Sashe 56
Abinda Ake Gudu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Motarsu ce a gaba Zubaida tayiwa Jafar kwatance. Su Asmau ma jiki ya mutu suka dena hirar saboda ganin yadda yanayinta ya canja. Asmau tana zancen zuci tace kada Allah Ya kawo ranar da Amatullah zata kyamaceta irin yadda Zubaida take yi a yanzu.
Gidan yana nan yadda yake ko fenti ba'a canja ba. 'Yan bakin kasuwa suna kallon abin mamaki. Motoci irin wadannan a kofar gidan Uwargida. Kuma gashi harda mata bare ace wasu kadangarun barikin ne suka zo neman 'yan matan gidan.
Asmau da Zubaida aka rasa me fara shiga. Ita Zubaida ma hawaye take yi har Kawu Garzali ya gani. Da sauri yazo ya karbi baby dinta mai suna Shuaibu suna kiransa Aiman sannan ya rike hannunta suka fara shiga. Zuciyar Asmau ta tsinke, yanzu haka Jikamshi zai shiga gidannan. Allah Yasa kada shi ko Hajiya wani yace a fasa auren.
Zuga guda suka shiga da sallamarsu. Matan a gaba maza a bayansu. Kaya ne tarkace kala kala a tsakar gidan. Wasu matan na wanki wasu suna girki. Kowacce da sabgar gabanta. Kadan a ciki Asmau ta gane. Duk barin abinda suke yo suka yi kallo ya dawo kan baki. Daga kofar dakin Uwargida Bulayi ya fito. Mutumin da ya fara kawota gidan nan. Dama can a dattijo ta san shi. Yanzu kuwa tsufa ya kara bayyana a tattare dashi. Yana kokarin zura takalmansa ne idonsa ya sauka akan Zubaida. Fuskarsa ba karamin mamaki ta nuna ba yace "Zuby???"
Ranta a dagule yake dama ta harare shi "Zubyn uwarka" a duniya yana cikin mutanen da ta tsana. Duk yarinyar da aka kawo gidan sai yayi amfani da ita kafin kasuwarta ta bude.
Maimakon ta ga bacin rai a fuskarsa sai ya washe baki cike da fara'a yace
"Shegiya ita ce kuwa, kina nan da bakinki kamar reza"
Cikin dakin ya koma da sauri har yana tuntube. Suna jin muryarsa yana kiran Uwargida tazo ga Zuby ta dawo. Zubaida ta ji muryar mahaifiyarta tana cewa "Bulayi kada kayi min wasan da zai tayar min da hawan jini"
"Yasin da gaske nake, bari na kamaki muje wajen"
Kunya ta kara kama Zubaida, yanzu haka zasu fito hannu da hannu kamar wasu mata da miji a gaban mutanen nan masu daraja a idonta. Dukkansu kallon kofar suke zasu ga wannan Uwargidan ga wadanda basu taba ganinta ba. Bulayi ne ya fara fitowa hannunsa rike da sanda yana cewa "yi hankali da matattakalar kofar"
Rike da sanda ta fito wacce Bulayi ya daga mata daga waje yana mata jagora. Tana nan da tsayinta fuskar nan tayi wani irin dabbara dabbara saboda mayukan bleaching da taji a baya. Sanye take da tubarau baki wuluk irin na makafi. Tana mika hannu cikin iska alamar lalube tace
"Zuby kina ina?"
