Sashe 17
Abinda Ake Gudu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A ranta kuwa tace sai dai na fadawa wani. Rabe-raben mutane ta fannin sha'awa tuni ta san shi a posts din waya. Muryarsa wadda take rawa taji a kusa da ita.
"Ina cikin tashin hankali da son kasancewa tare dake. Wallahi bazan iya kaimu Kano ba a yanayin da nake ji yanzu musamman da kike zaune kusa dani. Ki taimakeni ko sau daya ne na kawar da wannan masifaffen tunanin."
Kofar motar ta kama a gigice hawaye na wanke mata fuska jin ya saka lock. Sanyin AC bai hanata gumi ba.
"Yaya Abubakar ka rufa min asiri ka mayar dani gidan Anti Bintu. Duk ni na jawo wannan matsalar da na rinka saka kaya masu matse jiki ina zama kusa da kai. Sharrin shaidan ne da na zuciya don Allah kayi hakuri nan da wata hudu zamuyi aure fa".
Magiyar da take masa jin muryarta yake kamar tana masa busa. Wannan wace irin masifa ce??? Shiyasa tun a da yake nisanta daga duk abinda zai jawo masa sha'awa tunda ya gane yanayinsa.
Hawaye ne ya zubo a idonsa wanda bai san dalilinsu ba.
"Ke kadai nake so kuma da ke kadai na amince Asmy. Idan baki amince ba wallahi nayi miki rantsuwa zan nemi wata. Bani da lafiya duk a dalilin sonki da son kusantarki. Ko kinsan satin nan ko sau daya banje wurin aiki ba saboda halin dana tsinci kaina a ciki".
Kuka Asmau take yi sosai gashi tausayinsa ya mamaye zuciyarta.
" Yaya kada mu aikata haram. Kuma idan ka rabani da abinda duk budurwa take takama dashi yaya zanyi?"
Hannuwanta duka biyun ya rike. "Asmy kinsan dai nine mai aurenki ko? Kuma ni ba wai zanyi miki yadda zaki tashi daga budurwa bane. Akwai yadda zanyi babu wanda zai ce namiji ya kusanceki. Ki taimake ni.
Har bincike nayi wasu malaman sunce kudin aure daidai yake da sadaki. Ko baki ga iyayenmu maza ke zuwa ba ayi a gaban shaidu. Al'ada ce kawai sake taruwar da ake yi a daura aure. Amma yanzu ma a haka ni da ke matsayin mata da miji muke." Shi da yake fada mata hakan ya tabbatar karya yake yi amma babu yadda ya iya da zuciyarsa.
Roko da rarrashi haka ya rinka yiwa Asmau tana kuka haka ta amince saboda tausayin da ya bata da tsoron kada ya nemi wata.
Wani hotel ya sama musu kuma da yake duk sunyi shigar mutunci babu mai cewa ba ma'auratan gaske bane. Haka ya karbi mukullin dakin zuciyarsa tana kwabarsa da abinda yake shirin aikatawa amma gangar jikinsa bazata iya hakuri ba.
A kofar dakin da kyar Asmau ta shiga. Yana rufe kofar ta kara fashewa da kuka. Abubakar yayi nisa duk da yana tausayinta hakan bai hanashi biyan bukakarsa ba. Alkawarin da yayi mata na yin dabara kada ta rasa budurcinta tuni ya manta dashi.
Sai da komai ya kammala yaji kamar tashin hankalin duniya duk ya kare a kansa. Gefen gado ya koma ya dafe kai ya rasa inda zaisa kansa.
Asmau tana kwance sai sautin kukanta ke tashi. Ga ciwo ga bakinciki.
Sun kusa awa daya sannan yayi wanka ya umarceta da itama tayi. Wannan masifa da yawa take...Ya Allah Ka tsare mana imaninmu.
Haka suka fito babu wanda yake yiwa dan uwansa magana. Ya biya kudin hotel suka wuce Kano yana ta zabga gudu a hanya.
