Sashe 58
Abinda Ake Gudu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Asmau ta rufe ido kawai. Ba karamin kewarsa take yi ba ita kanta. Gashi tasan abubuwa sunyi masa yawa tunda bikin ya matso amma kullum kokarinsa ya ganta ko yaji dadi. Sai ake rashin sa'a idan yazo an fara shafe shafe ko turara mata jiki. Da daga ita sai Massouda ne kawai yadda suke wasa da matar ficewa zatayi ba'a sani ba. Amma kullum ba'a rasa babba da take jin kunya.
Har Yassar ya juya Hajjo ta dakatar dashi. Tace a goge jikin ta fita "gyaran nan ai saboda shi ake yi ko. Kwana nawa kullum yazo amsa daya ai babu dadi, sai kun sa ta fita a ransa. Ko dai ku barta ta fita ko kuma naje na kawo shi har dakin nan muga karshen gyara"
Umma kunya ta kamata ta fice daga dakin su Anti Bintu suna dariya. Auduga ake tsomawa cikin ruwan wani humra mai bala'in kamshi ana goge mata jiki. Sai da aka gama tas ta zura dogon hijab akan rigar jikinta ta fita don ko kwalliya an hanata sai ranar kamu.
*****
Tayi zaton yana waje sai ta ganshi a falo yana waya ga Yassar da Amatullah suma suna zaune. Cikin nutsuwa ta shigo falon Yassar ya dauki Amatullah a wuyansa suka fice.
Col. Ishaq ko sallama baiyi ba a wayar ya kashe yana kallonta. Ya ciri tuta a iya kallo mai kashe mata jiki. Ashe ita ma tayi missing dinsa sosai. Sai yanzu da ta ganshi taji sauki a ranta. Ko hoda babu a fuskarta kuma iya abinda yake iya gani kenan amma tayi masa kyau. Ga wani kamshi mai sanyi da bai san da yadda zai fasalta shi ba yana fitowa daga jikinta.
Kujeru biyu ne tsakanin wadda ta zauna da tashi ta gaishe shi amma da kai ya iya amsawa babu magana. Shirun nasa ya dameta tace "Jikamshina yaya, ko kayi fushi ne?"
Yayi sassanyar ajiyar zuciya "Matar Jikamshi harda muryarki ma gyarata ake yi? Tunanin nawa zan karawa matar da take gyara min ke nake. I just love the way you look. Matsalata daya ce hanani ganinki da ake yi"
Tayi murmushi "to kayi hakuri kaji _Jikamshina_ .
"Na fada miki idan zan tafi ki dena kirana da sunan nan amma kinki ji ko?"
Wani kalar tausayi yake mata tayi dariya sannan ta fara magana da shagwaba "haba Jikamshina yanzu fa na fito. Ko rabin ganinka banyi ba kake zancen tafiya"
"Kina wasa dani yarinyar nan. Nace ki dena kin cigaba. Kada kice banyi warning dinki ba dai. Bari na tafi, da na sani ban matsa sai na ganki ba yau"
Gabanta taji ya fadi ko dai yayi fushi da gaske ne. Tana ganin ya tashi itama ta mike tsaye jiki a sanyaye tace
"Me yasa kace haka"
Kallon da yake mata na ido cikin ido ne yasa tayi saurin kawar da kanta. Rage muryarsa yayi yadda itama bata jinsa sosai batare da ya bar kallonta ba yace "zan fada miki nan gaba. I love you. Sai da safe"
Kasa amsa masa tayi tana kallonsa ya fita. Ta koma ciki duk tana jin babu dadi. To me tayi masa haka da ko minti shabiyar batayi ba da fitowa ya tafi. Ko dai yayi fushi ne da gaske? Bazata iya jurewa hakan ba kwanaki kadan kafin aurensu. Dakinsu ta koma ta dauko wayarta zata tura masa text don bata son kira yana tuki. Hakuri zata bashi idan ma tayi laifi ne. Tana dauko wayar ta ga sakonni a whatsap dinta. Idan ba 'yan gidansu dasu Rashidan Azare ba babu wanda take chatting dashi sai Jikamshinta. Budewa tayi zata tura masa text sai taga nashi ne a sama alamun yanzu ya turo sakon.
