← Book details Abinda Ake Gudu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 41 OF 74

Sashe 41

Abinda Ake Gudu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Abinda ake gudu ya riga ya faru kumq shine yasa dole duk muyi hakuri. Kina jin da hakan bata faru da rayuwarta ba zan amince da auren nan ne? Yanzu kuwa bamu da bakin magana tunda mu za'a taimakawa. Ki dena bata bakinki akan maganar nan. An gama yanke shawara tun dazu"

Hajjo ta rasa yadda zatayi da su biyun. Kowacce ta kafe har suna neman yin fada "don Allah kuyi hakuri. Bintu kece karama, mu taru kawai mu tayata addua."

Hawayene kamar an kunna famfo yake saukowa daga idanun Asmau. Dama shiyasa Qasim yace ta jira zuwan lahadi? Yanzu shikenan tun ba'aje ko'ina ba an datse mata samun farinciki daga wurin Jikamshi. Duk maganar su Umma kuma gaskiya suke fada. Ita din tana da tabo a rayuwarta. Wannan yasa a komai shawararta zata zamo ta karshe. Iyaye zasuyi ta ganin kamar komai suka yanke shine alkhairi gareta.

A sanyaye ta shiga dakin ta zauna a kasa.
"Umma indai auren Qasim kuke gani shi yafi dacewa dani na amince"

Anti Bintu ta taso ta tayar da ita tsaye.
"Asmau wace irin magana ce wannan. Ishaq kike so kuma na shaida yana matukar sonki. In Allah Ya yarda shine mijinki"

Umma taji tausayin Asmau har ranta amma yadda abin yazo musu ne basu da yadda zasuyi "Bintu na dauka mun gama maganar Ishaq dinnan"

"Yaya Bara'atu bazan bar maganar ba sai naji daga bakin Ishaq ko shi din ya hakura"

Cikin kuka Asmau tace "Anti Bintu ki bar maganar kawai. Allah Yasa hakan shine mafi alkhairi"

Tashi tayi ta fita jikinta duk babu kwari. Gobe in Allah Ya yarda zata kira Jikamshi ta bashi hakuri. Bata san wace irin rayuwa kuma zatayi da Qasim ba. Mutumin da bata taba jin sonsa ko kadan a ranta ba.
ABINDA AKE GUDU🙆🏽42

Batul Mamman💖

Sallar isha kawai tayi ta kwanta sai kuka. Ganin bazai fishsheta ba yasa ta tashi ta dauro alwala ta soma nafila. Yi take tana kuka tana kara istigfari. Rokon Allah take Ya yafe musu kuskuren da suka aikata wanda har yau yake bibiyar komai na rayuwarsu. Daga nan tayi adduar fatan samun nutsuwa da dukkan wanda Allah Ya kaddara zata aura. Tana sallar Anti Bintu ta shigo da niyyar sake bata baki ta tarar tana sallah. Gefen gado ta samu ta zauna tana jiran ta idar. Tunanin wannan al'amari ne ya rinka damunta. Idan akace *abinda ake gudu*to ba faruwar laifin ake ji ba. Abubuwan da zasu iya biyo bayansa. Asmau ta dade tana ganin tasirin hakan a rayuwarta tun ranar da Abubakar ya rasu. Miji ya rasu ranar daurin aure sannan a sami amarya da ciki. Ai ko a iya nan aka barta ta kafa tarihi a rayuwa wanda duk mutumin da ya santa idan suka hadu sai ya tuna. Ga 'ya ta haifa itama nan gaba tana kara wayo zata iya bukatar jin waye ainihin babanta. Idan kuma marasa tausayi cikin mutane suka goranta mata yanayin haihuwarta ko na sakan daya ne sai ta tsani mahaifiyar da ta sha wahalar rayuwa don ta haifeta. Babu dan da yake son jin shi shege ne. Sannan ga soyayyar wani Allah Ya dora mata amma saboda abinda ya faru a baya idan tace zata bijire ma kallon mara kunya kuma mara godiyar Allah za'ayi mata. Allah Sarki Asmau da matan da suka sami kawunansu a yanayi shigen nata. Tuba da tawakkali shine kawai kwanciyar hankali garesu.

