Sashe 42
Abinda Ake Gudu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Gabadaya ta manta da inhaler din da aka basu a asibiti ta dauketa sai dakin Hajjo. Kuka take yi sosai tun kafin ta shiga su Umma suka fara fitowa saboda muryarta da suke ji.
Ganin Amatullah na numfashi da kyar Shemau ta karbeta Sabira kuma ta kira Jafar a waya. Lokacin Umma har ta dauko mukullin tata motar. Yassar baya gidan shi tun safe ya fice.
Sabira na fadawa Jafar ya tashi da sauri. Lokacin an gama gaisawa da dangin Qasim kenan. Abdulhalim ya tambayeshi abinda ya faru ya fada musu.
Kowa sai salati suka tashi don ta nan su Umma zasu wuce.
Kafin kace meye wannan suna mota Asmau ta cire dankwali sai hijabinta kawai tana yiwa Amatullah fifita. A can gidansu kuma Alh Adamu ya gama gigicewa. Yana matukar son jikarsa shiyasa hankalinsa ya tashi. Karshe yace don Allah suyi hakuri zai bisu asibitin. Idan komai ya lafa sai su karasa abinda ya tara su. Duk da wasu basu ji dadi ba to amma lafiya tafi komai. Haka suma aka samu wasu cikinsu suka bi bayansu aka tafi asibiti.
Ainau ce ta kira Yassar ta fada masa. Kafin ya karasa asibitin ya kira Col. Ishaq ya sanar dashi da kuma sunan asibitin. Shima hankalinsa a tashe ya tafi. Dama yayi ta kiran wayar Asmau yau baya samu. Niyarsa bayan magariba yaje gidan.
*****
Emergency suka kaita nan da nan likitoci suka fara aikinsu. Sun tabbatar musu ba abin damuwa bane asthma dinta ce ta tashi amma abin baiyi tsanani ba.
Ana ta rarrashin Asmau ta kasa shiru. Dama can hankalinta ba a kwance yake ba. Suna nan aka canza mata daki lokacin numfashin ta daidaita ta sami bacci. Qasim ya shigo dakin aka gaisa ya duba Amatullah ya fita. Bai dade da fita ba Jafar yace taje waje Qasim na kiranta.
Bata son nunawa mutane rashin son auren shiyasa ta fita ta same shi. Kokarin kwantar mata da hankali yayi tace ta gode. Suna nan tsaye Col. Ishaq ya iso. Tunda idonsa ya gano masa Asmau da Qasim yaji wani bacin rai sai dai jikin Amatullah ne a gabansa. Daya karaso suka gaisa da Qasim. Itama ta gaisheshi sai ya shareta kawai. Tana kallo Yassar ya fito ya kaishi dakin ya duba Amatullah.
Kasa nutsuwa yayi ya fito ya dawo inda suke. Gaban Asmau sai faduwa yake yi. Yana zuwa yace
"Naga dakin a ciki da mutane da yawa. Tun yaushe ta fara ciwon ban sani ba?"
Qasim ne ya bashi amsa "ko awa daya ba'ayi ba. Mutanen ciki 'yan uwana ne dana Asmau. Kayi hakuri naso sanar da kai ma abin ne yazo a kurarren lokaci."
Idon Col. Ishaq akan Asmau yace "wane abu kenan?"
Da dan murmushi Qasim yace "kawo kudi aka zo sai ciwon Amatullah ya tashi"
Guntuwar fara'ar fuskar Col. Ishaq tuni ta bace "kudin aure??? Na wa?"
Kirjin Asmau sai bugu yake da karfi don tsoro. Gashi yq tsareta da ido.
Qasim yace "kin barni ina ta magana ni kadai ko, wallahi daga fadawa iyayena kawai sai suka yanke shawarar gara ayi komai lokaci guda. kudin *aurenmu* aka zo kawowa."
