Sashe 36
Abinda Ake Gudu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Muryarsa da komai nasa daban take jinsa. Ga wani girmansa da take gani a kullum. Lumshe ido tayi batare da tayi koda gyaran murya ba.
"Idan kin janye yajin aikin yi min magana ki fada min zan zo na ganki. Ina Princess dina?"
Mika mata wayar tayi ta fara bashi labarin tun dazu suke cikin mota suna ta tafiya. Ina zasu je da safen nan ya tambayi kansa. Sai kuma ya tambayeta waye yake tuka motar tace Uncle Yassay ne. Yana son jin inda zasu je amma kuma baya son tilasta Asmau tayi masa magana. Karshe yace tace masa ya kirashu idan sun tsaya. Bata ajiye wayar ba ta fadi sakon. Yassar yasa Ainau ta danna speaker a wayar. Gaisawa suka yi ya fada masa inda zasu je. Col. Ishaq yace to a kula masa da 'yarsa.
Sai da ya ajiye wayar ya hau tunanin ko kwana nawa zasuyi. Kwana biyun da baiji murya ko yaga Asmau ba baya jindadi.
*****
A gidan Anti Bintu yau tun safe suke kitchen ita da 'ya'yanta. Yadda kasan bata ga Asmau ba bayan dawowarta haka take ji. Maman mijinta Kawu Yuduf tana gidan ana gyara a nata gidan. Tun da taga suna aikin nam take tabe baki tana kananan surutai. Bata tashi yin magana sosai ba sai da taji tsayuwar mota taga duk sun fita tarbarsu Asmau. Suna shigowa ta ganeta don dama ta santa. Yar tsohuwa tace
"Yanzu duk wannan doki da murnar na ganin shegiya ne da uwarta, banda lalacecar zamani yaushe 'ya zatayi zina sannan a rinka rawar jiki don ta dawo kamar wadda tayi wani abin arziki"
Anti Bintu ta rasa me zata ce don tsabar kunya. Asmau kuwa tuni ta soma zubar da hawaye. Babbar 'yar Anti Bintu da ake shirin aurarwa bata rai tace "haba Gwaggo"
"Wane irin haba, barni nayi magana son raina. Ba 'yar zinar bace ko kuwa uwarta bata bar mata abin kunya ba na 'ya'ya da jikoki?"
Ba Asmau ba hatta Aina'u sai da tayi kuka. Allah Ya rufa musu asiri ma Kawu Yusuf yana gidan ya fito daidai sanda babarsa ke yabawa Asmau maganganu.
"Gwaggo me ya kawo wannan maganar kuma. Kaddara ce wacce bata wuce kan kowa"
"A'a wallahi irin wannan kaddarar sai 'ya'yan da basu da tsayayye a kansu. Nawa jikokin Allah Ya tsare min su. Kowacce zata kai budurcinta gidan miji"
Kuka wiwi Asmau take yi. Kukan nata ba don abinda Gwaggo ta fada bane ai duk abinda tace gaskiya ne. Gaskiya kuwa akwaita da daci. Lallai sun tafka babban kuskure a rayuwarsu kuma muddin tana numfashi tasan wannan abu bazai taba gogewa daga zukatan mutane ba. Mutumci madara ne idan ya zube ba'a taba iya kwashe shi gabadaya.
Anti Bintu ta kaisu dakinta tana ta rarrashi da bata baki. Yassar ya kasa zama ya fice ya koma mota rai a bace. Allah Kadai muke yiwa laifi yafe mana baki daya amma indai dan adam ne to a kowane lokaci ya sami dama sai ya tuna mana da laifinmu ko da bisa kuskure ne. Hakika shaidan dole yayi murna idan yaci galaba ya sanya mutane suka aikata zina domin tabonta baya taba kankaruwa a duniyar mutane dai.
