Sashe 69
Abinda Ake Gudu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ran Col. Ishaq ya soma baci yace "Hussaini bana son wasa. Kada ka manta banda dangina bani da wani amini sama da kai. Kai kadai na fadawa komai game da Asmau kafin na aureta. Sauran a gari suka ji idan har sun sani. After all these years aure kasa da shekara ko wata shida bamuyi ba tace min tana da ciki" muryarsa tayi rauni sosai dauriya ce kawai yake.
Zama Hussaini yayi a kujerar da take kallon ta Col. Ishaq hankakinsa a tashe.
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un. Kada kace min zarginta kake yi. Col. Ishaq Jikamshi waye ya fada maka bazaka taba haihuwa ba? Na tabbatar ba ni bane"
Maganar ta fara daure masa kai yace "ku likitoci kun iya boyewa mutane zahirin abu sai kuyi ta rufa rufa don kada ku tsorata patient. Ka gwadani ka kuma hadani da likitocin da lalurata ta shafe su. Kowanne sai ya cemin lokaci ne baiyi ba. wane magani ne ban sha ba. Sai gashi Badar ta haihu daga yin aure. Wannan ya tabbatar min ni nake da matsalar. Nine bana haihuwa "
Hussaini ya jima yana kallon abokinsa kafin yayi magana "idan ni ko wasu a nan zamu boye maka idan bazaka taba haihuwa ba, asibitocin da kaje a kasashen waje kasan bazasu yi maka karya ba. Babu wanda ya kai bature baro baro. Sai ya fada maka nan da lokaci kaza zaka mutu. Duk wani sakamakonka kana bani copy na ajiye. Babu inda akace bazaka taba haihuwa ba. Dukkansu suna cewa ko dai akwai matsala a mahaifar Badariyya ko kuma wani dalili dai ya hana cikin samuwa amma ba rashin lafiya gareku ba."
Col. Ishaq ji yayi ya fara jin zafi. Me Hussaini yake nufi. Wai zai iya haihuwa???.
Hussaini ya cigaba "idan wasu zasu boye maka ni bazan bari kayi ta kashe kudi kamar baka san zafin nema ba akan haihuwa alhalin nasan bazaka samu ba. Garin yaya ka yankewa kanka wannan shawarar har kake zargin matarka. Allah Sarki shiyasa naga ta kasa magana da kuka shigo. Bani da masaniya game da Asmau bayan abinda ka fada min amma bana jin zata aikata wannan mummunan aikin gareka. Kada ka manta taga rayuwa a dalilin kuskuren farko. Wallahi ni ka kara tsoratani akan zina. Idan har zaka zargeta duk son da kake mata lallai har a nade duniya fentin zina bazai taba barin Asmau ba. Ya Allah Ka nesantamu daga wannan bala'i "
Jikin Col. Ishaq ya gama sanyi kam yanzu. A lokacin da Asmau tayi masa albishir da samun karuwa a lokacin tarihin rayuwarta ta baya ya dawo masa har yake tunanin ko a garuruwan da ta zauna ta cigaba da mugun aiki. Tashi yayi da sauri Hussaini ya dakatar dashi "ka jira nayi mata gwaji a tabbatar"
Zama yayi amma jinsa yake a kan kaya. So yake ya ga Matar Jikamshi a jikin Jikamshinta. Wani irin sonta yake ji na daban yana ratsa shi. Gabadaya yaji ya tsani kansa da zuciyarsa da ta raya masa wannan mummunan zargi..
Tana zaune an saka mata bandeji a yatsun Hussaini ya shigo dakin da suke. Nurse ya bawa umarni ta debi jininta nan da nan ya karba ya tafi lab dinsu. Da kansa yayi gwajin har sau biyu ya tabbatar babu karya Asmau tana da ciki. Dawowa yayi yayi mata tambayoyi wanda tana amsawa tana hawaye. Yaji tausayinta sosai sannan suka koma office dinsa.