Innalillahi wa inna ilaihi raji'un. Zubaida bata san lokacin da ta saki hannun Kawu Garzali ba ta tafi wurin babarta tana kuka
"Mama makancewa kika yi? Wayyo Allah na, kinga ni fa jikokinki na kawo miki nayi aure. 'Ya'yana hudu. Mama ki bude ido ki gansu don Allah"
Uwargida tayi dan murmushi tana rungume da 'yarta. Hawaye ya zubo mata tana ta shafa fuskar Zubaida tace "Ashe zamu gana kafin na mutu Zubaida. Allah nagode Maka. Ina yaran? Wane dan albarkan ne ya rufa min asiri ya aureki? Kinga yadda Allah Ya mayar dani ko. Karyar karuwanci ta kare bani da wani mataimaki sai Allah sai Bulayi da bai gujeni ba"
Zubaida ta kalle shi sai taji kunyar zagin da tayi masa. A yadda taga mahaifiyarta ta kara tsufa da yankwanewa sai ta godewa Allah da Umma ta dage lallai sai tazo. Bulayi ne yace "Uwargida tare da baki take fa. Ina jin surukanta ne mu shiga daga ciki ko kuma ina zuwa dai" dakin ya koma ya dauko tabarmi gudu uku. Kamar hadin baki Qasim da Col. Ishaq suka ki zama. In da sabo tsayuwa ba komai bace wurin soja da dan sanda. Sai akayi dace kyamarsu tazo daya basa son zama a tabarmar da ta fito daga dakin matar.
Sauran dai sun zauna sannan Zubaida ta fara yi mata bayanin kowa. Yaranta kuwa sai da Uwargida tabi tana shafasu tana binsu da kiss a fuska. Manyan biyu mace da namiji dai kyankyaminsu suke. Tana yi suna gogewa duk ta yaba musu yawu. Da Zubaida tace tare suke da Asmau Uwargida ta mika hannu zata kamata. Balayi yace "Yar dabas kin canja Yasin. Jikinki duk ya murje kinyi fresh. Dama naso naga kama to kuma sai naga ta yanzu tafi ta da kyau da daukar ido."
Wani mugun kallo Col. Ishaq ya sakar masa wanda ya girgiza har hanjin cikinsa. Ba arziki yayi shiru. Asmau ta dan matsa gaba Uwargida ta kama hannunta.
"Nayi sanadiyar lalacewar 'ya'yan mutane da yawa Yar dabas, iyayenki har nan sun zo nemanki. Nagodewa Allah da baki kama sa'a kamar yadda naso ba. Hakkin wadancan shegun kadai ya isheni. Ni shaida ce akanki har kika bar gidannan namiji bai taba zuwa kofar dakinki ba. Ke kam kinji dadi 'yan uwa basu kyamaceki ba har Allah Yasa rayuwarki ta koma kan layi. Me kika haifa?
Tausayi Uwargida ta rinka basu. Asmau ta soma kuka saboda yadda ta tuna Uwargida da iya gayu duk girmanta. Yanzu kuwa sai da dauriya zaka iya zama kusa da ita saboda warin jiki. Su Umma sun gama gaisawa da Uwargida sai Haj Lubabatu ta dan yunkura zata tashi. Col. Ishaq yace "Hajiya kafar ce?"
Bata bashi amsa ba sai matsawa da tayi gaban Uwargida ta zauna kusa da Zubaida tana kare mata kallo. Kuka sosai ya kwace mata tace "Habiba"
Uwargida ta fara mika hannu inda taji kira. Rabonta da amsa wannan sunan tun ranar da ta baro garinsu. Hannunta har rawa yake tana ta mika shi ko zata kama mai kiran tace "wace ce don Allah, babu wanda yasan sunana sai 'yan garinmu"
Hajiya sai kuka ta kara shigewa kusa da Uwargida. Col. Ishaq ji yake kamar ya janyota. Me ya hadata da wannan matar. Hannuwanta duka biyu ta rike
"Lubabatu ce, Luban gidan Sarkin dorin Jikamshi"
Salati sosai Uwargida ta saka kafin ta rungume Hajiya. Babu kyama Hajiya ta rungumeta itama suka barke da kuka. Kowa sai kallosu yake. Matan gidan sun fito ganin kwaf Qasim ya daka musu tsawar da ta kidimasu suka bar wurin suna karo da juna.
Uwargida ta share majina da kasan zaninta tace "Allah mai iko, ashe zan sake ganin na gida. Luba ina Baba da Inna, ina 'yan uwana?"