A bakin gate din gidansu ya sauketa zuciyarsa tana kuna. Ya rasa me yake ji game da Asmau. Ko kayanta bai taimaka mata da dauka ba haka ta fito dasu ta shige gida fuska a kumbure.
Su Umma sai murna suke yi ta dawo amma ganin yanayinta Umman ta tsorata tana tambayarta abinda ya faru.
Asmau ta fashe da kuka ta rungume mahaifiyarta. Yau taci amanar addininta kuma taci amanar Umma.
Taruwa suka yi a kanta Jafar ya taba jikinta. Zazzabi ne sosai a jikin hatta kanta ya dau zafi.
Ya danyi murmushi "Umma wannan 'yar taki ta fiye shagwaba da raki. Daga zazzabi kuma sai kuka?"
Sai a lokacin tayi dan murmushi ganin cewa idan ta cigaba da kukan zata tonawa kanta asiri.
"Yaya Jafar ji nake kamar kan zai tsage biyu"
Umma ta tasheta tsaye
"Ki dena tsorata ni irin haka Asmau. Baki ji yadda gabana ya fadi ba. Muje ki dan watsa ruwa sai kici abinci kisha magani. Ina Abubakar din?"
Har zuciyarta ta razana jin an ambaci sunansa.
"Ya tafi gida amma yace zai shigo ku gaisa anjima".
"Babu komai ai kun sha hanya ga rana. Allah Yasa ba kukan nan naki kika rinka yi masa ba saboda baki jindadi."
*****
Har washegari Asmau tana kiran wayar Abubakar saboda bai zo ba kamar yadda tayi tsammani. Babu waya babu text. Nata kiran kuma yaki dauka. Hankalinta yayi matukar tashi. Yanzu idan ya fasa aurenta saboda abinda suka yi yaya zata yi da ranta.
Shima a gida kwana yayi kuka. Idan yaga wayar Asmau ji yake kamar yasa ihu. Zuciyarsa ta kasa rabe masa haushinta yake ji don ta bashi kanta ko kuwa haushin kansa da ya tilasta mata.
ABINDA AKE GUDU🙆🏽18
Batul Mamman💖
Bacci barawo ne ya sace Asmau ba don taso ba. Ta raba dare tana kuka wanda ya haddasa mata mugun ciwon kai ga jikinta da yayi tsami. Washegari wurin karfe takwas da rabi ta fito daga dakinsu zata shiga kitchen dora ruwan tea ta tarar Umma har ta dama kunu tana buga kosai.
Gaishe da Umman tayi sannan ta yunkura zata karbi aikin ta karasa Umma tace ta bari ya jikin nata. Kafin ta amsa Umma ta dakatar da ita
"Asmau ki fada min gaskiya meye yake damunki? Ji yadda fuskarki ta kumbura ga wata tafiya kina yi kamar me tatata".
A dan tsorace Asmau tace "zamewa nayi a toilet da zanyi alwala."
Umma ta bita da kallo na rashin gamsuwa.
"To fuskar taki fa? Kinsan bana son boye-boye idan rigima kuka yi da Abubakar jiya ki fada min tun wuri ayiwa tufkar hanci."
Murmushi Asmau ta kalalo "Umma lafiya kalau muke. Kaina ne har yanzu yake ciwo sosai kamar bansha magani ba".
"Idan anyi breakfast sai Jafar ya kaiki asibiti tunda dai kin sha magani jiya bai warke ba gara kiga likita sosai. Allah Ya sauwake. Bari na soya kosan sai kici kiyi wanka."
Jikinta a sanyaye ta fita ta koma daki tayi wanka. Zuciyarta ta gama raunana amma cigaba da kukan bazai amfaneta da komai ba sai tonon silili.
Umma kuwa sai tattalinta take yi har daki ta kai mata abinci tana ta sannu. Wannan ya kara sawa taji ta tsani kanta. Ji yadda mahaifiyarta ke kula da ita bayan ciwon nata baya bukatar tausayawa daga kowa.
Sunje asbiti tasha allurai saboda zazzabi sannan aka bata magunguna.
