Sashe 67
Abinda Ake Gudu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tayi murmushi tana shafa sajensa "kullum ma kyau kake min Jikamshina. Musamman idan kasa kayan nan kamar kada ka fita"
Yaji dadin abinda ta fada. Kamar yadda mata ke son a yabe su haka maza suke so suma matansu su yaba musu. Wayarta ya karba ya daukesu selfie suna yiwa juna murmushi. Bayan ya dauka yace "Matar Jikamshi kinyi kuka ko"
Asmau tayi saurin kai hannunta wurin idonta zata goge sauran hawayen da tayi lokacin da take tsaye yana bacci.
"Abu ne ya shigar min ido fa"
"Uhmm uhm Matar Jikamshi kada mu fara yiwa juna karya. Na kuma san halinki da saurin kuka. Fada min me kika saka a ranki."
A nutse yake kallonta ta sake shige masa tana jin wani hawayen na kokarin zuba.
"Kawai ina tunanin abinda zanyi maka ne na faranta maka rai sosai. Kayi min komai a rayuwa har bana jin akwai matar da tayi dacen abokin rayuwa kamar ni. Har kunyarka nakan ji a raina in ga kamar bana yi maka abin da ya dace"
"Babu abinda nake so daga gareki da baki bani ba. Kin bani Asmau da duk abinda Asmau ta mallaka. Adduata kullum Allah Ya bamu zaman lafiya mai dorewa."
Ta amsa da amin hawayen da take boyewa suka gangaro. Ba su suka fito ba sai da Amatullah ta dawo daga islamiyya lokacin an kusa kiran magariba.
*****
Bayan ya tafi aiki da safe sannan Amatullah ta tafi makaranta ta gama gyaran gida ta dora abinci. Walida na son alala shiyasa da tayiwa Jikamshi nashi abincin ta gyara wake tayi musu alala mai cike da dafaffen kwai da ta yanka kanana da kayan hadi. Kafin ta iso ta gama komai da zatayi har da juice din kwakwa da ayaba.
Sai da tayi wanka Walida ta iso suka zauna hira. A hirar ne suna cin abinci Walida take neman shawararta akan abokin Col. Ishaq wanda shina soja ne kuma likita a nan asibitin barrack dinsu. Sunansa Hussaini, yana da mace daya da yara hudu. Asmau dadi ya kamata tace "ashe dai da gaske yake, Walida ki amince ni dai a dan haduwarmu a fuskanci mutumin kirki ne kuma mai addini. Yazo gidannan tare da Jikamshina yayi min tambayoyi a kanki. Dama shiru nayi sai kinji daga bakinsa."
Walida tace "wato ko kunyata ba kya ji kike cewa Jikamshinki"
"Don ma kada kice abin yayi yawa ne na tsaya a nan. Kinsan yadda nake ji dashi kuwa. Hmmm Jikamshi mijin Matar Jikamshi" tana magana tana kashewa Walida ido don tsokana. Ai kuwa ta kai mata dundu ta kauce suka saka dariya.
Walida tace "to ya batun matarsa? Kinsan yadda muke da Anti bana son harkar kishiya. Ko shekara batayi ba a gidanmu Abba ya saki Mama. Auren shekara tara ya iya yi mata saki uku lokaci guda."
Asmau tana tausayin Walida ta wannan fannin. Bata tashi tasan soyayyar mahaifiya ba kamar yadda suka sani ita da nata 'yan uwan. Tsakaninta da babarta sai anyi hutu. Shima babanta baya bari ta dade "Walida ba duka aka zama daya ba. Munje gidansa suma sun zo mana nan. Ni dai ina ganin kamar tana da kirki gaskiya duk da idan aka ce kishiya yanzu sai tunaninmu ya sauya. Ki dage da adduar neman zabin Allah. Idan mijinki ne sai kiga mun sha biki cikin kwanciyar hankali. Kada ki bari tsoron abinda baki da masaniya akansa ya sakaki ki amincewa da shi. Baki san inda alkhairinki yake ba"
"In sha Allah zan dage da yin istikhara. Allah Yasa yankewar zaman nawa a gida tazo. Nima nayi auren nan na huta da gorin Anti"
"Ke ba'a cewa haka, aure ai saboda Allah ake yinsa ba gorin kowa ba. Da baki samu da wuri ba ai ba laifinki bane. Auren wuri ko rashinsa jarabawace wallahi"
Murmushin yake kawai Walida tayi tace "Kada ki manta na girmeki da fin shekara. Ni fa ina jin kamshin shekara talatin. Gorin dangi anyi anyi har na saba dashi"
"Masu shekaru arbain suce me Walida? Nayi tunanin yanzu ke mai iya bawa wasu shawara ce idan kika duba rayuwarmu. Kowane bawa mace ko namiji akwai hanyar da Allah ke gwada imaninsa. Fatanmu kada Allah Yasa mu kasa hakuri har mu fadawa shirka."