Sabanin bacin ran da tayi tunanin gani a fuskar Jikamshi sai taga yayi dan murmushi
"Kasan mata da kawaici da kunya. Musamman ma dai _Matar Jikamshi_. Asma'una baki fada masa muna soyayya bane?"
Qasim ne yaji kamar an sauke masa guduma a kansa. Sai ya kalli Asmau da tayi mutuwar tsaye sannan ya kalli Col. Ishaq wanda yake binta da kallo mai nuni da tsantsar soyayya kamar ya sanyata a jikinsa.
Daga bayansu Yassar ne yazo kiran Asmau ya fada mata Amatullah ta farka. Jin abinda Col. Ishaq ya fada yasa shi daka tsalle ba shiri.
ABINDA AKE GUDU🙆🏽43
Batul Mamman💖
Shiru suka yi gaba dayansu sai Col. Ishaq da yake murmushi kamar bai san abinda yayi ba. Shi kuwa Qasim nema yake maganar da yaji ta gama shiga kwakwalwarsa. Ihun tsallen Yassar ne yasa duk suka kallo inda yake. Baiyi wani dogon tunani ba don kada a gano shi ya durkusa kasa tare da rike kafarsa ta hagu
"Wayyo Allah wani abu ne ya cije ni"
Asmau tayi kansa da sauri dama neman hanyar da zata bar wurin take yi don ji take kamar idan ta kara minti daya itama sai dai a bata gado kusa da Amatullah saboda irin bugun da zuciyarta take yi.
"Mu gani a ina ne?"
Ya dago kansa yana kallonta, duk sai ta bashi tausayi. Karyar kafar ma saboda ita yayi
"Barshi kawai bari na cire takalmin. Kije Amatullah ta tashi tana kuka"
Kamar an harba walkiya haka ta bar wurin ko waigowa baya bata yi ba. Qasim da Col Ishaq suka dawo kusa dashi suna tambayarsa abinda ya sami kafar.
"Ji nayi kamar abu ya cije ni. Ku shiga ciki Amatullah ta tashi."
Qasim ya dawo hayyacinsa daga abinda Col. Ishaq ya fada har ya yiwa Yassar sannu harda kokarin cire masa takalmin zai taya shi duba kafar. Yassar yayi saurin jan kafar yana mai jin kunyar karyar da yayi "ya dena ciwon, zan karasa motar Umma ina da silifas a ciki ina jin cinnaka ne ya shiga."
Daga haka ya samu Qasim ya shige. Kafin ya mike tsaye yaji an kama wuyan rigarsa an tayar dashi. Ba don yasan wanda ya rike shi ba sai yayi ihun gaske. Col. Ishaq yayi 'yar dariya yana kallonsa "ka kyauta da ka taimakawa yayarka don sauran kadan ta suma a wurin nan. Har na fara tunanin me zan fadawa su Umma"
Shima Yassar dariyar yayi yana murza wuyansa "haka kawai kun sata a tsakiya. Ga soja ga dan sanda da wanne zata ji"
"Laifinta ne da tasa duk muka kamu da sonta. Allah Yasa kada ta kwaso mana lauya ko alkali kuma."
Murmushi Yassar yayi tare da jin kunyar amsar da aka bashi. Shi dai komai na Col. Ishaq yana burge shi. Ina ma ace shi zai aureta. Ba kuma don baya son Qasim ba sai dai wannan maganar aure ce.
*****
Asmau na shiga dakin Amatullah ta dena kuka. Kan gadon taje ta zauna tana yi mata fadan dalilin kukan don bata ganta ba kamar bata san sauran mutanen wurin ba.
Mama tace "kiyi mata a hankali Asmau. Yarinyar nan taji jiki. Haka muka sha fama da Abubakar da yana yaro. Idan ta kara wayo zata san yadda zatayi ta rinka kiyayewa sai kiga attacks din basa zuwa sosai."