Da suka koma gida Umma ta sanar da ita Abubakar yazo amma ya wuce Kaduna ana nemansa akan wasu takardu da ya kulle a office. Kai kawai Asmau ta gyada ba don ta yarda ba. Daga dawowarsu zuwa wayewar gari tayi masa text yafi goma banda waya da ba'a kirgawa. Gani take yi kawai zai gujeta ne kamar yadda take yawan jin labarai na samari da suke yaudarar 'yan matansu.
*****
Kafin azahar Abubakar ya isa Kaduna. Jiya ko kadan bai runtsa ba sau tunani da ya addabi zuciyarsa. Ji yayi Kanon tayi masa zafi shiyasa ya dawo saboda baya son yawan tambaya akan me yake damunsa.
Kwanansa biyu da dawowa baya zuwa ko ina daga office sai gida sai ko masallacin unguwar da yake. Rabonsa da abincin kirki ma ya manta. Yana kwance ya kurawa fanka dake juyawa ido wayarsa tayi kara.
Sunan Qasim ya gani shiyasa ya dauka. Qasim ya sanar dashi wani aiki zai kawo shi garin yanzu zai kamo hanya. Addua Abubakar yayi masa sannan ya dan gyara dakin da ko shara baya samu.
Tun zuwan Qasim ya kula da canjawar da abokinsa yayi. Yayi tambayar har ya gaji babu amsa. To me zai fada masa?
A nata bangaren Asmau ji take yi kamar tayi hauka. Tayi wayar har ta gaji. Hawayenta ma ya kafe jira take kawai azo ace Abubakar ya fasa.
*****
Ranar juma'a da safe Abubakar ya gama shirin tafiya office Qasim yace
"Karfe nawa zamu tafi Kanon?"
"Wannan satin bazan je ba ayyuka sunyi min yawa" Abubakar ya bashi amsa.
Kayan da yake sawa a 'yar jakarsa ya ture ya koma kallonsa "Abubakar nayi nayi ka fada min abinda ke damunka kaki na rasa dalili. Ni mai sonka ne da alkhairi idan ka fada min ko addua sai na tayaka".
Kwalla yaji ta cika masa ido ya dan dake "na fada maka babu komai bari naje na dawo mu tafi. Shikenan ko".
Qasim dai bai gamsu ba. Yana nan zaune aka kawo wuta ya saka wani CD na wa'azi da ya gani a kusa da tv din dakin. Ko minti goma ba'ayi da farawa ba Abubakar ya shigo lokacin shabiyu saura.
Zamansa ke da wuya aka yiwa malamin dake wa'azin tambaya akan ZINA. Malamin yace
"Lallai zina tana daga cikin manyan kaba'ira da Allah SWT Yayi hani dasu. Ban da lalacewar zamani yanzu da muka dauketa ba a bakin komai ba zaka ga yawanci duk addinin duniya yayi hani da zina saboda muninta da kazantar dake cikinta. A cikin suratul Furqan ayoyi na 69 zuwa 71 Allah Yana cewa
*WADANDA BASA DAUKAN WANI BAYAN ALLAH A MATSAYIN UBANGIJI KUMA BASA KASHE RAI BA BISA SHARI'AH BA, KUMA BASA ZINA WANDA DUK YA AIKATA HAKA ZAI SAMI ZUNUBI DAIDAI AKIN DA YAYI*.
*ZA'A NINKA MASA AZABAR RANAR ALKIYAMA KUMA ZAI KASANCE A CIKINTA HAR ABADA*.
*SAI WANDA YA TUBA KUMA YAYI IMANI KUMA YA AIKATA AIKI MAI KYAU, WADANNAN SUNE ALLAH YAKE CANZA MUSU ZUNUBANSU ZUWA GA LADA. ALLAH MAI RAHMA NE MAI JINKAI* Abin duba a nan shine an lissafa zina da ayyuka masu matukar muni wato shirka da kisan rai ba tare da hakki na shariah ba"
Haka malamin ya cigaba da janyo ayoyin AlQurani da hadisan Annabi SAW wadanda suka yi hani da zina ko azabar dake jiran masu yinta.