Yassar na zaune ransa sai suya yake. Ko kadan abinda aka fadawa yayarsa baiyi masa dadi ba. Mutane basu san laifi indai Allah akayiwa kuma aka tuba Shi mai yawan gafara ne da jinkai. Yamadidi da mai laifi bashi daga cikin kyawawan halayen musulmi. Tsaki yayi ya dauki wayarsa ya kira Col. Ishaq dama ya karbi numbar a wurin Asmau. Ya sanar dashi sun iso lafiya sai dai tuni ya gano akwai abinda yake damun Yassar din. Yayi ta tambayarsa me ya faru ya dage babu komai. Hankalinsa ne ya tashi ya kira Asmau.
A lokacin Anti Bintu har da mijinta sun gama bata baki sun fita akan sai tayi hakuri domin zata yi ta cin karo da irin haka.
Tana ganin wayar batayi tunani komai ba ta dauka.
Wannan muryar mai dadi taji yace "Ummin Safina"
Fashewa tayi da kuka mai tsuma zuciya wanda ya sashi saurin tashi daga zaman da yayi.
"Asmau me ya ya sameki?"
Shasshekar kukanta ya cigaba da ji ya sake kiran sunanta har lokacin bata amsa ba. Hankalinsa a tashe yace "Asmau please ki amsa mana"
"Naam" ta fada cikin muryar kuka.
To me aka yi mata haka?duk yadda akayi abin ya shafi 'yan uwanta tunda yaji Yassar ma ransa a bace.
"Kina son ganin Jikamshin ki?" Ya fada cikin wata irin murya.
"Naam" ta sake fada da alamar tambaya duk da kukan da take yi.
"Kinji me nace fa ni bana son gulma. In zo ki ganni ki fada min damuwarki?"
Sake kankame wayar tayi tana jindadin maganarsa harda dan murmushi.
"Kinyi shiru ko ba kya son gani na?"
"Eh" sai tayi saurin cewa "a'a" tun kafin ya sake magana.
"Ban san abinda ya saka min ke kuka ba amma ki rinka jira sai ina wuri kiyi kuka don na rarrasheki. I will see you soon in sha Allah"
Bai jira tayi magana ba ya katse wayar ya tashi ya tafi office din abokinsa.
SADAUKARWA GAREKU
*MATAN KWARAI NA SAMI SAKON GAISUWA
*UMMUL DIHYAH, HASSANA, USAINA, AMINA DA RUQAYYA.
SAURA MASU GAISUWA DUK BAN MANTA DAKU BA. NAGODE
ABINDA AKE GUDU🙆🏽38
Batul Mamman💖
Har karfe tara na dare ta wuce Col. Ishaq bashi da niyar tafiya. Hira suke yi da Anti Bintu da Kawu Yusuf kamar sun dade da sani juna. Sai ko Amatullah da ta tare a falon tana jikinsa tun bayan tashinta daga bacci. Hatta masallaci da ita suka je da Yassar. Maman Kawu Yusuf kuwa tana daga daki tuni tayi bacci bata san wainar da ake toyawa ba.
Asmau tana tare da 'yan uwanta suna tasu hirar amma tana tunanin yaushe Jikamshi zai tafi ne. Gashi a dalilin zuwansa Yassar yayi biris da zancen komawa Kano. Ainau ta dauki waya zata kira babbar Yaya wato Shemau ta tsegumta mata abinda ke faruwa a Zaria Asmau ta hanata.
"Naga alama sai da ya tofeku tas ya shigo gidan nan. Kowa sai wani kokarin kyautata masa yakeyi"
Ainau tayi dariya "ki ce hakan baya miki dadi duk sai mu daure fuska"
"Yaya Asmau mu dai kada ki cucemu ki hanamu zuwa bikin sojoji. Kinsan babu abinda ke bani sha'awa kamar su hada takubba amarya da ango su wuce ta tsakiya." Dijah ta fada tana hango ranar bikin.