Ko da suka shiga kunya ce ta kama Col. Ishaq ya kasa yi mata magana. Hussaini yana murmushi yace "congrats Sir, uwargida tana da ciki wata na uku kenan. Zan bata appointment idan tazo sai a bata maganunguna ayi scanning domin ganin lafiyar baby. Allah Ya inganta Ya raba lafiya."
Col. Ishaq kamar yayi me don murna. Yana cewa Amin ita kuwa Asmau ta fita daga office din saboda kukan da yazo mata. A bakin mota ya sameta bayan Hussaini ya nanata masa lallai yayi kokarin shawo kanta saboda yayi mata laifi.
Sun shiga mota sun zauna bata ko kalli inda yake ba. Shiru suka yi yaja motar sai gidan Hajiya. Ta goge idonta sannan tabi bayansa suka shiga ciki. Hajiyan na daki tana kashingide ya shiga da sallama.
Ta tashi zaune tana amsawa. Asmau ta tsaya a bakin kofa kawai sai ji tayi ya kama hannunta ya ja har gaban gadon Hajiya. Kunya kuwa daga ita har Hajiyan. Zama yayi a kusa da ita a kasa sai ta fashe da kuka Hajiya tace "lafiyarku kuwa, me kayi mata"
Baya son kukan Asmau haka kuma baya son bacin ranta wanda shine ya haddasa mata. Kansa a sunkuye yace "Hajiya daga asibiti muke yanzu, tana da ciki wata biyu"
*Alhamdulillah....* Hajiya ta fada sai kawai ta rungumo Asmau jikinta. Abin mamaki kuka ta saka Asmau na tayata.
"Waye yace babu Allah? Allah sarkin dukkan mai sarauta. Ubangijin Annabi Adamu tsira da AmincinKa ya kara tabbata ga Annabi Muhammadu SAW. Ban taba fitar da rai da zaka ga jininka ba Ishaq. Allah Ya amsa min, Allah nagode. Sai dai bawa yaga jinkiri wanda komai daren dadewa zamu kwashi ladan hakurinmu a duniya ko a lahira. Allah Yayi miki albarka Ya raba lafiya"
Duk duniya babu matan da yake so sama da Hajiyarsa da matarsa. Yau Hajiya harda kiran sunansa don murna. Gasu a gabansa suna kuka. Hajiya ta dago kan Asmau tana kallo "ba abin kuka bane Asmau. Ki godewa Allah"
Col. Ishaq yace "Hajiya nayi mata laifi. Ko kallonta na kasa yi shiyasa na kawota wurinki"
Ai kuwa yasha harara a wurin Haj Lubabatu.
"Asmau me yayi miki? A wannan yanayin har
zaka bata mata rai"
Muryarta har ta dashe da kuka tace "ba laifinsa bane Hajiya. Laifina ne, kuskurena ne, da ban biyewa zuciyata da shaidan ba hakan bazata faru ba"
"Don Allah kuyi min bayani. Me kayi mata nace?"
Asmau ce ta kuma yin magana don ya kasa dago kansa "bakin fentin da nayiwa kaina bazai taba wankuwa ba ko me zanyi a duniya. Allah ne kadai shaida akan tuban bayinSa. Ban taba yi muku karya ba wallahi sau daya tsautsayi ya fada min. Da banyi cikin shege ba...."
Toshe mata baki yayi da hannu ya hanata karasa magana a gaban Hajiyarsa yana kokarin rungumeta. Hawaye ne da baisan daga ina ba suke zarya a kumatunsa.
Hajiya da kanta ta sa hannu ta janye Asmau ranta yayi masifar baci. Ita rashin kunyar tasa ma yau bata gani ba. Cikin fushi tace "hala cewa kayi ba cikinka bane?"
Bazaiyi mata karya ba ya gyada kai. Kowa a gaban mahaifiyarsa yaro ne. Tsawa tayi masa sosai abinda ya bawa Asmau tsoro.
