Sashe 35
Abinda Ake Gudu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da yamma ne ta tafi gidan Jafar saboda yace yana son ganinta tace ya bari zata zo da kanta. A gida ta bar Amatullah tana bacci. Sun dan taba hira da Sabira ta tashi ta basu wuri. Ba wani dogon abu bane maganar karatu yayi mata wanda yace sunyi shawara ne da Shemau zasu hada kudi su biya mata ta koma makaranta. Kuka take yi sosai kamar yasan abinda take son yi kenan.
"Yaya Jafar Allah Ya saka da alkhairi. Nagode sosai, nima abinda yake raina kenan don bana son nayi ta zaman haka."
"Kada ki damu Asmau. Ina so ki manta da rayuwar baya kiyi kokarin gina rayuwa mai kyau daga yanzu. Kada ki manta ko ke wacece a duk inda kike. A yanzu da kika dawo gida inda mutane suka sanki suka san labarin rayuwarki ki zauna da shiri na fuskantar kalubale kala kala. Dole duk inda kika shiga kiji maganganu marasa dadi daga bakin mutane daban daban. Abinda nake bukata daga gareki bai wuce ki toshe kunnuwanki ba. Komai yayi farko yana da karshe. Ki mayarda dukkan lamarinki ga Allah sai kiga kinyi nasara."
Tayi murmushin takaici "hakane, kuma nagode da shawararka. Dole ne nayi hakuri da dukkan abinda mutane zasu ce game dani da Amatullah. Irin labarinmu dai da wuya yake zama tarihi. Duk wanda ya sanmu duk sanda muka hadu sai sun tuna. Wannan kaddara har jikoki idan da rabo nasan za'a goranta musu wata rana" ta kare maganar da kuka.
Tausayin kanwarsa yaji sosai. Ya dade da sanin cewa illar zina tana bibiyar mutum duk inda yaje. Musamman idan akwai haihuwa tsakani. Fatanmu kawai Allah Ya tsare mana imaninmu Ya karemu daga fadawa sharrin shaidan da mukarrabansa.
"Ki tsarkake zuciyarki Asmau, daga nan ki barwa Allah komai. Rayuwa ce kowa da irin tasa. Babban abin dubawa dama shine tuba da komawa ga Allah. Idan kika yi haka to babu ruwanki da zancen mutane. Duk wanda ya fiye bibiyar kuskuren dan uwansa don tonon asiri to Allah na kallonsa kuma Shine Yasan yadda zaiyi da bayinSa."
Godiya ta sake yi masa har ta kira Shemau tace zata je har gida tayi mata godiya. Dan uwa rabin jiki inji bahaushe...banga mai kamarka ba. Abinda suka aikata ita da Abubakar ba su kadai yake bi ba domin kuwa tasan za'a nuna iyayensu da 'yan uwansu idan dalili ya kawo suma a goranta musu. Kai zina laifi ce mai muni, kazanta ce mai kaskantar da mai daraja. Ya Allah Kasa mufi karfin zukatanmu. Masu neman aure maza da mata Allah Ka basu abokan rayuwa nagari. Mu kuma Ka bamu zaman lafiya da wadanda Ka hadamu dasu.
*****
ASP Qasim zaune gaban mahaifiyarsa ya gabatar mata da zancen Asmau wanda ta dade da sanin kudurinsa akai.
"Baba ni bazan hanaka aurenta ba. Babanku ma yace ya amince da auren. Abu daya nake so da kai shine ka tuna dukkan abubuwan da suka faru. Naso kwarai kayi aure kafin yanzu ta yadda ko ka auri Asmaun zaka hadata da wata matar"
"Inna kenan, kina gudun ita kadai ta kasance surika a gareki saboda tana da 'ya kafin tayi aure?"