Sun cigaba da hirarsu Asmau ta soma jin zuciyarta na tashi. Da gudu ta tashi ta tafi toilet din cikin falon ta rinka kwara amai kamar kayan cikinta zasu fita. Walida duk ta gama tsorata ta dafe mata baya tana sannu. Hirar da basu karasa ba kenan sai da ta sani nutsuwa Walida tace "ke kuma aka ake yi sai dai idona ya gane min. Meye nufinki da, wato sai ya fito na gani kamar kowa." Ta kalli saitin cikin Asmau "dan albarka ko yar albarka Mama Walida na gaisuwa. Wannan aman nasan so kake nasan da zamanka. Ranka ya dade dan soja"
Asmau tayi murmushi mai ciwo. Ina ma dai gaske ne, "Walida ba ciki bane wallahi, kwanakin nan wake baya zama a cikina. Rannan ma daga cin kosai sai amai"
"Ban gane ba ciki bane, gashi kince wake na saka ki amai. Kin gwada ne kinga babu?"
"Babu amfanin gwajin nasan babu"
Walida bata gaskata ta ba tace "kina tsarin iyali ne, me ya kaiki daga aure ki fara da bin tsarin nan na sai an gama amarci"
Asmau tace "kema kinsan bazan soma ba"
"To mene ne, Asmau kinsan dai zaki iya fada min. Ni na iya karanta miki nawa sirrin amma ke..."
Ganin bata ji dadi ba Asmau ta fada mata komai game da Col. Ishaq
"Wannan sirrinmu ne daga mu sai iyaye muka sani."
Sosai Walida taji tausayin Asmau. Su kuma kullum sai sun hadu da wani nau'i na jarabawa.
"Naji yar uwa kuma ba fahimta. Amma haihuwa ta Allah ce. Shi ya tabbatar bazai taba haihuwa bane? Ki gwada yin test a gida idan babu shikenan. Sai da kika fara aman ma na kula kinyi haske kin kara jiki. Da na zata duk na amarcin ne"
"Walida ina son haihuwa da Jikamshina amma shekarun da yayi a auren fari sun ishemu shaida. Kada ki saka min rai da abinda yayi min nisa"
Walida ta tashi ta dauki mayafi da purse dinta daga cikin jaka "kinga bari naje can wurin titi naga kamar akwai pharmacy. Zan siyo miki PT strip ki gwada. Idan babu komai ba sai ya sani ba"
Bata saurari wani batu daga Asmau ba ta fita. Wurin mintuna ashirin sai gata ta dawo tayi uban gumi. Tasha yawo domin inda ta zata pharmacy ne ba shi bane sai da aka kwatanta mata wani. Asmau ta dage bazata yi gwajin ba Walida ta ji haushi sosai. "Ko albarkacin tafiyar da nayi ai kya yi min kara ki gwada."
Da kyar da nuna bacin rai Asmau ta karbi tsinken gwajin guda biyu ta shiga bandaki. Bata fi minti uku ba Walida taji ta kwalla kara. A razane ta tashi tayi hanyar bandakin suka yi karo da Asmau da ta fito. Walida na cewa me ta faru ta rungumeta sosai sai kuma kuka da dariya a hade.
"Kin gani Walida *ciki* *cikin haihuwa* gareni. Wayyo Allah Jikamshina Allah Yana sane da bayinSa"
Wayarta ta tafi daukowa suna ta dariya ita da Walida. Har ta nemo sunansa zata kira Walida ta karbe wayar.
"Mutumin da ya kwashi shekaru yana neman haihuwa zaki fadawa kina da ciki a waya? Haba kawalli, ai yau ranarsa ce. Tashi zakiyi mu shiga kitchen ki hada masa special abinci mu sake gyara gidan nan. Idan da hali tambaye shi muje gidan kunshi naga naki ya kusa ficewa. Ana yi miki zanyi miki kitson barebari kanana"
Asmau tayi dariya tana shafa ciki. Wai cikin Jikamshinta ne a tare da ita. "Nayi girki sai dai na kara masa wani abin ko farfesu haka. Bari na tambayi kunshin"
Sai da tayi da gaske ta iya boyewa bata fada masa a waya ba. Bai hanata zuwa ba yace su je da Mal Sabo amma idan akwai layi sosai ta dawo gida baya son dawowa dinnan ya tarar bata nan. Cikin sauri sauri suka sake kimtsa gidan suka tafi.