"Shekarunka da iliminka sun tashi a banza. Kuma ka bani kunya ashe son da kake ikirarin yi mata yana da iyaka. Idan bata yafe maka ba zargin nan kasan cewa zaka hadu da fushin.... "
Asmau ta kara fashewa da kuka ganin yadda mijinta abin sonta yake hawaye kamar karamin yaro ana yi masa fada bayan bashi da laifi "A'a Hajiya kiyi hakuri wallahi ba laifinsa bane. Laifina ne da na zubar da mutuncina a waje." Ta juya tana kallonsa shima ita yake kallo "ni nace ban yafe maka bane da ka kawo kanka kara, ko fushi banyi da kai ba. Don Allah ka dena kuka Jikamshina"
"Da gaske kin yafe min Matar Jikamshi?" Ya fada yana dago hannu zai share mata hawaye. Ta gyada kai tana murmushi.
Haj Lubabatu taji dadi sosai, wannan so da suke yiwa juna daga Allah ne. Gani tayi za'a fara rashin kunya a gabanta kamar sun manta tana wurin Col. Ishaq ya gama matsowa kusa da Asmau sai tayi gyaran murya ta sake hade rai.
"Dan bamu wuri zanyi mata magana"
Sai da ta maimaita ya tashi ya fita daga shi har Asmau suna kallon juna. Bayan ya fita Hajiya tace "Asmau kafin nace komai ina rokonki alfarma don Allah kada Haj Bara'atu taji zancen nan. Ko kadan bazata ji dadi ba. Sannan ina so ki kara hakuri da kaddara. Kamar yadda kika fada duk matar da ta taba aikata kuskure har wani namijin ya kusanceta to wallahi har abada lokaci zuwa lokaci akwai sanda zargi ko yaya zai darsu a zuciyar wadanda suke tare da ita. Zaki ga kinyi abin bajinta da burgewa amma karshe tuhumarki za'ayi. Kada ki rabe dayan biyun yaron nan yana sonki. Kiyi hakuri da halin da zakiyi ta tsintar kanki a ciki saboda abinda ya faru a baya"
Murmushi Asmau tayi "ko kadan banji haushinsa ba. Kukana nadama ce akan abinda nayi a baya. Na tabbatar ba don haka ba Allah kadai Yasan farincikin da zaiyi tun farko. Da wata yake aure wadda bata da tabo irin nawa zaiji dadi mara misaltuwa. Ni kuwa dole ne yaji tsoron ko ba nasa bane musamman da ya gama yarda bazai haihu ba"
Hajiya tace "shi kadai ya yankewa kansa wannan hukuncin babu ruwan likitoci. Badariyya ta haihu saboda rabonta na can shima gashi Allah Ya bashi nashi. Allah Yayi muku albarka." Ta kallo kofa "Sai ka shigo tunda ka koyi labe kaima"
Asmau ta kallo wurin kofa sai gashi Jikamshinta ya shigo. Ko tun yaushe yake wurin bata sani ba. Maganganunsu da Hajiya sun kara sashi jin bai kyautawa Asmau ba. Dole yayi kokari wurin mantar da ita kuncin da ya dasa mata.
Hajiya tace "sai ka tafi gida ita a nan zata kwana. Asmau me zan dafa miki?"
Asmau tace "Hajiya don Allah ki zauna bana jin yunwa"
"Dole kici abinci duk kin rame. Kai kuma me kake jira ka tafi mana."
Asmau na kallo ko motsi yaki yi. Hajiya ta fita daga dakin don take takensa rashin kunyar da ta rasa inda suka gado ta yake neman yi. Kitchen ta tafi tana tunanin me zata dafawa Asmau taci. Baiwar Allah duk ta rame. Shima kuma ya fada kamar bashi ba.