'Yan uwan Qasim suka ce zasu tafi sai dai su dawo wani satin. Alh Adamu yayi ta basu hakuri yace tunda Amatullah taji sauki suna iya komawa a karasa. Hakan ya razana Asmau sosai ta shiga rarraba idanu taji me Jikamshi zai ce. Sai tayi sa'a yayi kamar baya jinsu. Su din ma sun nuna babu damuwa tunda yamma tayi zasu sake saka rana.
Ita dai Asmau ko kallon Qasim din ta kasa. To da wane idon zata kalle shi bayan abinda Jikamshi ya fada masa. Shi a rayuwarsa ta kula baya jin shakkar fadin magana ko a gaban waye indai yana tunanin akan gaskiyarsa ne. Gashi yau ya fadi maganar da tasan dole Qasim ya kullaceta a ransa.
Shima a nasa bangaren gani yayi gara ya kyaleta saboda asibiti ba muhallin maganar bane. Sannan ga Amatullah babu lafiya yanzu ko me zata fada masa zai zamto babu nutsuwa a tare da ita. Tare da su Alh Adamu suka fita raka 'yan uwansa zasu biya gidan Umma su dauko sauran. Kayan ciye ciye da aka tanadar musu Umma tasa Sabira da Shemau su bi bayansu sai su hada a basu su tafi dashi.
*****
Suna zaune har akayi magariba sannan su Umma suka tafi aka bar Hajjo da Asmau. Kayan kwana za'a hadu musu sai Mama ta dawo su kwana tare. Col. Ishaq yana dakin amma shima yaki kallon inda Asmau take, shima bata da abin fada masa. Ba don ciwon Amatullah ba da yanzu an gama magana tsakaninta da Qasim sai batun saka rana. Biyewa Amatullah yayi tana ta shagwaba son ranta, sai Hajjo dake dan yi masa hira itan ma kunyarsa take ji tunda tasan komai. Duk yadda Asmau taso su hada ido yaki. So take ta bashi hakuri tunda tasan yanzu bata da sauran mafita. Karshenta kafin sati ya zagayo ma mutanen Shanono su sake dawowa.
Shigowar Jafar da Qasim yasa shi tashi yayi musu sallama ya fita.
Damarta kenan ta bashi hakuri a yau tunda wayarta tana gida. Bai dade da fita ba tace zata je tambayar likita ko zata iya bawa Amatullah abinci. Jafar yace ta bari yaje ta wayance "barshi Yaya Jafar so nake na dan fita na gaji da zaman wuri daya"
Shi kuwa Qasim tuni ya gane inda take son zuwa sai kawai ya dauke kansa. Yana kallo ta fita cikin sauri don kada ya bar asibitin kafin ta karasa wajen.
Tana fitowa ko alamunsa babu ta kara sauri harda dan gudunta. Tsoronta bai wuce kila daga yau yaki dawowa ba. Garin sauri tabi wata hanyar da zata kaita wurin ajiye motoci ta kusa karo da mutum har sai da taji tsoro saboda rashin wadatar haske a wurin. Tsaye yake ya sanya hannuwansa a aljihun wando yana kallonta. Kallo ne na tuhuma wanda har ranta sai da taji babu dadi don bata kyauta masa ba. Bai motsa daga inda yake ba yace "me yasa kika wahalar da kanki da yin gudu bayan kinsan dole zan jira fitowarki. You have alot of explaining to do"
Fuskarsa yau babu fara'ar nan da take kara saka mata sonsa. Yau a sojansa ya fito sai ta daburce ta rasa ta ina zata fara bayani.
"Kinyi shiru, na tafi ne?"
"A'a don Allah kayi hakuri" sai ta soma kuka.
"Matar Jikamshi" sai yanzu ta danji sanyi a ranta saboda yadda ya kirata. A hankali ta dago ido ta kalle shi.
"Why?" Ya tambaya shima duk dakewarsa yana jin babu dadi. Idan ya rasa Asmau gani yake bazai taba samun madadinta ba. Yana mamakin irin wannan so da yake mata wanda ya shige shi lokaci daya.