_Allah Ya kaimu ranar aurenmu Matar Jikamshi. Ranar zaki san irin matsayin da Allah Ya baki a zuciyar Ishaq. Kada ki fassara tafiyata da komai, idan na dade tare dake *kamshin matar jikamshi zaiyiwa jikamshinta illah* Ji nayi kamar na tafi dake._
Asmau ta karanta sakon yafi a kirga tana murmushi ita kadai. Ko a yanzu ace zaiyi mata kishiya ta tabbatar zuciyarta zata iya bugawa. Duk wannan kalaman nasa da iya nuna kulawa ace ya nunawa wata matar bata san inda kishi zaiyi da ita ba. Adduar son kai tayi a zuciyarta. Allah Yasa Jikamshi nata ne ita kadai....
*****
Washegari da azahar sai ga Zulaiha a Kano ita da su Humaira, Muhsin da sauran 'ya'yanta. A bakin kofa suka rungume juna suna tsalle kamar wasu yara ita da Asmau. Yara na murnar ganin Amatullah. Gida mai dadi ba Zulaiha ba hatta yaranta sun dan murmure. Kayan jikinsu kuwa ya isa ya fada maka cewa babanta wani ne. Don ko gidan Mama da Asmau take yiwa kallon arziki sosai bai kai na mahaifin Zulaiha ba. Kaddara da rabon 'ya'ya ya kaita auren Gidado. Dreba mahaifinta yasa ya kawosu tare da kanwarta itama sunanta Asmau suna kiranta Ma'u.
A tsarin bikin ranar Juma'a za'ayi Kamu da walima wanda gidan amarya ne suka dauki nauyi. Washegari asabar a daura aure sannan bayan magriba ayi Sword Crossing sai kuma ranar lahadi ayi yini a kai amarya.
Yadda su Shemau suka ci burin kawata kamun ayi biki mai kayatarwa wasu mata suka dauko masu shirya biki da duk wani abu na bikin kamar abinci da harkar decoration. Ya da kanwa ne Aisha da Zainab Maiturare. Tunda suka ji sunan ango har ragin kudi suka yi musu sun ce ai su kannensa ne wannan biki na yayansu ne saboda haka zasu zage damtse wurin yin abinda za'a yaba.
Rashida tazo itama da yaranta da kanwarta Harira. Yaya Tagwai ma ba'a barta a baya ba. Da ta shigo gidan harda kukata tana bawa Asmau hakuri da bata tausaya mata ba ta koreta. Sai a lokacin suka daidaita da Hajjo. Mutanen Wushishi da amarya Dijah wadda ta kafawa mijinta naci duk sun zo. Gida kam yayi albarka don ya cika da 'yan uwa da abokan arziki. Asmau gidan Jafar ta koma ita da Zulaiha. Rashida tana tare da Zubaida a nata gidan inda take kula da Uwargida. Sai bayan biki zasu je Jikamshi.
Sabira ce ta kai Asmau wani salon aka gyara mata kai gashin nan yana ta kyalli sannan aka gyara kafa da hannu. Ta kalli Sabira tace "yanzu banda iyayi har hannu ma ana gyara shi. Na zata sai masu saka farce ake yiwa"
"Ummin Amatullah yanzu gyara ai ko'ina ake yiwa. Matan da ake cewa suna kwacen miji a waje ba wata tsiya suka fimu ba sai gyaran da rashin kunya. Mu kuma Hausawa komai sai mu ce Allah Ya sauwake nayi kaza bayan kuma gidan mijinki kike"
"Kuma fa gaskiya ne, shiyasa naga Yaya Jafar indai abu ya shafeki wallahi baya kyashi ko kadan. Ashe gyara ne da sauran sirrikan da zanzo ki bani. Muma Allah Yasa mu dace"
Suka yi dariya, Sabira tace "ai dacewa dai kin gama. Wallahi ki rike baban Amatullah tsakani da Allah. Irin yadda yake sonki kadai ya isa ya nuna miki cewa Allah Yana jin adduar bayinSa. Abinda ya rage kawai ki bi duk wata hanyar kyautata masa yasan cewa shima ya auri mai sonsa."