Daga nan suka shiga tsara biki harda irin kayan da zasu saka. Tun Asmau na hanasu har ta koma sakin baki tana jin yadda suke bayani kamar gobe ne daurin aure. Da ta gaji tace "to amarori sai kuyi hakuri zan bata muku show amma ni bani da niyar aure, dadin abin ma ba cewa yayi yana sona ba kuke ta rawar kai"
Ainau tace "jiran *I love you*kike sai kace wata matar da. Yanzu ai alama kawai ta isheki. Dazu fa da na fito falo ba karamar kunya naji ba yadda yake yi miki ga Anti Bintu a wurin."
Bata da abin cewa da zai hanasu abinda suke yi sai kawai ta kyalesu.
*****
A falon Col. Ishaq yace zai nemi wurin kwana gobe da sassafe ya kama hanyar Kano don ba da niyar kwana yazo ba. Yassar yaso binsa masaukin da zai nema sai dai yadda Anti Bintu ke kallonsa ya gane rashin dacewar hakan ko don kada ya dora masa nauyi. Tace ya daure ya biyo ta gidan yayi breakfast sannan ya wuce. Ya tashi yana yi musu godiyar irin karramawar da suka yi masa, suma suna masa godiyar ziyarar da ya kawo musu.
A waje ya tsaya da Amatullah wurin motarsa ya tura Yassar ya kirawo masa Asmau. Daga shiga sallar magriba bata sake fitowa ba. Gabadaya kewarta ta dameshi. Don kada aga rashin kunyarsa tayi yawa ne da tuni ya nemeta saboda ziyarar ma don ita yayi.
Tasha tsokana a dakin kafin ta fito. Yassar ne mai yi musu jan ido su dena damun matar ubangidansa. Yana fadin haka ta dage ta kai masa dundu a baya tana cewa duk sun raina ta amma zatayi maganinsu.
Tana sakkowa daga matattakalar kofar wajen yana ta kallonta har sai da ta kusa faduwa saboda yadda kafarta ke hardewa. Yayi saurin zuwa inda take yana mata sannu ta dan daure fuska. Yayi murmushi
"ashe dai kema kina jin yadda nake ji Asmau."
"Nake jin me?"
"Dazu garin kallona kika kusa bugewa da bango, yanzu kuma gashi kina neman faduwa" yayi mata murmushi "idan muka yi aure anya zaki bari na rinka zuwa aiki?"
Tafa hannu tayi tana girgiza kai sannan tace "ni bansan me zan ce maka ba ma."
"Babu abin fada ne tunda kinsan gaskiya"
Ya bawa Amatullah ledar alawa yace ta shiga ciki yana zuwa. Sai da ta nunawa Asmau tayi masa godiya sannan ta shiga ciki.
Yace "gara ta koma cikin gida kada ki koya mata soyayya tun yanzu"
Dan cije lebenta tayi tana murmushi. Har kasan zuciyarta ta amince tana son Col. Ishaq. Bata san lokacin da ta kira sunansa ba a can ciki tana mai jan sunan.
_Jikamshi_"
Wani irin sonta yaji yana kara shigarsa. Bai taba damuwa da sunan garinsu ba amma saboda dashi Asmau take kiransa har wani dadi yake ji na daban.
"Yes dear"
Ta sunkuyar da kanta kasa "wai so...so"
"Ki fadi abinda zaki fada bana son jan rai. Ko don kinga ina son muryarki. Hmmm? Sai ki rinka kara hargitsani da ita."
Murmushi ta sake yi shima yayi. Yana jindadi idan yaga ta saki jikinta tana fara'a kamar kowa. Tace
"Wai soyayya muke yi"?
"A'a a filin yakin duniya na uku muke" ya bata amsa yana daga gira.
"Kina so nayi miki gwari gwari ne sai ki fi fahimta?"
Ta kawar da kanta gefe cike da kunya da fargaba. Muryarsa taji yace "Ina sonki Asmau Ummin Safina. Babban burina yanzu bai wuce na aurenki ba da kasancewa tare daku har karshen rayuwata. Kuma zuciyata tana bani kema abinda ke taki zuciyar kenan. Right?"