Idanunta cike da hawaye ta soma fada masa yadda abin ya faru." Kayi hakuri da ban sanar da kai ba. Babu yadda zanyi ne tunda duk iyaye sun amince"
Ganin Amatullah na numfashi da kyar Shemau ta karbeta Sabira kuma ta kira Jafar a waya. Lokacin Umma har ta dauko mukullin tata motar. Yassar baya gidan shi tun safe ya fice.
Sabira na fadawa Jafar ya tashi da sauri. Lokacin an gama gaisawa da dangin Qasim kenan. Abdulhalim ya tambayeshi abinda ya faru ya fada musu.
Kowa sai salati suka tashi don ta nan su Umma zasu wuce.
Kafin kace meye wannan suna mota Asmau ta cire dankwali sai hijabinta kawai tana yiwa Amatullah fifita. A can gidansu kuma Alh Adamu ya gama gigicewa. Yana matukar son jikarsa shiyasa hankalinsa ya tashi. Karshe yace don Allah suyi hakuri zai bisu asibitin. Idan komai ya lafa sai su karasa abinda ya tara su. Duk da wasu basu ji dadi ba to amma lafiya tafi komai. Haka suma aka samu wasu cikinsu suka bi bayansu aka tafi asibiti.
Ainau ce ta kira Yassar ta fada masa. Kafin ya karasa asibitin ya kira Col. Ishaq ya sanar dashi da kuma sunan asibitin. Shima hankalinsa a tashe ya tafi. Dama yayi ta kiran wayar Asmau yau baya samu. Niyarsa bayan magariba yaje gidan.
*****
Emergency suka kaita nan da nan likitoci suka fara aikinsu. Sun tabbatar musu ba abin damuwa bane asthma dinta ce ta tashi amma abin baiyi tsanani ba.
Ana ta rarrashin Asmau ta kasa shiru. Dama can hankalinta ba a kwance yake ba. Suna nan aka canza mata daki lokacin numfashin ta daidaita ta sami bacci. Qasim ya shigo dakin aka gaisa ya duba Amatullah ya fita. Bai dade da fita ba Jafar yace taje waje Qasim na kiranta.
Bata son nunawa mutane rashin son auren shiyasa ta fita ta same shi. Kokarin kwantar mata da hankali yayi tace ta gode. Suna nan tsaye Col. Ishaq ya iso. Tunda idonsa ya gano masa Asmau da Qasim yaji wani bacin rai sai dai jikin Amatullah ne a gabansa. Daya karaso suka gaisa da Qasim. Itama ta gaisheshi sai ya shareta kawai. Tana kallo Yassar ya fito ya kaishi dakin ya duba Amatullah.
Kasa nutsuwa yayi ya fito ya dawo inda suke. Gaban Asmau sai faduwa yake yi. Yana zuwa yace
"Naga dakin a ciki da mutane da yawa. Tun yaushe ta fara ciwon ban sani ba?"
Qasim ne ya bashi amsa "ko awa daya ba'ayi ba. Mutanen ciki 'yan uwana ne dana Asmau. Kayi hakuri naso sanar da kai ma abin ne yazo a kurarren lokaci."
Idon Col. Ishaq akan Asmau yace "wane abu kenan?"
Da dan murmushi Qasim yace "kawo kudi aka zo sai ciwon Amatullah ya tashi"
Guntuwar fara'ar fuskar Col. Ishaq tuni ta bace "kudin aure??? Na wa?"
Kirjin Asmau sai bugu yake da karfi don tsoro. Gashi yq tsareta da ido.
Qasim yace "kin barni ina ta magana ni kadai ko, wallahi daga fadawa iyayena kawai sai suka yanke shawarar gara ayi komai lokaci guda. kudin *aurenmu* aka zo kawowa."
Sabanin bacin ran da tayi tunanin gani a fuskar Jikamshi sai taga yayi dan murmushi
"Kasan mata da kawaici da kunya. Musamman ma dai _Matar Jikamshi_. Asma'una baki fada masa muna soyayya bane?"