Anti Bintu tana ta tunani har bacci ya kwasheta a zaune Asmau bata idar da sallah ba. Itama sai gabanin asuba ta soma baccin. Ana kiran assalatu ta tashi dama baiyi nisa ba. Ta shi Anti Bintu da 'yan matan da suka shigo dakin kwanciya tun tana sallah. Sai wurin bakwai na safe bacci mai nauyi ya dauketa.
*****

A kitchen Umma ta rabawa kowa aikinsa na taron gobe. Gidan Mama zasuyi meatpie da doughnut. Nan kuma cake zasuyi da pepper chicken sai lemuka da za'a siyo. Har dakin Yassar taje ta bashi kudin abubuwan da zai siyo a fara aikin yace mata da zazzabi ya kwana. Yassar da bashi da kyuyar aike yau kirikiri ya nuna mata bazashi ba. Dama tun jiya ta kula yana wani cin magani ta rasa dalili. Bata san Col. Ishaq yake tayawa kishi ba tun kafin ya fara nasa. Dayake Shemau zata zo sai kawai ta kirata a waya ta fada mata abubuwan da zata taho dasu.

Ta fito tana mitar tasan Yassar kalau yake Anti Bintu tayi dariya.
"Indai Yassar ne ranar daurin auren ma yana iya kirkiro ciwo. Don baki san irin shakuwarsu da Ishaq bane."

"Ke kuma naga alama abin yayi miki dadi. Ni duk a yaushe ya tara masoya a gidan nan ne ban sani ba?"

"duk abinsa ai dole yaji kunyarki. Don baki ga yadda mukayi dashi a Zaria ba. Hatta babansu Dijah sun sha hira sosai. Tamkar 'yan uwansa haka ya dauke mu. Gashi yanzu kun zo kun raba"

Umma ta rike haba tana kallon kanwarta. Da gaske Bintu ta zama 'yar kamfen "kun mayar dani wata boss dai. Gani kuke yi kamar bana son Asmau. Bari ayi auren ku gani idan suka fara zaman lafiya. Yau fa ko gaisheni bata fito tayi ba."

Anti Bintu tace "bacci take yi, jiya kwana tayi tana sallah da kuka"

Hajjo dake tsaye a bakin kofa tana musu dariya tace "ta kwana sallah kika ce, to ni dai babu ruwana Bara'atu da Garzali ne suka yanke shawarar. Allah Yasa dai bata ambaci sunana a adduar ba. Ko dai na tasheta na tambayeta ne. Kunsan addua ba abin wasa bace"

Duk su biyun dariya suka yi. Daga falo suka ji shigowar Zubaida da Sabira. Har kitchen din suka zo aka gaisa suna yiwa Zubaiba fadan dalilin zuwanta tace "Umma jiya banyi bacci ba tunda ya fada min gobe za'a kawo kudin Asmau. Mu dan shiga ciki akwai wani sirri da nake tsammanin bata fada miki ba"

Anti Bintu tace "fadi a nan kawai, ba zancen Ishaq bane"

Zubaida tace "wannan sojan ko. Ashe kun sani, to meyasa za'a hadata da Qasim?"

Hajjo tace "kinga matar auta, jeki ki bawa 'yar uwarki baki kawai. Maganar nan an gamata tun jiya. Allah Ya sanya mana alkhairi"

Jikin Zubaida duk sai yayi sanyi. Mata nawa ta gani a gidan Uwargida wadanda suka ce auren dole ne ya fito dasu daga gidan iyayensu. Allah Yasa Asmau ta iya hakuri dai.

Ko sau daya Asmau bata fito daga daki ba. Abinci ma Dijah ce ta kai mata. Amatullah da bata iya komai idan Umminta bata walwala itama a dakin ta zauna. Har su Shemau suka zo yara sun cika gidan amma taki fita sai nanikar jikin Asmau take yi. Col. Ishaq yayi ta kiranta ta daure ta dauka tace masa baki ne a gidan yau duk ya cika. Har su Anti Bintu sun zo.