Yana dena jin takun Hajiya ya daga Asmau yana juyi da ita "I love you so much Matar Jikamshi. Ki yafe min kinji"
Zata yi dariya saboda yau zuciyarta a wanke take yace "kada kiyi dariya ko so kike Hajiya taji tace baki da kunya"
"Kai da ka daukeni a tsakar dakinta ai ka fini rashin kunyar"
Zama Hussaini yayi a kujerar da take kallon ta Col. Ishaq hankakinsa a tashe.
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un. Kada kace min zarginta kake yi. Col. Ishaq Jikamshi waye ya fada maka bazaka taba haihuwa ba? Na tabbatar ba ni bane"
Maganar ta fara daure masa kai yace "ku likitoci kun iya boyewa mutane zahirin abu sai kuyi ta rufa rufa don kada ku tsorata patient. Ka gwadani ka kuma hadani da likitocin da lalurata ta shafe su. Kowanne sai ya cemin lokaci ne baiyi ba. wane magani ne ban sha ba. Sai gashi Badar ta haihu daga yin aure. Wannan ya tabbatar min ni nake da matsalar. Nine bana haihuwa "
Hussaini ya jima yana kallon abokinsa kafin yayi magana "idan ni ko wasu a nan zamu boye maka idan bazaka taba haihuwa ba, asibitocin da kaje a kasashen waje kasan bazasu yi maka karya ba. Babu wanda ya kai bature baro baro. Sai ya fada maka nan da lokaci kaza zaka mutu. Duk wani sakamakonka kana bani copy na ajiye. Babu inda akace bazaka taba haihuwa ba. Dukkansu suna cewa ko dai akwai matsala a mahaifar Badariyya ko kuma wani dalili dai ya hana cikin samuwa amma ba rashin lafiya gareku ba."
Col. Ishaq ji yayi ya fara jin zafi. Me Hussaini yake nufi. Wai zai iya haihuwa???.
Hussaini ya cigaba "idan wasu zasu boye maka ni bazan bari kayi ta kashe kudi kamar baka san zafin nema ba akan haihuwa alhalin nasan bazaka samu ba. Garin yaya ka yankewa kanka wannan shawarar har kake zargin matarka. Allah Sarki shiyasa naga ta kasa magana da kuka shigo. Bani da masaniya game da Asmau bayan abinda ka fada min amma bana jin zata aikata wannan mummunan aikin gareka. Kada ka manta taga rayuwa a dalilin kuskuren farko. Wallahi ni ka kara tsoratani akan zina. Idan har zaka zargeta duk son da kake mata lallai har a nade duniya fentin zina bazai taba barin Asmau ba. Ya Allah Ka nesantamu daga wannan bala'i "
Jikin Col. Ishaq ya gama sanyi kam yanzu. A lokacin da Asmau tayi masa albishir da samun karuwa a lokacin tarihin rayuwarta ta baya ya dawo masa har yake tunanin ko a garuruwan da ta zauna ta cigaba da mugun aiki. Tashi yayi da sauri Hussaini ya dakatar dashi "ka jira nayi mata gwaji a tabbatar"
Zama yayi amma jinsa yake a kan kaya. So yake ya ga Matar Jikamshi a jikin Jikamshinta. Wani irin sonta yake ji na daban yana ratsa shi. Gabadaya yaji ya tsani kansa da zuciyarsa da ta raya masa wannan mummunan zargi..
Tana zaune an saka mata bandeji a yatsun Hussaini ya shigo dakin da suke. Nurse ya bawa umarni ta debi jininta nan da nan ya karba ya tafi lab dinsu. Da kansa yayi gwajin har sau biyu ya tabbatar babu karya Asmau tana da ciki. Dawowa yayi yayi mata tambayoyi wanda tana amsawa tana hawaye. Yaji tausayinta sosai sannan suka koma office dinsa.
Ko da suka shiga kunya ce ta kama Col. Ishaq ya kasa yi mata magana. Hussaini yana murmushi yace "congrats Sir, uwargida tana da ciki wata na uku kenan. Zan bata appointment idan tazo sai a bata maganunguna ayi scanning domin ganin lafiyar baby. Allah Ya inganta Ya raba lafiya."