Ana gama saka mata lallen Walida ta kama kanta tayi mata kitso. Shuku ne wani sabon style mai kyau da yake gashin nada cika sosai yayi mata kyau fuskarta ta kara fitowa. Sai da aka dauko Amatullah daga makaranta aka zo daukarsu. Har gida suka kai Walida Asmau tana ta yi mata godiya.
Suna zuwa gida tayiwa Amatullah wanka ta saka mata wasu kayan sannan ta barta a daki saboda zata kunna turaren wuta kada ya dameta. Tana gamawa taje ta bata lokaci wurin wanka da shiriyawa.
Karfe tara a gida tayiwa Col. Ishaq. Asmau da Amatullah suka taro shi tun daga bakin kofa. Binta yayi da kallo ya kasa dauke idonsa. Kullum tana masa kwalliya amm yau kam ba don Amatullah na wurin ba bai san me zaiyi ba. Tana rike da hannunsa suka tafi daki zata taimaka masa yayi wanka yace "Kamar na cinyeki Matar Jikamshi. Kinyi kyau da yawa"
Tayi murmushi "nagode amma ko zaka cinyeni ka bari ka fara cin abinci"
Kusan tura shi bandaki tayi don yaki tafiya sai tsokanarta yake. Da ya gama ya dawo falo inda ta zuba musu abinci a plate daya har Amatullah wanda hakan tsarinsa ne cin abincin dare tare. Suna ci yana kallon yadda take ta murmushi da fara'a ya ajiye cokalinsa yace "ki taimakeni ki fada min abinda yake ranki ya saka min ke cikin irin wannan farincikin."
"Sai mun gama cin abinci"
Ya kwabe fuska "bazan iya cigaba da cin abincin nan ba duk dadinsa. So nake kawai ki fada min. Tun dazu kin sa kwakwalwata ta tafi dogon bincike ta kasa samun amsa"
"Ka bari mu gama please"
Shi kam hakurinsa ya kare. Tun dazu yana kallo ko abincin kirki bata ci ba sai murmushi. Ya dan tabata ta kallo fuskarsa. A hankali yadda ita kadai zata ji yace "ko ki fada min yanzu ko mu kwashi kunya a gaban 'yarmu"
Yaji dadin abinda ta fada. Kamar yadda mata ke son a yabe su haka maza suke so suma matansu su yaba musu. Wayarta ya karba ya daukesu selfie suna yiwa juna murmushi. Bayan ya dauka yace "Matar Jikamshi kinyi kuka ko"
Asmau tayi saurin kai hannunta wurin idonta zata goge sauran hawayen da tayi lokacin da take tsaye yana bacci.
"Abu ne ya shigar min ido fa"
"Uhmm uhm Matar Jikamshi kada mu fara yiwa juna karya. Na kuma san halinki da saurin kuka. Fada min me kika saka a ranki."
A nutse yake kallonta ta sake shige masa tana jin wani hawayen na kokarin zuba.
"Kawai ina tunanin abinda zanyi maka ne na faranta maka rai sosai. Kayi min komai a rayuwa har bana jin akwai matar da tayi dacen abokin rayuwa kamar ni. Har kunyarka nakan ji a raina in ga kamar bana yi maka abin da ya dace"
"Babu abinda nake so daga gareki da baki bani ba. Kin bani Asmau da duk abinda Asmau ta mallaka. Adduata kullum Allah Ya bamu zaman lafiya mai dorewa."
Ta amsa da amin hawayen da take boyewa suka gangaro. Ba su suka fito ba sai da Amatullah ta dawo daga islamiyya lokacin an kusa kiran magariba.
*****
Bayan ya tafi aiki da safe sannan Amatullah ta tafi makaranta ta gama gyaran gida ta dora abinci. Walida na son alala shiyasa da tayiwa Jikamshi nashi abincin ta gyara wake tayi musu alala mai cike da dafaffen kwai da ta yanka kanana da kayan hadi. Kafin ta iso ta gama komai da zatayi har da juice din kwakwa da ayaba.
Sai da tayi wanka Walida ta iso suka zauna hira. A hirar ne suna cin abinci Walida take neman shawararta akan abokin Col. Ishaq wanda shina soja ne kuma likita a nan asibitin barrack dinsu. Sunansa Hussaini, yana da mace daya da yara hudu. Asmau dadi ya kamata tace "ashe dai da gaske yake, Walida ki amince ni dai a dan haduwarmu a fuskanci mutumin kirki ne kuma mai addini. Yazo gidannan tare da Jikamshina yayi min tambayoyi a kanki. Dama shiru nayi sai kinji daga bakinsa."
