← Book details Abinda Ake Gudu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 18 OF 74

Sashe 18

Abinda Ake Gudu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Sai aya ta 2 a cikin suratun Nur wadda Allah SWT Yake cewa: *MAZINACIYA DA MAZINACI IDAN SUKA YI ZINA KU BULALI KOWANE DAYA DAGA CIKINSU BULALA DARI. KADA KUWA WANI TAUSAYI YA KAMAKU GAME DA TABBATAR DA HUKUNCIN ADDININ ALLAH IDAN KUN KASANCE KUN BADA GASKIYA GA ALLAH DA RANAR LAHIRA. KUMA LALLAI NE WATA TAWAGA DAGA MUMINAI SU HALARCI WURIN YI MUSU HADDIN*

Abubakar da Qasim duk hankalinsu yana ga bayanin wannan malami. Duk su biyun jikinsu yayi sanyi musamman Abubakar da yasan abinda ya aika.

Malam mai wa'azi cikin bayaninsa ya kawo hadisin Bukhari wanda Annabi SAW yake cewa _MAZINACI BA SHI DA IMANI A LOKACIN DA YAKE AIKATA ZINA...._

Da wani hadisin na Abdullahi ibn Mas'ud wanda yake cewa _MUN KASANCE TARE DA ANNABI SAW MATASA MARASA KOMAI NA DUKIYA_. _SAI ANNABI SAW YACE DAMU_:
_YA KU SAMARI, WANDA YA SAMI IKO A CIKINKU YAYI AURE DOMIN YAFI AKAN KARE KALLO DA MUTUMCI. WANDA BAZAI IYA BA SAI YAYI AZUMI SABODA ZAI ZAME MASA KARIYA._

Kallon kallo ne ya koma tsakanin Abubukar da Qasim a lokacin da malamin ya soma bayanin lahira da tanadin da Allah SWT Yayiwa bayi masu biyayya da masu sa6o. Ya karanto ayoyin Suratul Haaqqa wurin da Allah SWT Yake fadan irin farincikin da masu aikata aiki nagari zasu shiga idan sun karbi littafinsu da hannun dama da tanadi mafi kyau da Yayi musu a aljannah. Da kuma tashin hankalin ma'abota sabawa Allah a lokacin da suka karbi nasu littafin da hannun hagu(Ya Allah Kasa bama cikinsu. Amin) da azabar da zasu tarar.

Duk da Qasim ya shiga tashin hankali da jin wadannan bayanai saboda abinda yake aikatawa na shafa jikin 'yan matansa saboda gusar da sha'awa, yayi matukar mamaki ganin Abubakar ya fashe da kuka. Dafa abokin nasa yayi yana cewa
"Ba kaine zaka yi kuka ba Abubakar. Ni ne ya kamata nayi kuka saboda nasan na sabawa Allah sosai. Irin wannan abin da na fada maka akalla nayi da mata wurin biyar."

Abubakar ya kalle shi hawaye na kwararo masa." Qasim nawa sabon yafi naka. Na cuci kaina na aikata zunubin da bana hangowa kaina komai sai azaba."

A tsorace Qasim ya dago kan Abubakar dake kallon kasa" ban fahimceka ba, kada dai kace maganarmu ta rannan tasa kaima kaje kayi romancing wasu. Na shiga uku, ai ni ne cikin matsala tunda duk wanda yayi umarni da mummunan aiki yana da zunubi kwatankwacin na wanda ya aikata kamar yadda yake ga mai umarni da kyakkyawa".
Dafe kansa kawai yayi yana tunanin wannan sabon tashin hankali da ya saka kansa a ciki.

Zuciyar Abubakar cike da danasani yace "Qasim zina nayi"

"What??? Abubakar garin yaya? Da wa?"

Sai da ya hadiyi yawu da kyar ya iya amsawa "Asmau".

Qasim yana girgiza kai yana karanto La haula...
"Marainiyar yarinya, wayyo Abubakar ni ne sila ko? Tun yaushe ne? Garin yaya ka aikata hakan kai da ka kusa aure? Idan aka gane fa? Ga mahaifiyarta mutuniyar kirki."