Cikin kuka Hajiya tace "Liman da Inna sun dade da rasuwa. Yayarki Indo ma babu ita. Sauran 'yan uwanki duk suna nan an tara 'ya'ya da jikoki"
"Allahu Akbar, Allah Ya jikanku Baba, Allah Yasa sun yafe min kafin su rasu"
Tana kuka ta labarta musu yadda almajirin Liman yayi mata ciki ashe ma fyade ne yayi mata kuma ya gargadeta kada ta fada har ciki ya bullo. Babu uzuri ko neman ba'asi iyayenta suka tsine mata. Wannan kuskure ne babba. Yana da matukar amfani jurewa wajen kula da yara idan sunyi kuskure domin a toshe kofar gaba. Tunda ta fiti take aikatau da ayyukan wahala domin taci abinci. A haka cikin ya bare tana yawo a gari. A wani gidan aikinta ne a Bauchi maigidan ya kuma yi mata fyade da ta fada matarsa tayi mata duka duk da lokacin shekarunta sunyi gaba don da jima tana rayuwar kunci da wahala. Maigida ya karyata kamar yadda aka saba ji. Shine da ta fito ta sami uwardaki. Bata zubar da cikin ba ta haifi Zubaida. Da girmanta ta fara sana'ar karuwanci kuma tace ta gwada rashin imani kamar yadda mutane suka gwada mata. Sai shekaru biyu da suka wuce da ta kamu da lalurar ido tayu nadamar rayuwarta. Duk matan gidan sun dena bata kudin haya ga rashin abinci. Ta kare da bawa mutane shawara da su rinka taimakawa masu raunin imani da wadanda ke cikin matsanancin hali don gujewa samuwar karin mugayen dabi'u a cikin jamaa.
Su Mama duk anyi kukan tausayin labarin Uwargida da kuma dadin handala da Asmau tayi dacen haduwa da mutane nagari. Wannan kuma zamu iya cewa harda adduar da suke yi mata ba tsinuwa ko zagi ba. A gidan aka bar Zubaida da Kawu Garzali. Sun yanke shawarar idan zasu koma Kano a tafi da ita sai a kaita Jikamshi taga 'yan uwanta ko da basa maraba da dawowarta.
*****
Daga nan gidan Rashida suka wuce. Dama tasan da zuwansu. Sada ma yana gida yana jira ga su Abba duk an zama samari. Cikin gidan aka yi musu shimfida mazan kuma suna dakin nan da Asmau ta taba zama. Tana shiga gidan sai kuka da ta tuna lokacin da ta zauna ga ciki ga rashin iyaye a kusa. A falo taga Sada ya kalleta fuskarsa dauke da murmushi yace
"Asmau kece kuwa?"
Tana kuka ta durkusa har kasa ta gaishe shi. Sada ne mutum na farko da ya fara taimakonta a rayuwa sosai bayan Zubaida mai bata shawarar kada ta zabi gurbatacciyar rayuwa. Wurinsu Abdulhalim yaje inda aka ajiye musu kayan abinci. Sai da suka yi sallah suka ci abincin.
A ciki suma matan sallar suka yi aka ci abinci. Nan hira ta barke ana tuna baya ana kuka da dariya. Rashida tace "yakamata watarana muje kiga Yaya Tagwai fa"
Asmau tayi murmushi, Yaya Tagwai ai ta janyo mata kara shiga garari. Cikin yaran kuwa babu wanda ya tuna ta sai Abba. Sai da suka yi laasar a ranar dai suka kama hanyar Jos. Rashida da Sada sai lokacin biki zasu taho Kano.
Sun sha tafiya jiki kuma ya fada saboda zaman mota. Duka matan a gidan Mami akayi musu masauki sai gari ya waye zasu gidan Zulaiha. Asmau ta damu sosai da ita saboda dena samunta da tayi a waya. Col. Ishaq ne ya samarwa mazan masauki a cikin barikinsu na sojoji dake garin. Shi da Matarsa sai dare suka sami damar yin waya aka biya bashin soyayyar da ba'a yi ba a ranar.