Qasim ne yaji kamar an sauke masa guduma a kansa. Sai ya kalli Asmau da tayi mutuwar tsaye sannan ya kalli Col. Ishaq wanda yake binta da kallo mai nuni da tsantsar soyayya kamar ya sanyata a jikinsa.
Daga bayansu Yassar ne yazo kiran Asmau ya fada mata Amatullah ta farka. Jin abinda Col. Ishaq ya fada yasa shi daka tsalle ba shiri.
ABINDA AKE GUDU🙆🏽43
Batul Mamman💖
Shiru suka yi gaba dayansu sai Col. Ishaq da yake murmushi kamar bai san abinda yayi ba. Shi kuwa Qasim nema yake maganar da yaji ta gama shiga kwakwalwarsa. Ihun tsallen Yassar ne yasa duk suka kallo inda yake. Baiyi wani dogon tunani ba don kada a gano shi ya durkusa kasa tare da rike kafarsa ta hagu
"Wayyo Allah wani abu ne ya cije ni"
Asmau tayi kansa da sauri dama neman hanyar da zata bar wurin take yi don ji take kamar idan ta kara minti daya itama sai dai a bata gado kusa da Amatullah saboda irin bugun da zuciyarta take yi.
"Mu gani a ina ne?"
Ya dago kansa yana kallonta, duk sai ta bashi tausayi. Karyar kafar ma saboda ita yayi
"Barshi kawai bari na cire takalmin. Kije Amatullah ta tashi tana kuka"
Kamar an harba walkiya haka ta bar wurin ko waigowa baya bata yi ba. Qasim da Col Ishaq suka dawo kusa dashi suna tambayarsa abinda ya sami kafar.
"Ji nayi kamar abu ya cije ni. Ku shiga ciki Amatullah ta tashi."
Qasim ya dawo hayyacinsa daga abinda Col. Ishaq ya fada har ya yiwa Yassar sannu harda kokarin cire masa takalmin zai taya shi duba kafar. Yassar yayi saurin jan kafar yana mai jin kunyar karyar da yayi "ya dena ciwon, zan karasa motar Umma ina da silifas a ciki ina jin cinnaka ne ya shiga."
Daga haka ya samu Qasim ya shige. Kafin ya mike tsaye yaji an kama wuyan rigarsa an tayar dashi. Ba don yasan wanda ya rike shi ba sai yayi ihun gaske. Col. Ishaq yayi 'yar dariya yana kallonsa "ka kyauta da ka taimakawa yayarka don sauran kadan ta suma a wurin nan. Har na fara tunanin me zan fadawa su Umma"
Shima Yassar dariyar yayi yana murza wuyansa "haka kawai kun sata a tsakiya. Ga soja ga dan sanda da wanne zata ji"
"Laifinta ne da tasa duk muka kamu da sonta. Allah Yasa kada ta kwaso mana lauya ko alkali kuma."
Murmushi Yassar yayi tare da jin kunyar amsar da aka bashi. Shi dai komai na Col. Ishaq yana burge shi. Ina ma ace shi zai aureta. Ba kuma don baya son Qasim ba sai dai wannan maganar aure ce.
*****
Asmau na shiga dakin Amatullah ta dena kuka. Kan gadon taje ta zauna tana yi mata fadan dalilin kukan don bata ganta ba kamar bata san sauran mutanen wurin ba.
Mama tace "kiyi mata a hankali Asmau. Yarinyar nan taji jiki. Haka muka sha fama da Abubakar da yana yaro. Idan ta kara wayo zata san yadda zatayi ta rinka kiyayewa sai kiga attacks din basa zuwa sosai."
'Yan uwan Qasim suka ce zasu tafi sai dai su dawo wani satin. Alh Adamu yayi ta basu hakuri yace tunda Amatullah taji sauki suna iya komawa a karasa. Hakan ya razana Asmau sosai ta shiga rarraba idanu taji me Jikamshi zai ce. Sai tayi sa'a yayi kamar baya jinsu. Su din ma sun nuna babu damuwa tunda yamma tayi zasu sake saka rana.