Tambayoyin da Qasim keyi shima Abubakar din sune suke masa yawo a kansa. Yana hawaye ya sanar da Qasim abinda ya faru da irin kunya da bakincikin da ya sami kansa a ciki. "Yanzu shikenan nima da hannun hagu zan karbi littafi na ranar lahira. Lallai Annabi SAW yayi gaskiya da yace a hadisi na hudu cikin arba'una na Annawawi wanda aka karbo daga Ibn Mas'ud yake cewa ..
_......Hakika dayanku zaiyi ta aikata aiki irin na 'yan aljannah har sai ya kasance tsakaninsa da ita bai wuce zira'i ba sai littafinsa ya rinjaye shi sai ya aikata aiki irin na 'yan wuta sai ya shigeta...._

Qasim ya soma hawaye " in sha Allahu bazamu shiga wuta ba. Ka manta Allah Yayi alkawarin yafe zunubin masu tuba.?"

Sai da suka sha kukansu sannan Abubakar ya bawa Qasim wayarsa ya karanta wasu cikin sakonnin text da Asmau ta turo masa.

_Yaya Abubakar ka dubi girman Allah ka daga wayata. Kada ka gujeni a wannan lokacin_

_Idan ka rabu dani rayuwata bazata kara wani amfani ba. Me zan fadawa duniya nan gaba._

_Kai kadai ne zaka iya taimakona a wannan halin. Ka daure kada ka fasa aurena._

_Na amince ko washegarin aurenmu ne ka sakeni wallahi bazan yi korafi ba. Amma yanzu idan ka kini duk wanda ya aureni zai iya tona min asiri._

Kasa kara karatun Qasim yayi saboda tausayin Asmau da ya kama shi. Sun dauki wasu mintuna babu mai magana sai muryar malamin nan kawai suke ji yana kara tsorata mutane game da aikata zina.

Qasim ya tashi tsaye yana kashe kayan wuta na dakin dake kunne "ka tashi mu tafi ka bawa yarinyar nan hakuri sannan mu san yadda zamuyi su Baba su amince a matso da bikin nan zuwa wata biyu tunda kace mai hayar naka har ya gama ginin da wuri."

"Kana ganin zasu amince? Wata hudu ya rage da 'yan kwanaki yanzu nace a maido shi baya?"

"A nawa ganin hakan ne zai kara kwantarwa Asmau da hankali tasan cewa da gaske bazaka gujeta ba. Wallahi Abubakar ban taba zaton zamu wayi gari mu ga rana irin wannan ba. Ba don da bakinka ka fada min ba Allah bazan taba yarda ba."

Rufe dakin suka yi sannan suka fita zuwa motar Abubakar. Qasim ne zai tuka su. A hanya suka sami masallaci sukayi sallar juma'a sannan suka wuce Kano suna ta tattauna yadda zasu bullowa su Baba domin su yarda a dawo da bikin baya. Kafin su rabu sai da Abubakar yasa Qasim yayu masa alkawarin wannan zancen zai zama sirri a garesu har mutuwa.

*****
Ko gida Abubakar bai shiga ba yana sauke Qasim ya tashar unguwar kabuga zai wuce Shanono, gidansu Asmau ya wuce kai tsaye. Lokacin Umma na wurin aiki ita kuma tana daki tana sana'ar kuka. Ta gama sawa ranta Abubakar ya gujeta kenan yanzu abinda ya faru matsalarta ce ita kadai. Jafar ne ya buga mata kofar daki ya sanar da ita zuwan Abubakar.

A zabure ta tashi ta lulluba mayafi ya rufe mata rabin fuska ta fita ta same shi a wurin da Umma ke ajiye mota.

Tana zuwa gabansa bata yi la'ari da cewa wani zai iya ganinsu ba ta zube gwiwoyinta a kasa tana kuka mai sauti.
"Don Allah Yaya Abubakar kada kace kazo rabuwa dani. Gara na mutu da in ga ka juya min baya a wannan yanayin."

Waigawa yayi ya tabbatar babu mai ganinsu sannan yayi mata alama da ta tashi. Shima hawayen yake shirin yi.
"Asmy kiyi hakuri ki yafe min. Naci amanarki na cutar dake. Amma ina so kisan cewa bazan gujeki ba. Wannan tsautsayin ni ne na tilasta miki saboda haka tare zamu fuskance shi. Idan kin amince zanyi magana a gida a dawo da bikinmu nan da wata biyu".