Gidan yana nan yadda yake ko fenti ba'a canja ba. 'Yan bakin kasuwa suna kallon abin mamaki. Motoci irin wadannan a kofar gidan Uwargida. Kuma gashi harda mata bare ace wasu kadangarun barikin ne suka zo neman 'yan matan gidan.
Asmau da Zubaida aka rasa me fara shiga. Ita Zubaida ma hawaye take yi har Kawu Garzali ya gani. Da sauri yazo ya karbi baby dinta mai suna Shuaibu suna kiransa Aiman sannan ya rike hannunta suka fara shiga. Zuciyar Asmau ta tsinke, yanzu haka Jikamshi zai shiga gidannan. Allah Yasa kada shi ko Hajiya wani yace a fasa auren.
Zuga guda suka shiga da sallamarsu. Matan a gaba maza a bayansu. Kaya ne tarkace kala kala a tsakar gidan. Wasu matan na wanki wasu suna girki. Kowacce da sabgar gabanta. Kadan a ciki Asmau ta gane. Duk barin abinda suke yo suka yi kallo ya dawo kan baki. Daga kofar dakin Uwargida Bulayi ya fito. Mutumin da ya fara kawota gidan nan. Dama can a dattijo ta san shi. Yanzu kuwa tsufa ya kara bayyana a tattare dashi. Yana kokarin zura takalmansa ne idonsa ya sauka akan Zubaida. Fuskarsa ba karamin mamaki ta nuna ba yace "Zuby???"
Ranta a dagule yake dama ta harare shi "Zubyn uwarka" a duniya yana cikin mutanen da ta tsana. Duk yarinyar da aka kawo gidan sai yayi amfani da ita kafin kasuwarta ta bude.
Maimakon ta ga bacin rai a fuskarsa sai ya washe baki cike da fara'a yace
"Shegiya ita ce kuwa, kina nan da bakinki kamar reza"
Cikin dakin ya koma da sauri har yana tuntube. Suna jin muryarsa yana kiran Uwargida tazo ga Zuby ta dawo. Zubaida ta ji muryar mahaifiyarta tana cewa "Bulayi kada kayi min wasan da zai tayar min da hawan jini"
"Yasin da gaske nake, bari na kamaki muje wajen"
Kunya ta kara kama Zubaida, yanzu haka zasu fito hannu da hannu kamar wasu mata da miji a gaban mutanen nan masu daraja a idonta. Dukkansu kallon kofar suke zasu ga wannan Uwargidan ga wadanda basu taba ganinta ba. Bulayi ne ya fara fitowa hannunsa rike da sanda yana cewa "yi hankali da matattakalar kofar"
Rike da sanda ta fito wacce Bulayi ya daga mata daga waje yana mata jagora. Tana nan da tsayinta fuskar nan tayi wani irin dabbara dabbara saboda mayukan bleaching da taji a baya. Sanye take da tubarau baki wuluk irin na makafi. Tana mika hannu cikin iska alamar lalube tace
"Zuby kina ina?"