Walida tace "wato ko kunyata ba kya ji kike cewa Jikamshinki"
"Don ma kada kice abin yayi yawa ne na tsaya a nan. Kinsan yadda nake ji dashi kuwa. Hmmm Jikamshi mijin Matar Jikamshi" tana magana tana kashewa Walida ido don tsokana. Ai kuwa ta kai mata dundu ta kauce suka saka dariya.
Walida tace "to ya batun matarsa? Kinsan yadda muke da Anti bana son harkar kishiya. Ko shekara batayi ba a gidanmu Abba ya saki Mama. Auren shekara tara ya iya yi mata saki uku lokaci guda."
Asmau tana tausayin Walida ta wannan fannin. Bata tashi tasan soyayyar mahaifiya ba kamar yadda suka sani ita da nata 'yan uwan. Tsakaninta da babarta sai anyi hutu. Shima babanta baya bari ta dade "Walida ba duka aka zama daya ba. Munje gidansa suma sun zo mana nan. Ni dai ina ganin kamar tana da kirki gaskiya duk da idan aka ce kishiya yanzu sai tunaninmu ya sauya. Ki dage da adduar neman zabin Allah. Idan mijinki ne sai kiga mun sha biki cikin kwanciyar hankali. Kada ki bari tsoron abinda baki da masaniya akansa ya sakaki ki amincewa da shi. Baki san inda alkhairinki yake ba"
"In sha Allah zan dage da yin istikhara. Allah Yasa yankewar zaman nawa a gida tazo. Nima nayi auren nan na huta da gorin Anti"
"Ke ba'a cewa haka, aure ai saboda Allah ake yinsa ba gorin kowa ba. Da baki samu da wuri ba ai ba laifinki bane. Auren wuri ko rashinsa jarabawace wallahi"
Murmushin yake kawai Walida tayi tace "Kada ki manta na girmeki da fin shekara. Ni fa ina jin kamshin shekara talatin. Gorin dangi anyi anyi har na saba dashi"
"Masu shekaru arbain suce me Walida? Nayi tunanin yanzu ke mai iya bawa wasu shawara ce idan kika duba rayuwarmu. Kowane bawa mace ko namiji akwai hanyar da Allah ke gwada imaninsa. Fatanmu kada Allah Yasa mu kasa hakuri har mu fadawa shirka."
Sun cigaba da hirarsu Asmau ta soma jin zuciyarta na tashi. Da gudu ta tashi ta tafi toilet din cikin falon ta rinka kwara amai kamar kayan cikinta zasu fita. Walida duk ta gama tsorata ta dafe mata baya tana sannu. Hirar da basu karasa ba kenan sai da ta sani nutsuwa Walida tace "ke kuma aka ake yi sai dai idona ya gane min. Meye nufinki da, wato sai ya fito na gani kamar kowa." Ta kalli saitin cikin Asmau "dan albarka ko yar albarka Mama Walida na gaisuwa. Wannan aman nasan so kake nasan da zamanka. Ranka ya dade dan soja"
Asmau tayi murmushi mai ciwo. Ina ma dai gaske ne, "Walida ba ciki bane wallahi, kwanakin nan wake baya zama a cikina. Rannan ma daga cin kosai sai amai"
"Ban gane ba ciki bane, gashi kince wake na saka ki amai. Kin gwada ne kinga babu?"
"Babu amfanin gwajin nasan babu"
Walida bata gaskata ta ba tace "kina tsarin iyali ne, me ya kaiki daga aure ki fara da bin tsarin nan na sai an gama amarci"
Asmau tace "kema kinsan bazan soma ba"
"To mene ne, Asmau kinsan dai zaki iya fada min. Ni na iya karanta miki nawa sirrin amma ke..."
Ganin bata ji dadi ba Asmau ta fada mata komai game da Col. Ishaq
"Wannan sirrinmu ne daga mu sai iyaye muka sani."
Sosai Walida taji tausayin Asmau. Su kuma kullum sai sun hadu da wani nau'i na jarabawa.