Wani hawayen ne ya sakko mata ga dariyar farinciki duk a lokaci daya.
"Da gaske? Wallahi na amince. Na yarda. Nagode Yaya Abubakar."

"Ki dena yimin godiya. Ni dake duk bamu fi karfin kaddara ba. Kuma kowane bawa akwai irin jarabawarsa a duniya. Dama Annabi SAW yace _Shaidan yana gudu a jikin mutum kamar yadda jini yake yi._
Kinga ashe bamu fi karfin fadawa tarkonsa ba. Sai dai Ubangijinmu mai rahma ne da gafara. Idan muka tuba sai kiga kamar ba'ayi ba."

A sanyaye yake maganar ciki da nadama.

Daga wannan lokacin suka fara azumi da tashi cikin dare neman gafarar Allah. Yaso samun matsala da su Baba amma daga baya sun amince an matso da auren. Tun daga lokacin Asmau take bashi girma fiye da na da, tsoro take yi kada ta kuskure yace ya fasa asirinta ya tonu.

Haka lokaci ya tafi har zuwa bikinsu da abinda ya faru bayan nan.

*****
*CIGABAN LABARI*

Asmau ta share hawayenta bayan ta gama bawa Zubaida labarinta. Ita ma Zubaidan kukan take yi na tausayi ga bakuwar da kwanansu daya da haduwa amma jininsu ya hadu.

"Tabbas kinga tashin hankali a rayuwarki Asmau. To amma abinda ya daure min kai shine yadda kuka tuba amma duk da haka kika tsinci kanki a irin wannan rayuwar".

Dan murmushi Asmau tayi "Zubaida kenan, tubanmu ba shi zai hana faruwar kaddarar rayuwarmu ba. Komai da kika gani ya faru ga bawa rubutaccen al'amari ne tun kafin zuwansa duniya. Wani abin yana faruwa ne domin ya zama darasi ga wasu don su kiyaye. Ni bana bakinciki da ikon Allah. Nasan bazai barni na tabe ba albarkar Annabi SAW."

Zubaida ta gyada kai ta gamsu da bayanin Asmau.
"Allah Ya jikan Abubakar"

Asmau tace "Amin " tana share kwalla.
ABINDA AKE GUDU🙆🏽20

Batul Mamman💖

Wani mugun fitsari ne ya tashi Asmau daf da kiran assalatu. Ta fito zata je bandaki amma ko ruwan tsarki bata dashi. Haka ta koma daki tana ta matse shi da adduar Zubaida ta fito da wuri ko dan yaya ne ta sammata. Har aka idar da sallah a masallaci Zubaida bata fito ba. Zuwa lokacin Asmau sai gumi take yi tana cilla kafa. A hankali taji ya fara zubowa dole ta tafi bandakin da gudu tayi batare da tayi tsarki ba. Haka ta dawo dakinta ta shafi kura tayi taimama sannan tayi sallar asuba.

Batun jin yunwa dama ba'a magana. Wannan yanayin da ta tsinci kanta a ciki hakurinta ya fara karewa. Ace tayi fitsari ko ruwan tsarki babu gashi tana gani amma gidan nafsi nafsi (kowa na ta kansa)kawai ake yi.

Yau Zubaida bacci sosai take yi don har tara ta wuce bata farka ba. Asmau ta gaji da jiran tsammami ta duba hijabinta wanda yafi kowanne dauda ta saka ta fita bakin titi. Ga rana ta kwale haka ta daure zuciyarta ta zauna duk wanda yazo wucewa tace.

_Sadaka fisabilillah_

Mutumin farko da ya bata naira goma yana yin gaba ta saka kuka. Wai ita da watanni kadan da suka wuce take cikin rayuwar jindadi tare da masoyinta da iyayenta, ita ce take bara tamkar mara galihu. Bara sana'ar da take tattare da kaskanci da mutuwar zuciya. A ranta addua take yi Allah Yasa mufi karfin zukatanmu Ya nesanta mu da kaddara mai muni irin wannan.
Chapter 18 · 0% Book details