Innalillahi wa inna ilaihi raji'un. Zubaida bata san lokacin da ta saki hannun Kawu Garzali ba ta tafi wurin babarta tana kuka
"Mama makancewa kika yi? Wayyo Allah na, kinga ni fa jikokinki na kawo miki nayi aure. 'Ya'yana hudu. Mama ki bude ido ki gansu don Allah"
Uwargida tayi dan murmushi tana rungume da 'yarta. Hawaye ya zubo mata tana ta shafa fuskar Zubaida tace "Ashe zamu gana kafin na mutu Zubaida. Allah nagode Maka. Ina yaran? Wane dan albarkan ne ya rufa min asiri ya aureki? Kinga yadda Allah Ya mayar dani ko. Karyar karuwanci ta kare bani da wani mataimaki sai Allah sai Bulayi da bai gujeni ba"
Zubaida ta kalle shi sai taji kunyar zagin da tayi masa. A yadda taga mahaifiyarta ta kara tsufa da yankwanewa sai ta godewa Allah da Umma ta dage lallai sai tazo. Bulayi ne yace "Uwargida tare da baki take fa. Ina jin surukanta ne mu shiga daga ciki ko kuma ina zuwa dai" dakin ya koma ya dauko tabarmi gudu uku. Kamar hadin baki Qasim da Col. Ishaq suka ki zama. In da sabo tsayuwa ba komai bace wurin soja da dan sanda. Sai akayi dace kyamarsu tazo daya basa son zama a tabarmar da ta fito daga dakin matar.
Sauran dai sun zauna sannan Zubaida ta fara yi mata bayanin kowa. Yaranta kuwa sai da Uwargida tabi tana shafasu tana binsu da kiss a fuska. Manyan biyu mace da namiji dai kyankyaminsu suke. Tana yi suna gogewa duk ta yaba musu yawu. Da Zubaida tace tare suke da Asmau Uwargida ta mika hannu zata kamata. Balayi yace "Yar dabas kin canja Yasin. Jikinki duk ya murje kinyi fresh. Dama naso naga kama to kuma sai naga ta yanzu tafi ta da kyau da daukar ido."
Wani mugun kallo Col. Ishaq ya sakar masa wanda ya girgiza har hanjin cikinsa. Ba arziki yayi shiru. Asmau ta dan matsa gaba Uwargida ta kama hannunta.
"Nayi sanadiyar lalacewar 'ya'yan mutane da yawa Yar dabas, iyayenki har nan sun zo nemanki. Nagodewa Allah da baki kama sa'a kamar yadda naso ba. Hakkin wadancan shegun kadai ya isheni. Ni shaida ce akanki har kika bar gidannan namiji bai taba zuwa kofar dakinki ba. Ke kam kinji dadi 'yan uwa basu kyamaceki ba har Allah Yasa rayuwarki ta koma kan layi. Me kika haifa?
Tausayi Uwargida ta rinka basu. Asmau ta soma kuka saboda yadda ta tuna Uwargida da iya gayu duk girmanta. Yanzu kuwa sai da dauriya zaka iya zama kusa da ita saboda warin jiki. Su Umma sun gama gaisawa da Uwargida sai Haj Lubabatu ta dan yunkura zata tashi. Col. Ishaq yace "Hajiya kafar ce?"
Bata bashi amsa ba sai matsawa da tayi gaban Uwargida ta zauna kusa da Zubaida tana kare mata kallo. Kuka sosai ya kwace mata tace "Habiba"
Uwargida ta fara mika hannu inda taji kira. Rabonta da amsa wannan sunan tun ranar da ta baro garinsu. Hannunta har rawa yake tana ta mika shi ko zata kama mai kiran tace "wace ce don Allah, babu wanda yasan sunana sai 'yan garinmu"
Hajiya sai kuka ta kara shigewa kusa da Uwargida. Col. Ishaq ji yake kamar ya janyota. Me ya hadata da wannan matar. Hannuwanta duka biyu ta rike
"Lubabatu ce, Luban gidan Sarkin dorin Jikamshi"
Salati sosai Uwargida ta saka kafin ta rungume Hajiya. Babu kyama Hajiya ta rungumeta itama suka barke da kuka. Kowa sai kallosu yake. Matan gidan sun fito ganin kwaf Qasim ya daka musu tsawar da ta kidimasu suka bar wurin suna karo da juna.
Uwargida ta share majina da kasan zaninta tace "Allah mai iko, ashe zan sake ganin na gida. Luba ina Baba da Inna, ina 'yan uwana?"