Ya kawo aya ta 32 a cikin Sural Isra' wadda Allah Madaukakin Sarki Ya umarce wadanda suka yi imani da kada su kusanci zina.
"Ina cikin tashin hankali da son kasancewa tare dake. Wallahi bazan iya kaimu Kano ba a yanayin da nake ji yanzu musamman da kike zaune kusa dani. Ki taimakeni ko sau daya ne na kawar da wannan masifaffen tunanin."
Kofar motar ta kama a gigice hawaye na wanke mata fuska jin ya saka lock. Sanyin AC bai hanata gumi ba.
"Yaya Abubakar ka rufa min asiri ka mayar dani gidan Anti Bintu. Duk ni na jawo wannan matsalar da na rinka saka kaya masu matse jiki ina zama kusa da kai. Sharrin shaidan ne da na zuciya don Allah kayi hakuri nan da wata hudu zamuyi aure fa".
Magiyar da take masa jin muryarta yake kamar tana masa busa. Wannan wace irin masifa ce??? Shiyasa tun a da yake nisanta daga duk abinda zai jawo masa sha'awa tunda ya gane yanayinsa.
Hawaye ne ya zubo a idonsa wanda bai san dalilinsu ba.
"Ke kadai nake so kuma da ke kadai na amince Asmy. Idan baki amince ba wallahi nayi miki rantsuwa zan nemi wata. Bani da lafiya duk a dalilin sonki da son kusantarki. Ko kinsan satin nan ko sau daya banje wurin aiki ba saboda halin dana tsinci kaina a ciki".
Kuka Asmau take yi sosai gashi tausayinsa ya mamaye zuciyarta.
" Yaya kada mu aikata haram. Kuma idan ka rabani da abinda duk budurwa take takama dashi yaya zanyi?"
Hannuwanta duka biyun ya rike. "Asmy kinsan dai nine mai aurenki ko? Kuma ni ba wai zanyi miki yadda zaki tashi daga budurwa bane. Akwai yadda zanyi babu wanda zai ce namiji ya kusanceki. Ki taimake ni.
Har bincike nayi wasu malaman sunce kudin aure daidai yake da sadaki. Ko baki ga iyayenmu maza ke zuwa ba ayi a gaban shaidu. Al'ada ce kawai sake taruwar da ake yi a daura aure. Amma yanzu ma a haka ni da ke matsayin mata da miji muke." Shi da yake fada mata hakan ya tabbatar karya yake yi amma babu yadda ya iya da zuciyarsa.
Roko da rarrashi haka ya rinka yiwa Asmau tana kuka haka ta amince saboda tausayin da ya bata da tsoron kada ya nemi wata.
Wani hotel ya sama musu kuma da yake duk sunyi shigar mutunci babu mai cewa ba ma'auratan gaske bane. Haka ya karbi mukullin dakin zuciyarsa tana kwabarsa da abinda yake shirin aikatawa amma gangar jikinsa bazata iya hakuri ba.
A kofar dakin da kyar Asmau ta shiga. Yana rufe kofar ta kara fashewa da kuka. Abubakar yayi nisa duk da yana tausayinta hakan bai hanashi biyan bukakarsa ba. Alkawarin da yayi mata na yin dabara kada ta rasa budurcinta tuni ya manta dashi.
Sai da komai ya kammala yaji kamar tashin hankalin duniya duk ya kare a kansa. Gefen gado ya koma ya dafe kai ya rasa inda zaisa kansa.
Asmau tana kwance sai sautin kukanta ke tashi. Ga ciwo ga bakinciki.
Sun kusa awa daya sannan yayi wanka ya umarceta da itama tayi. Wannan masifa da yawa take...Ya Allah Ka tsare mana imaninmu.
Haka suka fito babu wanda yake yiwa dan uwansa magana. Ya biya kudin hotel suka wuce Kano yana ta zabga gudu a hanya.
A bakin gate din gidansu ya sauketa zuciyarsa tana kuna. Ya rasa me yake ji game da Asmau. Ko kayanta bai taimaka mata da dauka ba haka ta fito dasu ta shige gida fuska a kumbure.