"Dan nan yau da gobe sai Allah. Mutane da bakinsu bazasu fasa surutu ba"
"Amma Inna nasha fada miki ina gudun zamansu da kishiya yaki dadi saboda gori. Da bata dawo ba kamar yadda kika bukata a shekarar nan zan nemi aure. Ku cigaba da yi mana addua."
Ta kada kai "Allah Ya tabbatar mana da alkhairi. Haj Yalwa tace zata zo dasu su gaishe da Malam. Allah Ya kiyaye hanya"
Qasim ya tashi ya leka dakin mahaifinsa har lokacin bacci yake yi. Shiryawa yayi cikin wani yadi mara nauyi ruwan toka yayi kyau sosai ya kama hanyar Kano daga Shanono.
Ana magariba ya iso. Gidan Mama ya fara zuwa suka gaisa sannan ya kira Asmau ya fada mata zai zo idan an idar da sallar isha. Umma taje ta sanarwa.
"Allah Sarki Qasim, gaskiya ya rike amana. Ji yadda yake kokarin kula daku duk da ba a garin nan yake aiki ba. Allah Ya biya shi da mafificin alkhairi."
Asmau ta amsa da amin tana gyara goyon Husna da tayi.
Suna cikin hira Qasim yayi sallama Umma tayi masa izini ya shigo. Cike da ladabi ya gaisheta ta amsa fuska a sake. Daga nan ta tashi ta bar falon ta koma dakin Hajjo. A nan ta sanar da Amatullah zuwan Qasim daya baban nata ta fito gaishe shi.
Qasim ya ajiye kofin lemon dake hannunsa yana maida hankalinsa Asmau.
"Asmau magana nazo muyi, ina fata zaki saurare kuma ki fahimceni."
"Ina jinka Yaya Qasim"
"Asmau kinsan irin shakuwa da abotar dake tsakanina da marigayi Abubakar"
Ta gyada kai tana tuno masoyin da bazata taba mantawa ba a tarihin rayuwarta.
"Duk abinda ya gudana a rayuwarku na sani na kuma san nima akwai sa hannuna a ciki. Bazan gaji da rokon gafararki ba saboda ance karfe daya baya amo. Kamar yadda kawa ta ribaceki haka nima nayiwa Abubakar, ga kuma sakamakon hakan duniya ta gani. Asmau tun kafin ki dawo na yanke shawarar aurenki ko a wane yanayi na sameki. Cikin ikon Allah yanzu na tsinci kaina da tsananin kaunarki"
A razane ta dago kai ta kalleshi ta mayar da kanta kasa. Yayi sassanyar dariya
"Nasan dole kiyi mamaki sai dai kuma ki sani burina ba wai na maye gurbin Abubakar bane. Ina so ki bani dama a matsayin masoyi na sami kaunarki na kuma zama uba ga 'yata Amatullah."
Wannan shine ana wata ga wata. Ita fa ko kadan bata son maganar aure ma yanzu. Qasim wani babban jigo ne a rayuwarta saboda yadda ya damu da lamarinta da na Amatullah. Ya rike amanar Abubakar ba da wasa ba.
"Yaya Qasim bani da abinda zance maka sai godiya da fatan alkhairi amma don Allah ka janye maganar aure a tsakaninmu. Maganar aure ba ta mace irina bace. Duk yadda zan so bani da wani mutumci da kima da zan kai gidan aure. Amatullah ko naki ko naso 'yarka ce amma don Allah mu bar maganar aure."
Dama yasan da wuya ta amince kai tsaye.
"Ba cewa nayi ki bani amsa yanzun nan ba. Zan baki lokaci kiyi tunani. Amma ki sani kamar yadda aure yake zama garkuwa ga kowace mace kema shine mutumcinki. Zamanki a haka shine zai janyo miki duk abinda kike gudu wato surutun mutane."
"Ni dai....."