"Idan kin janye yajin aikin yi min magana ki fada min zan zo na ganki. Ina Princess dina?"
Mika mata wayar tayi ta fara bashi labarin tun dazu suke cikin mota suna ta tafiya. Ina zasu je da safen nan ya tambayi kansa. Sai kuma ya tambayeta waye yake tuka motar tace Uncle Yassay ne. Yana son jin inda zasu je amma kuma baya son tilasta Asmau tayi masa magana. Karshe yace tace masa ya kirashu idan sun tsaya. Bata ajiye wayar ba ta fadi sakon. Yassar yasa Ainau ta danna speaker a wayar. Gaisawa suka yi ya fada masa inda zasu je. Col. Ishaq yace to a kula masa da 'yarsa.
Sai da ya ajiye wayar ya hau tunanin ko kwana nawa zasuyi. Kwana biyun da baiji murya ko yaga Asmau ba baya jindadi.
*****
A gidan Anti Bintu yau tun safe suke kitchen ita da 'ya'yanta. Yadda kasan bata ga Asmau ba bayan dawowarta haka take ji. Maman mijinta Kawu Yuduf tana gidan ana gyara a nata gidan. Tun da taga suna aikin nam take tabe baki tana kananan surutai. Bata tashi yin magana sosai ba sai da taji tsayuwar mota taga duk sun fita tarbarsu Asmau. Suna shigowa ta ganeta don dama ta santa. Yar tsohuwa tace
"Yanzu duk wannan doki da murnar na ganin shegiya ne da uwarta, banda lalacecar zamani yaushe 'ya zatayi zina sannan a rinka rawar jiki don ta dawo kamar wadda tayi wani abin arziki"
Anti Bintu ta rasa me zata ce don tsabar kunya. Asmau kuwa tuni ta soma zubar da hawaye. Babbar 'yar Anti Bintu da ake shirin aurarwa bata rai tace "haba Gwaggo"
"Wane irin haba, barni nayi magana son raina. Ba 'yar zinar bace ko kuwa uwarta bata bar mata abin kunya ba na 'ya'ya da jikoki?"
Ba Asmau ba hatta Aina'u sai da tayi kuka. Allah Ya rufa musu asiri ma Kawu Yusuf yana gidan ya fito daidai sanda babarsa ke yabawa Asmau maganganu.
"Gwaggo me ya kawo wannan maganar kuma. Kaddara ce wacce bata wuce kan kowa"
"A'a wallahi irin wannan kaddarar sai 'ya'yan da basu da tsayayye a kansu. Nawa jikokin Allah Ya tsare min su. Kowacce zata kai budurcinta gidan miji"
Kuka wiwi Asmau take yi. Kukan nata ba don abinda Gwaggo ta fada bane ai duk abinda tace gaskiya ne. Gaskiya kuwa akwaita da daci. Lallai sun tafka babban kuskure a rayuwarsu kuma muddin tana numfashi tasan wannan abu bazai taba gogewa daga zukatan mutane ba. Mutumci madara ne idan ya zube ba'a taba iya kwashe shi gabadaya.
Anti Bintu ta kaisu dakinta tana ta rarrashi da bata baki. Yassar ya kasa zama ya fice ya koma mota rai a bace. Allah Kadai muke yiwa laifi yafe mana baki daya amma indai dan adam ne to a kowane lokaci ya sami dama sai ya tuna mana da laifinmu ko da bisa kuskure ne. Hakika shaidan dole yayi murna idan yaci galaba ya sanya mutane suka aikata zina domin tabonta baya taba kankaruwa a duniyar mutane dai.