Su Umma sai murna suke yi ta dawo amma ganin yanayinta Umman ta tsorata tana tambayarta abinda ya faru.
Asmau ta fashe da kuka ta rungume mahaifiyarta. Yau taci amanar addininta kuma taci amanar Umma.
Taruwa suka yi a kanta Jafar ya taba jikinta. Zazzabi ne sosai a jikin hatta kanta ya dau zafi.
Ya danyi murmushi "Umma wannan 'yar taki ta fiye shagwaba da raki. Daga zazzabi kuma sai kuka?"
Sai a lokacin tayi dan murmushi ganin cewa idan ta cigaba da kukan zata tonawa kanta asiri.
"Yaya Jafar ji nake kamar kan zai tsage biyu"
Umma ta tasheta tsaye
"Ki dena tsorata ni irin haka Asmau. Baki ji yadda gabana ya fadi ba. Muje ki dan watsa ruwa sai kici abinci kisha magani. Ina Abubakar din?"
Har zuciyarta ta razana jin an ambaci sunansa.
"Ya tafi gida amma yace zai shigo ku gaisa anjima".
"Babu komai ai kun sha hanya ga rana. Allah Yasa ba kukan nan naki kika rinka yi masa ba saboda baki jindadi."
*****
Har washegari Asmau tana kiran wayar Abubakar saboda bai zo ba kamar yadda tayi tsammani. Babu waya babu text. Nata kiran kuma yaki dauka. Hankalinta yayi matukar tashi. Yanzu idan ya fasa aurenta saboda abinda suka yi yaya zata yi da ranta.
Shima a gida kwana yayi kuka. Idan yaga wayar Asmau ji yake kamar yasa ihu. Zuciyarsa ta kasa rabe masa haushinta yake ji don ta bashi kanta ko kuwa haushin kansa da ya tilasta mata.
ABINDA AKE GUDU🙆🏽18
Batul Mamman💖
Bacci barawo ne ya sace Asmau ba don taso ba. Ta raba dare tana kuka wanda ya haddasa mata mugun ciwon kai ga jikinta da yayi tsami. Washegari wurin karfe takwas da rabi ta fito daga dakinsu zata shiga kitchen dora ruwan tea ta tarar Umma har ta dama kunu tana buga kosai.
Gaishe da Umman tayi sannan ta yunkura zata karbi aikin ta karasa Umma tace ta bari ya jikin nata. Kafin ta amsa Umma ta dakatar da ita
"Asmau ki fada min gaskiya meye yake damunki? Ji yadda fuskarki ta kumbura ga wata tafiya kina yi kamar me tatata".
A dan tsorace Asmau tace "zamewa nayi a toilet da zanyi alwala."
Umma ta bita da kallo na rashin gamsuwa.
"To fuskar taki fa? Kinsan bana son boye-boye idan rigima kuka yi da Abubakar jiya ki fada min tun wuri ayiwa tufkar hanci."
Murmushi Asmau ta kalalo "Umma lafiya kalau muke. Kaina ne har yanzu yake ciwo sosai kamar bansha magani ba".
"Idan anyi breakfast sai Jafar ya kaiki asibiti tunda dai kin sha magani jiya bai warke ba gara kiga likita sosai. Allah Ya sauwake. Bari na soya kosan sai kici kiyi wanka."
Jikinta a sanyaye ta fita ta koma daki tayi wanka. Zuciyarta ta gama raunana amma cigaba da kukan bazai amfaneta da komai ba sai tonon silili.
Umma kuwa sai tattalinta take yi har daki ta kai mata abinci tana ta sannu. Wannan ya kara sawa taji ta tsani kanta. Ji yadda mahaifiyarta ke kula da ita bayan ciwon nata baya bukatar tausayawa daga kowa.
Sunje asbiti tasha allurai saboda zazzabi sannan aka bata magunguna.