Hannu ya daga mata alamun tayi shiru ya tashi tsaye "kiyi tunani nace kuma kiyi shawara da duk wanda kika san zai baki shawara tagari"
Rasa abin fada tayi kawai ta sanar dashi batun tafiyarsu a washegari yayi mata addua sannan yace zai zo idan ta dawo yasan lokacin tayi duk wani tunani da zata yi.
Bayan tafiyarsa Asmau ta shiga tashin hankali. Ko zata yi aure ba dai da Qasim ba. Idan ta amince tamkar taci amanar Abubakar ne. Kana ganinta kasan tana cikin damuwa ta tafi daki da niyar kwanciya wayarta ta soma kara.
Sai da gabanta ya fadi da taga sunan mai kiran. Kwana biyu tun ranar da taki amsa wayarsa bai kara kiranta ba sai yau. Zuciyarta ce ta rinka bugu da sauri da sauri amma ta kasa amsa kiran. Text taga ya turo mata
_Idan Safina batayi bacci ba ki hadani da ita. Taki muryar ma ina son ji amma ba a waya ba, so wayar ba taki bace._
Wani dan murmushi ne ya subuce mata. Sai kuma ta dan dake tana yiwa zuciyarta tuni da cewar ta manta da maganar aure. Babu wani namiji da zai aureta a yanayin da take ciki komai tsahon lokaci ace wata rana bai goranta mata irin rayuwar da tayi a baya ba.
Dakin Umma taje ta bawa Amatullah dake aikin wasa da Husna wayar da ya sake kira. Kusan minti ashirin tana ta yi masa hira sannan mikawa Asmau. Da ta karba sakawa tayi a kunnenta tayi shiru tana so taji ko ya ajiye.
Yanayin yadda take saukar da numfashi ne ya tabbatar masa ta karbi wayar. Murmushi yayi kamar tana kallonsa yace
"Ana so ana kaiwa kasuwa"
Da sauri Asmau ta kashe wayar tana dariya. Me ya kaita saka wayar a kunnenta ne. Umma tace "ke lafiyarki kuwa?"
Tayi saurin daidaita kanta. Yanzu fa ta gama cewa babu zancen aure a sauran rayuwarta. Me yasa take jin wani daban idan al'amarin ya shafi Jikamshi.
*****
Col. Ishaq yana zaune ya saka abinci a gaba bai ci ba ya soma wayar. Dariyar da yake yiwa Asmau ce tasa Hajiya kallonsa.
"Yaya dai kake dariya kai kadai? Kwana biyu na fuskanci wani nishadi kake ji."
"Hajiyata babu komai" abincin yaci dan kadan ya sa Bilkisu ta kwashe kwanukan. Wai shine tunanin mace ya mayar haka. Abin da mamaki, duk dakiya irin ta soja yanzu baya jimawa sai Asmau ta fado masa.
******
Da wuri suka tashi aka karasa shiri saboda Yassar yana son dawowa a ranar. Kafin karfe goma na safe sun hau hanya bayan sun biya gidan Mama sunyi mata sallama.
Aina'u tana gaba Asmau na zaune a baya da baby Husna da Amatullah. Sunyi nisa Qasim ya kirata. Har kunya taji saboda yace ta kirashi kafin su fito taki kira, a cewarta kada ta sa masa rai yayi zaton zata amince nan gaba. Adduar neman tsari yayi musu sannan ya gaisa da Amatullah. Ba dadewa kuma Col. Ishaq yayi mata text. Lokacin bai dade da shiga office dinsa ba.
_Zan kira ki yanzu ki fara dauka kafin ki hadani da princess dina._
Ya zata yi ne da Jikamshi. Duk irin wannan abubuwan da yake yi mata kara kashe mata jiki yake yi. A daya bangaren kuma tana ganin gangancinta da har ta bari yake tasiri a zuciyarta haka. Idan har aure ya zama dole a kanta ma bashi ya kamata ta aura ba. Qasim yafi kusanci da ita, yafi sanin dukkan matsalarta. Amma Jikamshi shine a ranki zuciyarta ta tuna mata kafin wayar ta fara ringing.