Ita dai Asmau ko kallon Qasim din ta kasa. To da wane idon zata kalle shi bayan abinda Jikamshi ya fada masa. Shi a rayuwarsa ta kula baya jin shakkar fadin magana ko a gaban waye indai yana tunanin akan gaskiyarsa ne. Gashi yau ya fadi maganar da tasan dole Qasim ya kullaceta a ransa.
Shima a nasa bangaren gani yayi gara ya kyaleta saboda asibiti ba muhallin maganar bane. Sannan ga Amatullah babu lafiya yanzu ko me zata fada masa zai zamto babu nutsuwa a tare da ita. Tare da su Alh Adamu suka fita raka 'yan uwansa zasu biya gidan Umma su dauko sauran. Kayan ciye ciye da aka tanadar musu Umma tasa Sabira da Shemau su bi bayansu sai su hada a basu su tafi dashi.
*****
Suna zaune har akayi magariba sannan su Umma suka tafi aka bar Hajjo da Asmau. Kayan kwana za'a hadu musu sai Mama ta dawo su kwana tare. Col. Ishaq yana dakin amma shima yaki kallon inda Asmau take, shima bata da abin fada masa. Ba don ciwon Amatullah ba da yanzu an gama magana tsakaninta da Qasim sai batun saka rana. Biyewa Amatullah yayi tana ta shagwaba son ranta, sai Hajjo dake dan yi masa hira itan ma kunyarsa take ji tunda tasan komai. Duk yadda Asmau taso su hada ido yaki. So take ta bashi hakuri tunda tasan yanzu bata da sauran mafita. Karshenta kafin sati ya zagayo ma mutanen Shanono su sake dawowa.
Shigowar Jafar da Qasim yasa shi tashi yayi musu sallama ya fita.
Damarta kenan ta bashi hakuri a yau tunda wayarta tana gida. Bai dade da fita ba tace zata je tambayar likita ko zata iya bawa Amatullah abinci. Jafar yace ta bari yaje ta wayance "barshi Yaya Jafar so nake na dan fita na gaji da zaman wuri daya"
Shi kuwa Qasim tuni ya gane inda take son zuwa sai kawai ya dauke kansa. Yana kallo ta fita cikin sauri don kada ya bar asibitin kafin ta karasa wajen.
Tana fitowa ko alamunsa babu ta kara sauri harda dan gudunta. Tsoronta bai wuce kila daga yau yaki dawowa ba. Garin sauri tabi wata hanyar da zata kaita wurin ajiye motoci ta kusa karo da mutum har sai da taji tsoro saboda rashin wadatar haske a wurin. Tsaye yake ya sanya hannuwansa a aljihun wando yana kallonta. Kallo ne na tuhuma wanda har ranta sai da taji babu dadi don bata kyauta masa ba. Bai motsa daga inda yake ba yace "me yasa kika wahalar da kanki da yin gudu bayan kinsan dole zan jira fitowarki. You have alot of explaining to do"
Fuskarsa yau babu fara'ar nan da take kara saka mata sonsa. Yau a sojansa ya fito sai ta daburce ta rasa ta ina zata fara bayani.
"Kinyi shiru, na tafi ne?"
"A'a don Allah kayi hakuri" sai ta soma kuka.
"Matar Jikamshi" sai yanzu ta danji sanyi a ranta saboda yadda ya kirata. A hankali ta dago ido ta kalle shi.
"Why?" Ya tambaya shima duk dakewarsa yana jin babu dadi. Idan ya rasa Asmau gani yake bazai taba samun madadinta ba. Yana mamakin irin wannan so da yake mata wanda ya shige shi lokaci daya.
Idanunta cike da hawaye ta soma fada masa yadda abin ya faru." Kayi hakuri da ban sanar da kai ba. Babu yadda zanyi ne tunda duk iyaye sun amince"