Ummy mai salon tana mata gyara tana nade shawarar da Sabira ke bata itama zata gwada a nata gidan.
*****
Ranar da daddare Col. Ishaq ya dawo gida a gajiye saboda ya tsaya karasa wasu ayyuka kafin hutunsa na aure ya fara washegari. Har wani aiki za'a turo shi Liberia ya samu aka bawa wani. Suna magana da Mami da ta iso a ranar ne yaji waya. A zatonsa Asmau ce don yau aiki yasha masa kai tun wayar safe bai kara kiranta ba. Da ta kira ma bai ji ba sai daga baya ya gani ya aika mata da text.
Bakuwar numba ce ya dauka tare da sallama. Muryar da yaji ko bata fadi sunanta ba bazai taba mantawa da ita ba.
Badariyya...
Ko aurenta ya mutu ne????
ABINDA AKE GUDU🙆🏽53
Batul Mamman💖
Amsa sallamar tasa tayi suka gaisa a mutunce. Shiru ya biyo baya ya katse shi ta hanyar tambayarta ya maigidanta da danta Nabil. Dan gyaran murya tayi tace
"Uhmm Ishaq dama dazu naje yini gida ne aka bani katin bikinka. Ashe aure zakayi babu labari"
"Badar kenan, kina gidan mijinki ai bai kamata na kiraki nace zanyi aure ba. Dama Hajiya tace zata aika cards nasan zaki ji labari"
Rayuwa kenan, mutumin da suke matukar son juna gashi yanzu akwai katanga mai karfi tsakaninsu. Tayi dan murmushi. Wayar ma sai da ta nemi izinin mijinta dama ta kira saboda kare hakkin aure. Zancen ba'a son ranta akayi auren ba tuni ya wuce da ta sami ciki.
"Allah Ya sanya alkhairi na bugu inyi maka dama. Sai dai naji wani labari a gida da ya tada min hankali...."
Katseta yayi wayar ta fara isarsa. Abokai da mutanen da bai ba sani ba duk sun ishe shi da irin wannan maganar. Ga kiran Asmau yana ta shiga call waiting.
"Cewa Asmau tana da 'yar da ta haifa babu aure ko? Haka ne abu daya kawai zakiyi min shine adduar da kika yi ta Allah Ya sanya alkhairi ki cigaba da yi"
Maganarsa batayi mata dadi ba "idan saboda rashin haihuwa ne don Allah ka nemi wata mai 'ya'yan. Me zakayi da wadda ta gama yawonta a gari?"
Runtse ido yayi ransa na kara baci. Haka ce zata yi ta faruwa kenan ko bayan aurensu. Albakarcin zaman tare da son da yayi mata a baya ya hana shi fada mata maganar da zata dade tana mata ciwo a rai.
"Kema kinsan bazanyi aure irin wannan ba. Ina son Asmau da zuciya daya. Anyway nagode da wayar taki. Ki gaida mijinki"
Ya katse wayar Mami tace "kayi hakuri Yaya. Nasan bazai wuce irin maganar da mukayi ba ita ma shi tayi. Sai an sami mai zurfin tunani ne zai nemi jin ainihin labarin Asmau kafin ya yanke muku hukunci."
"Gaskiya ne, Allah Ya kyauta. Babu mai iyawa mutane sai Ubangijin da Ya haliccemu. Komai kayi a wurin mutane baka iya ba a wurin wasu."