Yassar na zaune ransa sai suya yake. Ko kadan abinda aka fadawa yayarsa baiyi masa dadi ba. Mutane basu san laifi indai Allah akayiwa kuma aka tuba Shi mai yawan gafara ne da jinkai. Yamadidi da mai laifi bashi daga cikin kyawawan halayen musulmi. Tsaki yayi ya dauki wayarsa ya kira Col. Ishaq dama ya karbi numbar a wurin Asmau. Ya sanar dashi sun iso lafiya sai dai tuni ya gano akwai abinda yake damun Yassar din. Yayi ta tambayarsa me ya faru ya dage babu komai. Hankalinsa ne ya tashi ya kira Asmau.
A lokacin Anti Bintu har da mijinta sun gama bata baki sun fita akan sai tayi hakuri domin zata yi ta cin karo da irin haka.
Tana ganin wayar batayi tunani komai ba ta dauka.
Wannan muryar mai dadi taji yace "Ummin Safina"
Fashewa tayi da kuka mai tsuma zuciya wanda ya sashi saurin tashi daga zaman da yayi.
"Asmau me ya ya sameki?"
Shasshekar kukanta ya cigaba da ji ya sake kiran sunanta har lokacin bata amsa ba. Hankalinsa a tashe yace "Asmau please ki amsa mana"
"Naam" ta fada cikin muryar kuka.
To me aka yi mata haka?duk yadda akayi abin ya shafi 'yan uwanta tunda yaji Yassar ma ransa a bace.
"Kina son ganin Jikamshin ki?" Ya fada cikin wata irin murya.
"Naam" ta sake fada da alamar tambaya duk da kukan da take yi.
"Kinji me nace fa ni bana son gulma. In zo ki ganni ki fada min damuwarki?"
Sake kankame wayar tayi tana jindadin maganarsa harda dan murmushi.
"Kinyi shiru ko ba kya son gani na?"
"Eh" sai tayi saurin cewa "a'a" tun kafin ya sake magana.
"Ban san abinda ya saka min ke kuka ba amma ki rinka jira sai ina wuri kiyi kuka don na rarrasheki. I will see you soon in sha Allah"
Bai jira tayi magana ba ya katse wayar ya tashi ya tafi office din abokinsa.
SADAUKARWA GAREKU
*MATAN KWARAI NA SAMI SAKON GAISUWA
*UMMUL DIHYAH, HASSANA, USAINA, AMINA DA RUQAYYA.
SAURA MASU GAISUWA DUK BAN MANTA DAKU BA. NAGODE
ABINDA AKE GUDU🙆🏽38
Batul Mamman💖
Har karfe tara na dare ta wuce Col. Ishaq bashi da niyar tafiya. Hira suke yi da Anti Bintu da Kawu Yusuf kamar sun dade da sani juna. Sai ko Amatullah da ta tare a falon tana jikinsa tun bayan tashinta daga bacci. Hatta masallaci da ita suka je da Yassar. Maman Kawu Yusuf kuwa tana daga daki tuni tayi bacci bata san wainar da ake toyawa ba.
Asmau tana tare da 'yan uwanta suna tasu hirar amma tana tunanin yaushe Jikamshi zai tafi ne. Gashi a dalilin zuwansa Yassar yayi biris da zancen komawa Kano. Ainau ta dauki waya zata kira babbar Yaya wato Shemau ta tsegumta mata abinda ke faruwa a Zaria Asmau ta hanata.
"Naga alama sai da ya tofeku tas ya shigo gidan nan. Kowa sai wani kokarin kyautata masa yakeyi"
Ainau tayi dariya "ki ce hakan baya miki dadi duk sai mu daure fuska"
"Yaya Asmau mu dai kada ki cucemu ki hanamu zuwa bikin sojoji. Kinsan babu abinda ke bani sha'awa kamar su hada takubba amarya da ango su wuce ta tsakiya." Dijah ta fada tana hango ranar bikin.
