BK, Didi, Mjay, Zahra BB, Biebie Isah, Temseey, Khadija Candy.....(wai abin da yawa ni mai rubutu naji hannuna zai tsinke nace wallahi sauran ma duk ina sonku har raina).
Taro kam ya kayatar. Anci an sha an kuma rausaya. Ana cikin daukar hotuna ne Mama Yalwa tazo zasu dauka ita da Asmau da ango. Suna hada ido da Asmau suka tuna abu daya suka fara kuka lokaci guda. Duk wanda yasan wadannan matan yasan kukan me suke yi. Allah Ya jikan Abubakar, mutuwarsa ce tasa har aka zo rana irin wannan. Suna yi ana tayasu har su Umma. Suwaiba karamar kanwarsa ce ta iya daurewa tana basu baki. Col. Ishaq duk kishi irin nasa ya dauke kai a yau. Abubakar wani bangare ne na rayuwar Asmau da bazai gogu ba.
Haka aka kare taron kowa ya tafi gida cikin farinciki da annashuwa. 'Yan gulma basu sami abin fada ba sai san barka domin taro ya burge kowa.
*****
Washegari sai shabiyun rana zaa daura aure. Asmau tun dare ta kasa baccin kirki. Yaushe zata manta ranar aurenta na farko da ango ya rasu. Ji tayi gabadaya bata da kuzari har gari ya waye.
Col. Ishaq kuwa jin kansa yake kamar anyi masa wani albishir mai kyau. Farar shadda ya saka harda babbar riga. Anyi mata aiki da zare ruwan goro saboda haka hularsa da takalmi harda agogon hannunsa ruwan goron ne. Masallacin Hotoro ya dauki jama'a wadanda suke son shaida wannan babbar rana. Su Jafar da Yassar suna kan gaba, ga Kawu Garzali da wani abin mamaki Kawu Rabe yazo yana ta ra6e ra6e. Bisa amincewar Hajjo da sauran 'yan uwansu Alh Adamu Matawalle shine waliyin amarya. ASP Qasim ma gayya guda yazo da ita daga abokan aiki zuwa makusantansa a Shanono. Ga su Sada suma ba'a barsu a baya ba.
Ango sai faraa yake yana gaisawa da jama'a. Har hoto suka yi da Qasim suka gaisa a mutunce. Shabiyu nayi Liman ya bukaci wakilin angon da waliyin amarya. An daura auren Col. Ishaq Muhammad Jikamshi da Asmau Shu'aib Yahya akan sadaki dubu sittin.
*****
Asmau na zaune kowa yayi wanka ana ta shirin tafiya gidan Umma inda zasu zauna saboda baki masu son ganin amarya. Tamkar wadda aka zarewa laka haka take jin jikinta. Ga faduwar gaba da ta kwana dashi. Tana kwance text ya shigo wayarta ta dauka a firgice. Kalma daya ta gani daga Jikamshi wadda ta saka ta kuka sosai.
*Alhamdulillah.*
Su Sabira suka zuba mata ido har dakin ya fara cika da su Ainau da Zulaiha suna ta tambayarta me aka yi mata. Shemau rai a bace tace "ku kyaleta tayi kukan nan. Tun daren jiya take neman yinsa. Ni nayi mamaki ma da kika jira sai yanzu. Ace mutum bashi da sana'a sai ta zubar da hawaye."
Tana kukan tace "Anti Shemau an daura fa"
La'ila ha ilallah....shine abinda Shemau ke fada tana tafa hannuwa.
"Amaryar zamani da kanta take sanar da aurenta"
Wani hawayen ne ya zubowa Asmau bata ji haushin yayarta ba tace "na zata shima mutuwa zaiyi, tun jiya gabana ke faduwa"
Jikin Shemau yayi sanyi bata san abinda ke ran kanwarta ta ba kenan taje ta rungumeta. Ainau ma ta matso ta rungumeta suka soma kuka. Sabira da Zulaiha aka bari da rarrashinsu.
Sai da suka saka Asmau yin nafila godewa Allah sannan tayi wanka ta shirya suka tafi. Shigarsu gidan ke da wuya Yassar ya shigo yace ga ango a waje zasu dauki hoto da amarya. Umma tana cikin mutane ta girgiza kai tana murmushi. Wannan ango bashi da dama. Bare an daura aure ai shikenan kuma.
Dakin da suke zaune da su Rashida Mimi taje ta kirawota. Yawanci sallah masu rakata sukeyi sai ta nemi takwararta Ma'u ta rakata. Mayafi tasa ta rufe fuska haka suka fito. Ashe tawaga guda ce domin harda su Jafar da Qasim. Ita dai duk kunya ta isheta haka akayi hotunan ta kasa sakewa. Shima bai matsa mata ba. Ko don idon mutane ya raga mata.
Qasim tun fitowarsu idanunsa suka fada kan Ma'u. Yarinya ce kyakkyawa suna kama da Zulaiha sosai. Itama ta kula da kallon da yake mata sai ta sunkuyar da kanta cike da kunya. A take yaji wani abu a ransa game da ita. Sun gaisa da Asmau zata shiga ciki ya kalli Col. Ishaq. "Ango don Allah a bani dama zan roki amarya alfarma. Ta dan daga kai suka hada ido da Jikamshi yace "bari na matsa ga mutane can zamu gaisa. Idan kun gama sai kuyi mana jagora mu dauka dasu Hajjo"
"Godiya nake yallabai, idan tarkona ya kama zan fada maka don kune masu nema"