Dakinsa ya tafi ya kira Asmaunsa yana bata hakurin rashin jinsa da tayi. Dayake tasan yana aiki tace babu damuwa. Sunyi hira wadda duk akan abinda ya shafi biki ce sannan ta kwanta.
*****
Har Yassar ya juya Hajjo ta dakatar dashi. Tace a goge jikin ta fita "gyaran nan ai saboda shi ake yi ko. Kwana nawa kullum yazo amsa daya ai babu dadi, sai kun sa ta fita a ransa. Ko dai ku barta ta fita ko kuma naje na kawo shi har dakin nan muga karshen gyara"
Umma kunya ta kamata ta fice daga dakin su Anti Bintu suna dariya. Auduga ake tsomawa cikin ruwan wani humra mai bala'in kamshi ana goge mata jiki. Sai da aka gama tas ta zura dogon hijab akan rigar jikinta ta fita don ko kwalliya an hanata sai ranar kamu.
*****
Tayi zaton yana waje sai ta ganshi a falo yana waya ga Yassar da Amatullah suma suna zaune. Cikin nutsuwa ta shigo falon Yassar ya dauki Amatullah a wuyansa suka fice.
Col. Ishaq ko sallama baiyi ba a wayar ya kashe yana kallonta. Ya ciri tuta a iya kallo mai kashe mata jiki. Ashe ita ma tayi missing dinsa sosai. Sai yanzu da ta ganshi taji sauki a ranta. Ko hoda babu a fuskarta kuma iya abinda yake iya gani kenan amma tayi masa kyau. Ga wani kamshi mai sanyi da bai san da yadda zai fasalta shi ba yana fitowa daga jikinta.
Kujeru biyu ne tsakanin wadda ta zauna da tashi ta gaishe shi amma da kai ya iya amsawa babu magana. Shirun nasa ya dameta tace "Jikamshina yaya, ko kayi fushi ne?"
Yayi sassanyar ajiyar zuciya "Matar Jikamshi harda muryarki ma gyarata ake yi? Tunanin nawa zan karawa matar da take gyara min ke nake. I just love the way you look. Matsalata daya ce hanani ganinki da ake yi"
Tayi murmushi "to kayi hakuri kaji _Jikamshina_ .
"Na fada miki idan zan tafi ki dena kirana da sunan nan amma kinki ji ko?"
Wani kalar tausayi yake mata tayi dariya sannan ta fara magana da shagwaba "haba Jikamshina yanzu fa na fito. Ko rabin ganinka banyi ba kake zancen tafiya"
"Kina wasa dani yarinyar nan. Nace ki dena kin cigaba. Kada kice banyi warning dinki ba dai. Bari na tafi, da na sani ban matsa sai na ganki ba yau"
Gabanta taji ya fadi ko dai yayi fushi da gaske ne. Tana ganin ya tashi itama ta mike tsaye jiki a sanyaye tace
"Me yasa kace haka"
Kallon da yake mata na ido cikin ido ne yasa tayi saurin kawar da kanta. Rage muryarsa yayi yadda itama bata jinsa sosai batare da ya bar kallonta ba yace "zan fada miki nan gaba. I love you. Sai da safe"
Kasa amsa masa tayi tana kallonsa ya fita. Ta koma ciki duk tana jin babu dadi. To me tayi masa haka da ko minti shabiyar batayi ba da fitowa ya tafi. Ko dai yayi fushi ne da gaske? Bazata iya jurewa hakan ba kwanaki kadan kafin aurensu. Dakinsu ta koma ta dauko wayarta zata tura masa text don bata son kira yana tuki. Hakuri zata bashi idan ma tayi laifi ne. Tana dauko wayar ta ga sakonni a whatsap dinta. Idan ba 'yan gidansu dasu Rashidan Azare ba babu wanda take chatting dashi sai Jikamshinta. Budewa tayi zata tura masa text sai taga nashi ne a sama alamun yanzu ya turo sakon.