Cikin kuka Hajiya tace "Liman da Inna sun dade da rasuwa. Yayarki Indo ma babu ita. Sauran 'yan uwanki duk suna nan an tara 'ya'ya da jikoki"
"Allahu Akbar, Allah Ya jikanku Baba, Allah Yasa sun yafe min kafin su rasu"
Tana kuka ta labarta musu yadda almajirin Liman yayi mata ciki ashe ma fyade ne yayi mata kuma ya gargadeta kada ta fada har ciki ya bullo. Babu uzuri ko neman ba'asi iyayenta suka tsine mata. Wannan kuskure ne babba. Yana da matukar amfani jurewa wajen kula da yara idan sunyi kuskure domin a toshe kofar gaba. Tunda ta fiti take aikatau da ayyukan wahala domin taci abinci. A haka cikin ya bare tana yawo a gari. A wani gidan aikinta ne a Bauchi maigidan ya kuma yi mata fyade da ta fada matarsa tayi mata duka duk da lokacin shekarunta sunyi gaba don da jima tana rayuwar kunci da wahala. Maigida ya karyata kamar yadda aka saba ji. Shine da ta fito ta sami uwardaki. Bata zubar da cikin ba ta haifi Zubaida. Da girmanta ta fara sana'ar karuwanci kuma tace ta gwada rashin imani kamar yadda mutane suka gwada mata. Sai shekaru biyu da suka wuce da ta kamu da lalurar ido tayu nadamar rayuwarta. Duk matan gidan sun dena bata kudin haya ga rashin abinci. Ta kare da bawa mutane shawara da su rinka taimakawa masu raunin imani da wadanda ke cikin matsanancin hali don gujewa samuwar karin mugayen dabi'u a cikin jamaa.
Su Mama duk anyi kukan tausayin labarin Uwargida da kuma dadin handala da Asmau tayi dacen haduwa da mutane nagari. Wannan kuma zamu iya cewa harda adduar da suke yi mata ba tsinuwa ko zagi ba. A gidan aka bar Zubaida da Kawu Garzali. Sun yanke shawarar idan zasu koma Kano a tafi da ita sai a kaita Jikamshi taga 'yan uwanta ko da basa maraba da dawowarta.
*****
Daga nan gidan Rashida suka wuce. Dama tasan da zuwansu. Sada ma yana gida yana jira ga su Abba duk an zama samari. Cikin gidan aka yi musu shimfida mazan kuma suna dakin nan da Asmau ta taba zama. Tana shiga gidan sai kuka da ta tuna lokacin da ta zauna ga ciki ga rashin iyaye a kusa. A falo taga Sada ya kalleta fuskarsa dauke da murmushi yace
"Asmau kece kuwa?"
Tana kuka ta durkusa har kasa ta gaishe shi. Sada ne mutum na farko da ya fara taimakonta a rayuwa sosai bayan Zubaida mai bata shawarar kada ta zabi gurbatacciyar rayuwa. Wurinsu Abdulhalim yaje inda aka ajiye musu kayan abinci. Sai da suka yi sallah suka ci abincin.
A ciki suma matan sallar suka yi aka ci abinci. Nan hira ta barke ana tuna baya ana kuka da dariya. Rashida tace "yakamata watarana muje kiga Yaya Tagwai fa"
Asmau tayi murmushi, Yaya Tagwai ai ta janyo mata kara shiga garari. Cikin yaran kuwa babu wanda ya tuna ta sai Abba. Sai da suka yi laasar a ranar dai suka kama hanyar Jos. Rashida da Sada sai lokacin biki zasu taho Kano.
Sun sha tafiya jiki kuma ya fada saboda zaman mota. Duka matan a gidan Mami akayi musu masauki sai gari ya waye zasu gidan Zulaiha. Asmau ta damu sosai da ita saboda dena samunta da tayi a waya. Col. Ishaq ne ya samarwa mazan masauki a cikin barikinsu na sojoji dake garin. Shi da Matarsa sai dare suka sami damar yin waya aka biya bashin soyayyar da ba'a yi ba a ranar.