"Naji yar uwa kuma ba fahimta. Amma haihuwa ta Allah ce. Shi ya tabbatar bazai taba haihuwa bane? Ki gwada yin test a gida idan babu shikenan. Sai da kika fara aman ma na kula kinyi haske kin kara jiki. Da na zata duk na amarcin ne"
"Walida ina son haihuwa da Jikamshina amma shekarun da yayi a auren fari sun ishemu shaida. Kada ki saka min rai da abinda yayi min nisa"
Walida ta tashi ta dauki mayafi da purse dinta daga cikin jaka "kinga bari naje can wurin titi naga kamar akwai pharmacy. Zan siyo miki PT strip ki gwada. Idan babu komai ba sai ya sani ba"
Bata saurari wani batu daga Asmau ba ta fita. Wurin mintuna ashirin sai gata ta dawo tayi uban gumi. Tasha yawo domin inda ta zata pharmacy ne ba shi bane sai da aka kwatanta mata wani. Asmau ta dage bazata yi gwajin ba Walida ta ji haushi sosai. "Ko albarkacin tafiyar da nayi ai kya yi min kara ki gwada."
Da kyar da nuna bacin rai Asmau ta karbi tsinken gwajin guda biyu ta shiga bandaki. Bata fi minti uku ba Walida taji ta kwalla kara. A razane ta tashi tayi hanyar bandakin suka yi karo da Asmau da ta fito. Walida na cewa me ta faru ta rungumeta sosai sai kuma kuka da dariya a hade.
"Kin gani Walida *ciki* *cikin haihuwa* gareni. Wayyo Allah Jikamshina Allah Yana sane da bayinSa"
Wayarta ta tafi daukowa suna ta dariya ita da Walida. Har ta nemo sunansa zata kira Walida ta karbe wayar.
"Mutumin da ya kwashi shekaru yana neman haihuwa zaki fadawa kina da ciki a waya? Haba kawalli, ai yau ranarsa ce. Tashi zakiyi mu shiga kitchen ki hada masa special abinci mu sake gyara gidan nan. Idan da hali tambaye shi muje gidan kunshi naga naki ya kusa ficewa. Ana yi miki zanyi miki kitson barebari kanana"
Asmau tayi dariya tana shafa ciki. Wai cikin Jikamshinta ne a tare da ita. "Nayi girki sai dai na kara masa wani abin ko farfesu haka. Bari na tambayi kunshin"
Sai da tayi da gaske ta iya boyewa bata fada masa a waya ba. Bai hanata zuwa ba yace su je da Mal Sabo amma idan akwai layi sosai ta dawo gida baya son dawowa dinnan ya tarar bata nan. Cikin sauri sauri suka sake kimtsa gidan suka tafi.
Ana gama saka mata lallen Walida ta kama kanta tayi mata kitso. Shuku ne wani sabon style mai kyau da yake gashin nada cika sosai yayi mata kyau fuskarta ta kara fitowa. Sai da aka dauko Amatullah daga makaranta aka zo daukarsu. Har gida suka kai Walida Asmau tana ta yi mata godiya.
Suna zuwa gida tayiwa Amatullah wanka ta saka mata wasu kayan sannan ta barta a daki saboda zata kunna turaren wuta kada ya dameta. Tana gamawa taje ta bata lokaci wurin wanka da shiriyawa.
Karfe tara a gida tayiwa Col. Ishaq. Asmau da Amatullah suka taro shi tun daga bakin kofa. Binta yayi da kallo ya kasa dauke idonsa. Kullum tana masa kwalliya amm yau kam ba don Amatullah na wurin ba bai san me zaiyi ba. Tana rike da hannunsa suka tafi daki zata taimaka masa yayi wanka yace "Kamar na cinyeki Matar Jikamshi. Kinyi kyau da yawa"
Tayi murmushi "nagode amma ko zaka cinyeni ka bari ka fara cin abinci"
Kusan tura shi bandaki tayi don yaki tafiya sai tsokanarta yake. Da ya gama ya dawo falo inda ta zuba musu abinci a plate daya har Amatullah wanda hakan tsarinsa ne cin abincin dare tare. Suna ci yana kallon yadda take ta murmushi da fara'a ya ajiye cokalinsa yace "ki taimakeni ki fada min abinda yake ranki ya saka min ke cikin irin wannan farincikin."
"Sai mun gama cin abinci"
Ya kwabe fuska "bazan iya cigaba da cin abincin nan ba duk dadinsa. So nake kawai ki fada min. Tun dazu kin sa kwakwalwata ta tafi dogon bincike ta kasa samun amsa"
"Ka bari mu gama please"
Shi kam hakurinsa ya kare. Tun dazu yana kallo ko abincin kirki bata ci ba sai murmushi. Ya dan tabata ta kallo fuskarsa. A hankali yadda ita kadai zata ji yace "ko ki fada min yanzu ko mu kwashi kunya a gaban 'yarmu"