Daga nan suka shiga tsara biki harda irin kayan da zasu saka. Tun Asmau na hanasu har ta koma sakin baki tana jin yadda suke bayani kamar gobe ne daurin aure. Da ta gaji tace "to amarori sai kuyi hakuri zan bata muku show amma ni bani da niyar aure, dadin abin ma ba cewa yayi yana sona ba kuke ta rawar kai"
Ainau tace "jiran *I love you*kike sai kace wata matar da. Yanzu ai alama kawai ta isheki. Dazu fa da na fito falo ba karamar kunya naji ba yadda yake yi miki ga Anti Bintu a wurin."
Bata da abin cewa da zai hanasu abinda suke yi sai kawai ta kyalesu.
*****
A falon Col. Ishaq yace zai nemi wurin kwana gobe da sassafe ya kama hanyar Kano don ba da niyar kwana yazo ba. Yassar yaso binsa masaukin da zai nema sai dai yadda Anti Bintu ke kallonsa ya gane rashin dacewar hakan ko don kada ya dora masa nauyi. Tace ya daure ya biyo ta gidan yayi breakfast sannan ya wuce. Ya tashi yana yi musu godiyar irin karramawar da suka yi masa, suma suna masa godiyar ziyarar da ya kawo musu.
A waje ya tsaya da Amatullah wurin motarsa ya tura Yassar ya kirawo masa Asmau. Daga shiga sallar magriba bata sake fitowa ba. Gabadaya kewarta ta dameshi. Don kada aga rashin kunyarsa tayi yawa ne da tuni ya nemeta saboda ziyarar ma don ita yayi.
Tasha tsokana a dakin kafin ta fito. Yassar ne mai yi musu jan ido su dena damun matar ubangidansa. Yana fadin haka ta dage ta kai masa dundu a baya tana cewa duk sun raina ta amma zatayi maganinsu.
Tana sakkowa daga matattakalar kofar wajen yana ta kallonta har sai da ta kusa faduwa saboda yadda kafarta ke hardewa. Yayi saurin zuwa inda take yana mata sannu ta dan daure fuska. Yayi murmushi
"ashe dai kema kina jin yadda nake ji Asmau."
"Nake jin me?"
"Dazu garin kallona kika kusa bugewa da bango, yanzu kuma gashi kina neman faduwa" yayi mata murmushi "idan muka yi aure anya zaki bari na rinka zuwa aiki?"
Tafa hannu tayi tana girgiza kai sannan tace "ni bansan me zan ce maka ba ma."
"Babu abin fada ne tunda kinsan gaskiya"
Ya bawa Amatullah ledar alawa yace ta shiga ciki yana zuwa. Sai da ta nunawa Asmau tayi masa godiya sannan ta shiga ciki.
Yace "gara ta koma cikin gida kada ki koya mata soyayya tun yanzu"
Dan cije lebenta tayi tana murmushi. Har kasan zuciyarta ta amince tana son Col. Ishaq. Bata san lokacin da ta kira sunansa ba a can ciki tana mai jan sunan.
_Jikamshi_"
Wani irin sonta yaji yana kara shigarsa. Bai taba damuwa da sunan garinsu ba amma saboda dashi Asmau take kiransa har wani dadi yake ji na daban.
"Yes dear"
Ta sunkuyar da kanta kasa "wai so...so"
"Ki fadi abinda zaki fada bana son jan rai. Ko don kinga ina son muryarki. Hmmm? Sai ki rinka kara hargitsani da ita."
Murmushi ta sake yi shima yayi. Yana jindadi idan yaga ta saki jikinta tana fara'a kamar kowa. Tace
"Wai soyayya muke yi"?
"A'a a filin yakin duniya na uku muke" ya bata amsa yana daga gira.
"Kina so nayi miki gwari gwari ne sai ki fi fahimta?"
Ta kawar da kanta gefe cike da kunya da fargaba. Muryarsa taji yace "Ina sonki Asmau Ummin Safina. Babban burina yanzu bai wuce na aurenki ba da kasancewa tare daku har karshen rayuwata. Kuma zuciyata tana bani kema abinda ke taki zuciyar kenan. Right?"