_Allah Ya kaimu ranar aurenmu Matar Jikamshi. Ranar zaki san irin matsayin da Allah Ya baki a zuciyar Ishaq. Kada ki fassara tafiyata da komai, idan na dade tare dake *kamshin matar jikamshi zaiyiwa jikamshinta illah* Ji nayi kamar na tafi dake._
Asmau ta karanta sakon yafi a kirga tana murmushi ita kadai. Ko a yanzu ace zaiyi mata kishiya ta tabbatar zuciyarta zata iya bugawa. Duk wannan kalaman nasa da iya nuna kulawa ace ya nunawa wata matar bata san inda kishi zaiyi da ita ba. Adduar son kai tayi a zuciyarta. Allah Yasa Jikamshi nata ne ita kadai....
*****
Washegari da azahar sai ga Zulaiha a Kano ita da su Humaira, Muhsin da sauran 'ya'yanta. A bakin kofa suka rungume juna suna tsalle kamar wasu yara ita da Asmau. Yara na murnar ganin Amatullah. Gida mai dadi ba Zulaiha ba hatta yaranta sun dan murmure. Kayan jikinsu kuwa ya isa ya fada maka cewa babanta wani ne. Don ko gidan Mama da Asmau take yiwa kallon arziki sosai bai kai na mahaifin Zulaiha ba. Kaddara da rabon 'ya'ya ya kaita auren Gidado. Dreba mahaifinta yasa ya kawosu tare da kanwarta itama sunanta Asmau suna kiranta Ma'u.
A tsarin bikin ranar Juma'a za'ayi Kamu da walima wanda gidan amarya ne suka dauki nauyi. Washegari asabar a daura aure sannan bayan magriba ayi Sword Crossing sai kuma ranar lahadi ayi yini a kai amarya.
Yadda su Shemau suka ci burin kawata kamun ayi biki mai kayatarwa wasu mata suka dauko masu shirya biki da duk wani abu na bikin kamar abinci da harkar decoration. Ya da kanwa ne Aisha da Zainab Maiturare. Tunda suka ji sunan ango har ragin kudi suka yi musu sun ce ai su kannensa ne wannan biki na yayansu ne saboda haka zasu zage damtse wurin yin abinda za'a yaba.
Rashida tazo itama da yaranta da kanwarta Harira. Yaya Tagwai ma ba'a barta a baya ba. Da ta shigo gidan harda kukata tana bawa Asmau hakuri da bata tausaya mata ba ta koreta. Sai a lokacin suka daidaita da Hajjo. Mutanen Wushishi da amarya Dijah wadda ta kafawa mijinta naci duk sun zo. Gida kam yayi albarka don ya cika da 'yan uwa da abokan arziki. Asmau gidan Jafar ta koma ita da Zulaiha. Rashida tana tare da Zubaida a nata gidan inda take kula da Uwargida. Sai bayan biki zasu je Jikamshi.
Sabira ce ta kai Asmau wani salon aka gyara mata kai gashin nan yana ta kyalli sannan aka gyara kafa da hannu. Ta kalli Sabira tace "yanzu banda iyayi har hannu ma ana gyara shi. Na zata sai masu saka farce ake yiwa"
"Ummin Amatullah yanzu gyara ai ko'ina ake yiwa. Matan da ake cewa suna kwacen miji a waje ba wata tsiya suka fimu ba sai gyaran da rashin kunya. Mu kuma Hausawa komai sai mu ce Allah Ya sauwake nayi kaza bayan kuma gidan mijinki kike"
"Kuma fa gaskiya ne, shiyasa naga Yaya Jafar indai abu ya shafeki wallahi baya kyashi ko kadan. Ashe gyara ne da sauran sirrikan da zanzo ki bani. Muma Allah Yasa mu dace"
Suka yi dariya, Sabira tace "ai dacewa dai kin gama. Wallahi ki rike baban Amatullah tsakani da Allah. Irin yadda yake sonki kadai ya isa ya nuna miki cewa Allah Yana jin adduar bayinSa. Abinda ya rage kawai ki bi duk wata hanyar kyautata masa yasan cewa shima ya auri mai sonsa."