A kasalance ta daga wayar ta kara a kunnenta kamar tana jin tsoron amsawa.
Shi kadai ya sauke ajiyar zuciya da yaji ta dauka.
"Just wanted to let you know how much I miss you."
"Yaya Jafar Allah Ya saka da alkhairi. Nagode sosai, nima abinda yake raina kenan don bana son nayi ta zaman haka."
"Kada ki damu Asmau. Ina so ki manta da rayuwar baya kiyi kokarin gina rayuwa mai kyau daga yanzu. Kada ki manta ko ke wacece a duk inda kike. A yanzu da kika dawo gida inda mutane suka sanki suka san labarin rayuwarki ki zauna da shiri na fuskantar kalubale kala kala. Dole duk inda kika shiga kiji maganganu marasa dadi daga bakin mutane daban daban. Abinda nake bukata daga gareki bai wuce ki toshe kunnuwanki ba. Komai yayi farko yana da karshe. Ki mayarda dukkan lamarinki ga Allah sai kiga kinyi nasara."
Tayi murmushin takaici "hakane, kuma nagode da shawararka. Dole ne nayi hakuri da dukkan abinda mutane zasu ce game dani da Amatullah. Irin labarinmu dai da wuya yake zama tarihi. Duk wanda ya sanmu duk sanda muka hadu sai sun tuna. Wannan kaddara har jikoki idan da rabo nasan za'a goranta musu wata rana" ta kare maganar da kuka.
Tausayin kanwarsa yaji sosai. Ya dade da sanin cewa illar zina tana bibiyar mutum duk inda yaje. Musamman idan akwai haihuwa tsakani. Fatanmu kawai Allah Ya tsare mana imaninmu Ya karemu daga fadawa sharrin shaidan da mukarrabansa.
"Ki tsarkake zuciyarki Asmau, daga nan ki barwa Allah komai. Rayuwa ce kowa da irin tasa. Babban abin dubawa dama shine tuba da komawa ga Allah. Idan kika yi haka to babu ruwanki da zancen mutane. Duk wanda ya fiye bibiyar kuskuren dan uwansa don tonon asiri to Allah na kallonsa kuma Shine Yasan yadda zaiyi da bayinSa."
Godiya ta sake yi masa har ta kira Shemau tace zata je har gida tayi mata godiya. Dan uwa rabin jiki inji bahaushe...banga mai kamarka ba. Abinda suka aikata ita da Abubakar ba su kadai yake bi ba domin kuwa tasan za'a nuna iyayensu da 'yan uwansu idan dalili ya kawo suma a goranta musu. Kai zina laifi ce mai muni, kazanta ce mai kaskantar da mai daraja. Ya Allah Kasa mufi karfin zukatanmu. Masu neman aure maza da mata Allah Ka basu abokan rayuwa nagari. Mu kuma Ka bamu zaman lafiya da wadanda Ka hadamu dasu.
*****
ASP Qasim zaune gaban mahaifiyarsa ya gabatar mata da zancen Asmau wanda ta dade da sanin kudurinsa akai.
"Baba ni bazan hanaka aurenta ba. Babanku ma yace ya amince da auren. Abu daya nake so da kai shine ka tuna dukkan abubuwan da suka faru. Naso kwarai kayi aure kafin yanzu ta yadda ko ka auri Asmaun zaka hadata da wata matar"
"Inna kenan, kina gudun ita kadai ta kasance surika a gareki saboda tana da 'ya kafin tayi aure?"
"Dan nan yau da gobe sai Allah. Mutane da bakinsu bazasu fasa surutu ba"
"Amma Inna nasha fada miki ina gudun zamansu da kishiya yaki dadi saboda gori. Da bata dawo ba kamar yadda kika bukata a shekarar nan zan nemi aure. Ku cigaba da yi mana addua."