Col. Ishaq kamar yayi me don murna. Yana cewa Amin ita kuwa Asmau ta fita daga office din saboda kukan da yazo mata. A bakin mota ya sameta bayan Hussaini ya nanata masa lallai yayi kokarin shawo kanta saboda yayi mata laifi.
Sun shiga mota sun zauna bata ko kalli inda yake ba. Shiru suka yi yaja motar sai gidan Hajiya. Ta goge idonta sannan tabi bayansa suka shiga ciki. Hajiyan na daki tana kashingide ya shiga da sallama.
Ta tashi zaune tana amsawa. Asmau ta tsaya a bakin kofa kawai sai ji tayi ya kama hannunta ya ja har gaban gadon Hajiya. Kunya kuwa daga ita har Hajiyan. Zama yayi a kusa da ita a kasa sai ta fashe da kuka Hajiya tace "lafiyarku kuwa, me kayi mata"
Baya son kukan Asmau haka kuma baya son bacin ranta wanda shine ya haddasa mata. Kansa a sunkuye yace "Hajiya daga asibiti muke yanzu, tana da ciki wata biyu"
*Alhamdulillah....* Hajiya ta fada sai kawai ta rungumo Asmau jikinta. Abin mamaki kuka ta saka Asmau na tayata.
"Waye yace babu Allah? Allah sarkin dukkan mai sarauta. Ubangijin Annabi Adamu tsira da AmincinKa ya kara tabbata ga Annabi Muhammadu SAW. Ban taba fitar da rai da zaka ga jininka ba Ishaq. Allah Ya amsa min, Allah nagode. Sai dai bawa yaga jinkiri wanda komai daren dadewa zamu kwashi ladan hakurinmu a duniya ko a lahira. Allah Yayi miki albarka Ya raba lafiya"
Duk duniya babu matan da yake so sama da Hajiyarsa da matarsa. Yau Hajiya harda kiran sunansa don murna. Gasu a gabansa suna kuka. Hajiya ta dago kan Asmau tana kallo "ba abin kuka bane Asmau. Ki godewa Allah"
Col. Ishaq yace "Hajiya nayi mata laifi. Ko kallonta na kasa yi shiyasa na kawota wurinki"
Ai kuwa yasha harara a wurin Haj Lubabatu.
"Asmau me yayi miki? A wannan yanayin har
zaka bata mata rai"
Muryarta har ta dashe da kuka tace "ba laifinsa bane Hajiya. Laifina ne, kuskurena ne, da ban biyewa zuciyata da shaidan ba hakan bazata faru ba"
"Don Allah kuyi min bayani. Me kayi mata nace?"
Asmau ce ta kuma yin magana don ya kasa dago kansa "bakin fentin da nayiwa kaina bazai taba wankuwa ba ko me zanyi a duniya. Allah ne kadai shaida akan tuban bayinSa. Ban taba yi muku karya ba wallahi sau daya tsautsayi ya fada min. Da banyi cikin shege ba...."
Toshe mata baki yayi da hannu ya hanata karasa magana a gaban Hajiyarsa yana kokarin rungumeta. Hawaye ne da baisan daga ina ba suke zarya a kumatunsa.
Hajiya da kanta ta sa hannu ta janye Asmau ranta yayi masifar baci. Ita rashin kunyar tasa ma yau bata gani ba. Cikin fushi tace "hala cewa kayi ba cikinka bane?"
Bazaiyi mata karya ba ya gyada kai. Kowa a gaban mahaifiyarsa yaro ne. Tsawa tayi masa sosai abinda ya bawa Asmau tsoro.