Ummy mai salon tana mata gyara tana nade shawarar da Sabira ke bata itama zata gwada a nata gidan.
*****
Ranar da daddare Col. Ishaq ya dawo gida a gajiye saboda ya tsaya karasa wasu ayyuka kafin hutunsa na aure ya fara washegari. Har wani aiki za'a turo shi Liberia ya samu aka bawa wani. Suna magana da Mami da ta iso a ranar ne yaji waya. A zatonsa Asmau ce don yau aiki yasha masa kai tun wayar safe bai kara kiranta ba. Da ta kira ma bai ji ba sai daga baya ya gani ya aika mata da text.
Bakuwar numba ce ya dauka tare da sallama. Muryar da yaji ko bata fadi sunanta ba bazai taba mantawa da ita ba.
Badariyya...
Ko aurenta ya mutu ne????
ABINDA AKE GUDU🙆🏽53
Batul Mamman💖
Amsa sallamar tasa tayi suka gaisa a mutunce. Shiru ya biyo baya ya katse shi ta hanyar tambayarta ya maigidanta da danta Nabil. Dan gyaran murya tayi tace
"Uhmm Ishaq dama dazu naje yini gida ne aka bani katin bikinka. Ashe aure zakayi babu labari"
"Badar kenan, kina gidan mijinki ai bai kamata na kiraki nace zanyi aure ba. Dama Hajiya tace zata aika cards nasan zaki ji labari"
Rayuwa kenan, mutumin da suke matukar son juna gashi yanzu akwai katanga mai karfi tsakaninsu. Tayi dan murmushi. Wayar ma sai da ta nemi izinin mijinta dama ta kira saboda kare hakkin aure. Zancen ba'a son ranta akayi auren ba tuni ya wuce da ta sami ciki.
"Allah Ya sanya alkhairi na bugu inyi maka dama. Sai dai naji wani labari a gida da ya tada min hankali...."
Katseta yayi wayar ta fara isarsa. Abokai da mutanen da bai ba sani ba duk sun ishe shi da irin wannan maganar. Ga kiran Asmau yana ta shiga call waiting.
"Cewa Asmau tana da 'yar da ta haifa babu aure ko? Haka ne abu daya kawai zakiyi min shine adduar da kika yi ta Allah Ya sanya alkhairi ki cigaba da yi"
Maganarsa batayi mata dadi ba "idan saboda rashin haihuwa ne don Allah ka nemi wata mai 'ya'yan. Me zakayi da wadda ta gama yawonta a gari?"
Runtse ido yayi ransa na kara baci. Haka ce zata yi ta faruwa kenan ko bayan aurensu. Albakarcin zaman tare da son da yayi mata a baya ya hana shi fada mata maganar da zata dade tana mata ciwo a rai.
"Kema kinsan bazanyi aure irin wannan ba. Ina son Asmau da zuciya daya. Anyway nagode da wayar taki. Ki gaida mijinki"
Ya katse wayar Mami tace "kayi hakuri Yaya. Nasan bazai wuce irin maganar da mukayi ba ita ma shi tayi. Sai an sami mai zurfin tunani ne zai nemi jin ainihin labarin Asmau kafin ya yanke muku hukunci."
"Gaskiya ne, Allah Ya kyauta. Babu mai iyawa mutane sai Ubangijin da Ya haliccemu. Komai kayi a wurin mutane baka iya ba a wurin wasu."
Dakinsa ya tafi ya kira Asmaunsa yana bata hakurin rashin jinsa da tayi. Dayake tasan yana aiki tace babu damuwa. Sunyi hira wadda duk akan abinda ya shafi biki ce sannan ta kwanta.
*****