Da suka koma gida Umma ta sanar da ita Abubakar yazo amma ya wuce Kaduna ana nemansa akan wasu takardu da ya kulle a office. Kai kawai Asmau ta gyada ba don ta yarda ba. Daga dawowarsu zuwa wayewar gari tayi masa text yafi goma banda waya da ba'a kirgawa. Gani take yi kawai zai gujeta ne kamar yadda take yawan jin labarai na samari da suke yaudarar 'yan matansu.
*****
Kafin azahar Abubakar ya isa Kaduna. Jiya ko kadan bai runtsa ba sau tunani da ya addabi zuciyarsa. Ji yayi Kanon tayi masa zafi shiyasa ya dawo saboda baya son yawan tambaya akan me yake damunsa.
Kwanansa biyu da dawowa baya zuwa ko ina daga office sai gida sai ko masallacin unguwar da yake. Rabonsa da abincin kirki ma ya manta. Yana kwance ya kurawa fanka dake juyawa ido wayarsa tayi kara.
Sunan Qasim ya gani shiyasa ya dauka. Qasim ya sanar dashi wani aiki zai kawo shi garin yanzu zai kamo hanya. Addua Abubakar yayi masa sannan ya dan gyara dakin da ko shara baya samu.
Tun zuwan Qasim ya kula da canjawar da abokinsa yayi. Yayi tambayar har ya gaji babu amsa. To me zai fada masa?
A nata bangaren Asmau ji take yi kamar tayi hauka. Tayi wayar har ta gaji. Hawayenta ma ya kafe jira take kawai azo ace Abubakar ya fasa.
*****
Ranar juma'a da safe Abubakar ya gama shirin tafiya office Qasim yace
"Karfe nawa zamu tafi Kanon?"
"Wannan satin bazan je ba ayyuka sunyi min yawa" Abubakar ya bashi amsa.
Kayan da yake sawa a 'yar jakarsa ya ture ya koma kallonsa "Abubakar nayi nayi ka fada min abinda ke damunka kaki na rasa dalili. Ni mai sonka ne da alkhairi idan ka fada min ko addua sai na tayaka".
Kwalla yaji ta cika masa ido ya dan dake "na fada maka babu komai bari naje na dawo mu tafi. Shikenan ko".
Qasim dai bai gamsu ba. Yana nan zaune aka kawo wuta ya saka wani CD na wa'azi da ya gani a kusa da tv din dakin. Ko minti goma ba'ayi da farawa ba Abubakar ya shigo lokacin shabiyu saura.
Zamansa ke da wuya aka yiwa malamin dake wa'azin tambaya akan ZINA. Malamin yace
"Lallai zina tana daga cikin manyan kaba'ira da Allah SWT Yayi hani dasu. Ban da lalacewar zamani yanzu da muka dauketa ba a bakin komai ba zaka ga yawanci duk addinin duniya yayi hani da zina saboda muninta da kazantar dake cikinta. A cikin suratul Furqan ayoyi na 69 zuwa 71 Allah Yana cewa
*WADANDA BASA DAUKAN WANI BAYAN ALLAH A MATSAYIN UBANGIJI KUMA BASA KASHE RAI BA BISA SHARI'AH BA, KUMA BASA ZINA WANDA DUK YA AIKATA HAKA ZAI SAMI ZUNUBI DAIDAI AKIN DA YAYI*.
*ZA'A NINKA MASA AZABAR RANAR ALKIYAMA KUMA ZAI KASANCE A CIKINTA HAR ABADA*.
*SAI WANDA YA TUBA KUMA YAYI IMANI KUMA YA AIKATA AIKI MAI KYAU, WADANNAN SUNE ALLAH YAKE CANZA MUSU ZUNUBANSU ZUWA GA LADA. ALLAH MAI RAHMA NE MAI JINKAI* Abin duba a nan shine an lissafa zina da ayyuka masu matukar muni wato shirka da kisan rai ba tare da hakki na shariah ba"
Haka malamin ya cigaba da janyo ayoyin AlQurani da hadisan Annabi SAW wadanda suka yi hani da zina ko azabar dake jiran masu yinta.
Ya kawo aya ta 32 a cikin Sural Isra' wadda Allah Madaukakin Sarki Ya umarce wadanda suka yi imani da kada su kusanci zina.