"Shekarunka da iliminka sun tashi a banza. Kuma ka bani kunya ashe son da kake ikirarin yi mata yana da iyaka. Idan bata yafe maka ba zargin nan kasan cewa zaka hadu da fushin.... "
Asmau ta kara fashewa da kuka ganin yadda mijinta abin sonta yake hawaye kamar karamin yaro ana yi masa fada bayan bashi da laifi "A'a Hajiya kiyi hakuri wallahi ba laifinsa bane. Laifina ne da na zubar da mutuncina a waje." Ta juya tana kallonsa shima ita yake kallo "ni nace ban yafe maka bane da ka kawo kanka kara, ko fushi banyi da kai ba. Don Allah ka dena kuka Jikamshina"
"Da gaske kin yafe min Matar Jikamshi?" Ya fada yana dago hannu zai share mata hawaye. Ta gyada kai tana murmushi.
Haj Lubabatu taji dadi sosai, wannan so da suke yiwa juna daga Allah ne. Gani tayi za'a fara rashin kunya a gabanta kamar sun manta tana wurin Col. Ishaq ya gama matsowa kusa da Asmau sai tayi gyaran murya ta sake hade rai.
"Dan bamu wuri zanyi mata magana"
Sai da ta maimaita ya tashi ya fita daga shi har Asmau suna kallon juna. Bayan ya fita Hajiya tace "Asmau kafin nace komai ina rokonki alfarma don Allah kada Haj Bara'atu taji zancen nan. Ko kadan bazata ji dadi ba. Sannan ina so ki kara hakuri da kaddara. Kamar yadda kika fada duk matar da ta taba aikata kuskure har wani namijin ya kusanceta to wallahi har abada lokaci zuwa lokaci akwai sanda zargi ko yaya zai darsu a zuciyar wadanda suke tare da ita. Zaki ga kinyi abin bajinta da burgewa amma karshe tuhumarki za'ayi. Kada ki rabe dayan biyun yaron nan yana sonki. Kiyi hakuri da halin da zakiyi ta tsintar kanki a ciki saboda abinda ya faru a baya"
Murmushi Asmau tayi "ko kadan banji haushinsa ba. Kukana nadama ce akan abinda nayi a baya. Na tabbatar ba don haka ba Allah kadai Yasan farincikin da zaiyi tun farko. Da wata yake aure wadda bata da tabo irin nawa zaiji dadi mara misaltuwa. Ni kuwa dole ne yaji tsoron ko ba nasa bane musamman da ya gama yarda bazai haihu ba"
Hajiya tace "shi kadai ya yankewa kansa wannan hukuncin babu ruwan likitoci. Badariyya ta haihu saboda rabonta na can shima gashi Allah Ya bashi nashi. Allah Yayi muku albarka." Ta kallo kofa "Sai ka shigo tunda ka koyi labe kaima"
Asmau ta kallo wurin kofa sai gashi Jikamshinta ya shigo. Ko tun yaushe yake wurin bata sani ba. Maganganunsu da Hajiya sun kara sashi jin bai kyautawa Asmau ba. Dole yayi kokari wurin mantar da ita kuncin da ya dasa mata.
Hajiya tace "sai ka tafi gida ita a nan zata kwana. Asmau me zan dafa miki?"
Asmau tace "Hajiya don Allah ki zauna bana jin yunwa"
"Dole kici abinci duk kin rame. Kai kuma me kake jira ka tafi mana."
Asmau na kallo ko motsi yaki yi. Hajiya ta fita daga dakin don take takensa rashin kunyar da ta rasa inda suka gado ta yake neman yi. Kitchen ta tafi tana tunanin me zata dafawa Asmau taci. Baiwar Allah duk ta rame. Shima kuma ya fada kamar bashi ba.
Yana dena jin takun Hajiya ya daga Asmau yana juyi da ita "I love you so much Matar Jikamshi. Ki yafe min kinji"
Zata yi dariya saboda yau zuciyarta a wanke take yace "kada kiyi dariya ko so kike Hajiya taji tace baki da kunya"
"Kai da ka daukeni a tsakar dakinta ai ka fini rashin kunyar"