Ta kada kai "Allah Ya tabbatar mana da alkhairi. Haj Yalwa tace zata zo dasu su gaishe da Malam. Allah Ya kiyaye hanya"
Qasim ya tashi ya leka dakin mahaifinsa har lokacin bacci yake yi. Shiryawa yayi cikin wani yadi mara nauyi ruwan toka yayi kyau sosai ya kama hanyar Kano daga Shanono.
Ana magariba ya iso. Gidan Mama ya fara zuwa suka gaisa sannan ya kira Asmau ya fada mata zai zo idan an idar da sallar isha. Umma taje ta sanarwa.
"Allah Sarki Qasim, gaskiya ya rike amana. Ji yadda yake kokarin kula daku duk da ba a garin nan yake aiki ba. Allah Ya biya shi da mafificin alkhairi."
Asmau ta amsa da amin tana gyara goyon Husna da tayi.
Suna cikin hira Qasim yayi sallama Umma tayi masa izini ya shigo. Cike da ladabi ya gaisheta ta amsa fuska a sake. Daga nan ta tashi ta bar falon ta koma dakin Hajjo. A nan ta sanar da Amatullah zuwan Qasim daya baban nata ta fito gaishe shi.
Qasim ya ajiye kofin lemon dake hannunsa yana maida hankalinsa Asmau.
"Asmau magana nazo muyi, ina fata zaki saurare kuma ki fahimceni."
"Ina jinka Yaya Qasim"
"Asmau kinsan irin shakuwa da abotar dake tsakanina da marigayi Abubakar"
Ta gyada kai tana tuno masoyin da bazata taba mantawa ba a tarihin rayuwarta.
"Duk abinda ya gudana a rayuwarku na sani na kuma san nima akwai sa hannuna a ciki. Bazan gaji da rokon gafararki ba saboda ance karfe daya baya amo. Kamar yadda kawa ta ribaceki haka nima nayiwa Abubakar, ga kuma sakamakon hakan duniya ta gani. Asmau tun kafin ki dawo na yanke shawarar aurenki ko a wane yanayi na sameki. Cikin ikon Allah yanzu na tsinci kaina da tsananin kaunarki"
A razane ta dago kai ta kalleshi ta mayar da kanta kasa. Yayi sassanyar dariya
"Nasan dole kiyi mamaki sai dai kuma ki sani burina ba wai na maye gurbin Abubakar bane. Ina so ki bani dama a matsayin masoyi na sami kaunarki na kuma zama uba ga 'yata Amatullah."
Wannan shine ana wata ga wata. Ita fa ko kadan bata son maganar aure ma yanzu. Qasim wani babban jigo ne a rayuwarta saboda yadda ya damu da lamarinta da na Amatullah. Ya rike amanar Abubakar ba da wasa ba.
"Yaya Qasim bani da abinda zance maka sai godiya da fatan alkhairi amma don Allah ka janye maganar aure a tsakaninmu. Maganar aure ba ta mace irina bace. Duk yadda zan so bani da wani mutumci da kima da zan kai gidan aure. Amatullah ko naki ko naso 'yarka ce amma don Allah mu bar maganar aure."
Dama yasan da wuya ta amince kai tsaye.
"Ba cewa nayi ki bani amsa yanzun nan ba. Zan baki lokaci kiyi tunani. Amma ki sani kamar yadda aure yake zama garkuwa ga kowace mace kema shine mutumcinki. Zamanki a haka shine zai janyo miki duk abinda kike gudu wato surutun mutane."
"Ni dai....."
Hannu ya daga mata alamun tayi shiru ya tashi tsaye "kiyi tunani nace kuma kiyi shawara da duk wanda kika san zai baki shawara tagari"
Rasa abin fada tayi kawai ta sanar dashi batun tafiyarsu a washegari yayi mata addua sannan yace zai zo idan ta dawo yasan lokacin tayi duk wani tunani da zata yi.