"To bazan takuraki ba kije kuyi hira zuwa dare sai muyi magana. Ki gaishe min da Yayata Bintu"

Tana ajiye wayar sai kuka. Yanzu da tasan za'ayi mata katanga dashi tafi jin sonsa ma a zuciyarta. Duk bayan dan lokaci kadan sai tayi mata text mai cike da kalamai masu ratsa zuciya. Shemau tazo tayi ta rarrashinta akan ta hakura ta karbi wanda Allah Ya zaba mata. Gudun kada su dameta yasa ta dan sake tana amsa musu idan an sakota a hira.

Sunyi aikinsu sun gama zuwa yamma. Washegari kawai ake jira mutanen Shanono su iso. A daren ranar Ainau da bata sami zuwa tayasu aiki ba ta kirata harda kukanta. Ta kira Umma tana rokon kada a hana yayarta wanda take so. Umma dai ta rasa yadda zata yi. Duk sun hade mata kai. Jafar ne ma bai nuna ga wanda ransa tafi so da Asmau ba.

Uban gayya ASP Qasim shima sai dare ya kira Asmau. Kana jinsa kasan yana cikin farinciki yace
"Asmau kinga ikon Allah ko. Ina sanar da su Baba maganarmu suka ce kawai azo ayi komai. Ina fatan hakan zai karan kwantar miki da hankali kisan cewa komai ya wuce."

Zuciyarta har wani zafi take yi don bacin rai ta daure tace "babu komai Yaya Qasim, Allah Ya tabbatar mana da alkhairi"

Yaji dadin furucinta "Amin Asmau, goben zanzo nima. Idan sum gama nasu sai mu fara tsara bikin. Sai da safe ko gimbiyata"

Ta kakalo murmushi tayi "to sai da safe" ta ajiye wayar ido na cikowa da kwalla.
*****

Washegari da wuri gidan ya cika kamar masu shirin biki. Yaya Abu da Anti Lami sun zo, Mama da 'ya'yanta mata harda matar Abdulhalim. Sai Aina'u da Shemau da Sabira. Falon aka share aka tura kujerun baya aka shinfida wani kafet din ko da wurin zaman zaiyi kadan. A bangaren maza ma akwai masu zuwa ta bangaren Hajjo da maigidanta sai Kawu Garzali da abokansa biyu. Ga mazansu Anti Lami da na Anti Bintu. Banda kuma gayyar Alh Adamu. So suke su nunawa dangin Qasim suna son 'yarsu kuma ita din 'yar dangi ce.

Tun safe Asmau ta kashe wayarta don bata san me zata cewa Jikamshi ba idan ya kirata. Adduarta kada yazo ana tsakar taron. Yau ma a daki ta zauna sai dai 'yan uwanta su shigo tayata hira.
*****

Ana la'asar mutanen Shanono suka iso gidan Alh Adamu. Daga nan suka dunguma zuwa gidansu Asmau. Mota biyu suka ciko da nasu 'yan uwan. Qasim dama ya rigasu zuwa ya sai zauna a cikin gidan idan taro ya watse zaije ganin Asmau gimbiyarsa.

Kafin su iso Umma tace Asmau ta tafi gidan Jafar tare da wasu cikin 'yan matan tace kanta na ciwo bazata iya fita ba. Umma tayi murmushi kawai ta rabu da ita.

Sauran suka tashi aka jera komai a falon sannan suka koma ciki suna hira a dakin Hajjo saboda yafi fadi.

Asmau na kwance zazzabin dole ya rufeta taji hannuwan Amatullah sun rike mata wuya ta baya. Tun jiya taki sakewa itama. Idan ta korata tayi wasa bata dadewa take dawowa wurin Umminta. Murmushi tayi tana kokarin cire hannunwan don rikon ya danyi karfi
"Ama sake min wuya mana"

Jin tayi shiru yasa ta juyawa sosai. Amatullah ta gani tana kokarin numfashi bakinta a bude.
"Subhanallah" ta fada a rude tana dagata.
"Ama ki rufa min asiri, wayyo Allah"
Chapter 41 · 0% Book details