Bayan tafiyarsa Asmau ta shiga tashin hankali. Ko zata yi aure ba dai da Qasim ba. Idan ta amince tamkar taci amanar Abubakar ne. Kana ganinta kasan tana cikin damuwa ta tafi daki da niyar kwanciya wayarta ta soma kara.
Sai da gabanta ya fadi da taga sunan mai kiran. Kwana biyu tun ranar da taki amsa wayarsa bai kara kiranta ba sai yau. Zuciyarta ce ta rinka bugu da sauri da sauri amma ta kasa amsa kiran. Text taga ya turo mata
_Idan Safina batayi bacci ba ki hadani da ita. Taki muryar ma ina son ji amma ba a waya ba, so wayar ba taki bace._
Wani dan murmushi ne ya subuce mata. Sai kuma ta dan dake tana yiwa zuciyarta tuni da cewar ta manta da maganar aure. Babu wani namiji da zai aureta a yanayin da take ciki komai tsahon lokaci ace wata rana bai goranta mata irin rayuwar da tayi a baya ba.
Dakin Umma taje ta bawa Amatullah dake aikin wasa da Husna wayar da ya sake kira. Kusan minti ashirin tana ta yi masa hira sannan mikawa Asmau. Da ta karba sakawa tayi a kunnenta tayi shiru tana so taji ko ya ajiye.
Yanayin yadda take saukar da numfashi ne ya tabbatar masa ta karbi wayar. Murmushi yayi kamar tana kallonsa yace
"Ana so ana kaiwa kasuwa"
Da sauri Asmau ta kashe wayar tana dariya. Me ya kaita saka wayar a kunnenta ne. Umma tace "ke lafiyarki kuwa?"
Tayi saurin daidaita kanta. Yanzu fa ta gama cewa babu zancen aure a sauran rayuwarta. Me yasa take jin wani daban idan al'amarin ya shafi Jikamshi.
*****
Col. Ishaq yana zaune ya saka abinci a gaba bai ci ba ya soma wayar. Dariyar da yake yiwa Asmau ce tasa Hajiya kallonsa.
"Yaya dai kake dariya kai kadai? Kwana biyu na fuskanci wani nishadi kake ji."
"Hajiyata babu komai" abincin yaci dan kadan ya sa Bilkisu ta kwashe kwanukan. Wai shine tunanin mace ya mayar haka. Abin da mamaki, duk dakiya irin ta soja yanzu baya jimawa sai Asmau ta fado masa.
******
Da wuri suka tashi aka karasa shiri saboda Yassar yana son dawowa a ranar. Kafin karfe goma na safe sun hau hanya bayan sun biya gidan Mama sunyi mata sallama.
Aina'u tana gaba Asmau na zaune a baya da baby Husna da Amatullah. Sunyi nisa Qasim ya kirata. Har kunya taji saboda yace ta kirashi kafin su fito taki kira, a cewarta kada ta sa masa rai yayi zaton zata amince nan gaba. Adduar neman tsari yayi musu sannan ya gaisa da Amatullah. Ba dadewa kuma Col. Ishaq yayi mata text. Lokacin bai dade da shiga office dinsa ba.
_Zan kira ki yanzu ki fara dauka kafin ki hadani da princess dina._
Ya zata yi ne da Jikamshi. Duk irin wannan abubuwan da yake yi mata kara kashe mata jiki yake yi. A daya bangaren kuma tana ganin gangancinta da har ta bari yake tasiri a zuciyarta haka. Idan har aure ya zama dole a kanta ma bashi ya kamata ta aura ba. Qasim yafi kusanci da ita, yafi sanin dukkan matsalarta. Amma Jikamshi shine a ranki zuciyarta ta tuna mata kafin wayar ta fara ringing.
A kasalance ta daga wayar ta kara a kunnenta kamar tana jin tsoron amsawa.
Shi kadai ya sauke ajiyar zuciya da yaji ta dauka.
"Just wanted to let you know how much I miss you."