Sashe 40
Abinda Ake Gudu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Zubaida taji dadi sosai "kinga yadda Allah ke juya lamarinSa ko. Shawarar zan baki ki yarda kiyi aure amma ki zabi wanda zuciyarki tafi so. Ni shaida ce akan irin abinda Qasim yayi da kika bata to amma nafi danganta hakan da rike amanar Abubakar da yayi. Bansan gaskiyar lamari akan menene a zuciyarsa ba yanzu. Ma'ana soyayya ce ko tausayi. Shi kuwa sojan nan dole na yaba masa. Duka duka yaushe ya sanki amma yake sonki da aure"
"Ba kya tunanin nan gaba matsala ta taso ko a kaina ko akan Amatullah"
"Hmmm Asmau kenan, ke kike da goben da har kike tunanin matsala? Yadda Allah Ya daidaita miki lamura yanzu, idan har wani abin ya taso a gaba Shi din dai zai mana magani. Kada ki manta nima ba 'yar aure bace amma Allah Ya hadani daku gashi babu wanda ya taba yi mim gori. Auren ma Hajjo ce ta hada. Zamana nake lafiya na manta da kazantar da na taso cikinta. Yadda na hadu daku da yardar Allah itama zata hadu da mutane nagari a rayuwarta"
Asmau ta sunkuyar da kanta kasa hawaye na taho mata. Duk matar da tayi zina ta gama cutar abinda ta haifa. Sai dai idan an hadu da mutane na kwarai. Kuma duk da haka haifewar itace tafi akan zubar da ciki wanda yake daidai da kisa idan an busawa jaririn rai. Mace sai ta sami rahmar Allah idan ta rungumi kaddararta ta bawa abinda ta haifa tarbiyar da ta dace da addininmu.
"Ki kara hakuri da rayuwa Asmau. Haka Allah Ya tsara miki. Ke kika zama ishara ga masu hankali wadanda idan sunji labarinki zasu san cewa biyewa sharrin yanar gizo da son zuciya halaka ne. Uwa uba babu wani alkhairi da yake tattare da shiga groups din nan na whatsapp ko facebook masu yada alfasha."
"Nagode Antina ta kaina. Allah Ya raba lafiya mu sha suna"
Dadi Zubaida taji da taga Asmau ta dan sake. Amatullah tana tsakar gida suna wasa da yaran Zubaidan.
"Tashi mu soya wainar fulawa"
Asmau ta zaro ido "yaushe muka gama cin abinci?"
Cikinta ta shafa "bani nake so ba kaninki ne ko kanwa"
"To kala masa sharri saboda bashi da baki. Ina fulawar take na hada?" Ta fada tana tashi.
Ranar dai sun wuni suna hira kuma taji dadin shawarar da Zubaida ta bata. Duniya kenan, Zubaida da ta tashi a matsayin 'yar magajiyar karuwai gashi Allah Ya sauya mata rayuwa. Sai bayan magariba Asmau tayi shirin tafiya. Dama Jafar yace zai dawo daukarta sai ya kira yace ayyuka sun masa yawa. Nan kuwa bata san suna can gidansu ana maganar aurenta bane.
Zubaida ta sake yi mata tuni akan lallai kada ta bari dama ta kubuce mata. Ta amince tayi aure
"Ni na kula sojan nan ba dai iya nuna kulawa ba. Zuwanki nan kunyi waya sau uku."
Murmushin Asmau ya tabbatar mata da zarginta na cewa shi take so. Har kofar gida ta rakata suka tafi titi suka shiga adaidaita sahu ita da Amatullah suka tafi gida..
Abin mamaki tana zuwa ta tarar da Anti Bintu tazo da yaranta wai zasuyi weekend. Tayi murna sosai. Amatullah ma ta ganesu saboda haka ta saki jiki ana hira. Umma tace idan ta huta tazo dakin Hajjo tana son ganinta. Anti Bintu Asmau ta kalla tana dan murmushi, ko dai ta fadawa Umma zuwan Jikamshi Zaria ne. Karshenta maganar aure ce. Ta riga ta kudiri niyar bin shawarar Zubaida. Zata tsananta addua ta amince da Col. I M Jikamshi.
*****
Ko kayanta bata cire ba da ta shiga daki Jikamshi ya kirata kamar yasan tunaninsa take yi a wannan lokacin.
Daukar wayar tayi tare da yin sallama.
Shima lokacin yana gida ya tasa laptop a gaba yana kallon wasu hotuna da ya dauki Amatullah. Yana son yarinyar nan, ko babu komai ta dauke shi uba sannan gashi tayi sanadiyar hadashi da Umminta. Safinansa akwai shiga rai.
Sallamar Asmau ce ta katse masa tunani ya amsa mata cikin daddadar muryarsa.
"Matar Jikamshi kun dawo gida lafiya?"
"Lafiya kalau"
"I miss you so much"
"Duk wayar da muke yi tun safe?"
Yayi yar dariya "yanzu ke hirar waya ta isheki. Ni nafi son na ganki a gabana. By the way lokacin da na baki fa yayi. Anyi sati daya ya kuka yi da Qasim?"
Shiru tayi domin kuwa bata sami biyan bukata ba. Tayi kokarin nuna masa ya hakura da zancen aure sai ya rinka danganta abin da ko tana gudun aurensa saboda tunanin Abubakar ne. Karshe yace mata ta jira nan da lahadi komai zai zo karshe.
Col Ishaq yace "ya kika yu shiru? Kada kice min bakiyi komai ba."
Sautin muryarsa kamar baiji dadi ba tace "ka kara hakuri yace na jira zuwa ranar lahadi idan yazo kamai zai zo karshe"
"Ban fahimceki ba, komai zaizo karshe kamar yaya?"
Asmau kanta bata gane abinda Qasim yake nufi ba "nima dai haka yace min"
Col. Ishaq ya tashi daga kashingidar da yayi "look Matar Jikamshi, ni mutum ne kaifi daya. Idan kina jin nauyin fada masa saboda kusancin families dinku ni zan fada masa da kaina. Tunda naga ya cigaba da yi min text da waya nasan bai san alakarmu ba. Kinga kashe wayar kawai bari na kira shi na fada masa Ishaq da Asmau suna son juna don Allah ka nemi wata"
Bata san lokacin da ta kwashe da dariya ba "yanzu don Allah sai ka fada masa haka"?
"Kin dauka wasa nake yi, yara ne suke da lokacin wasa da soyayya."
Tace "kayi hakuri zuwa lahadin please"
Yadda take magana duk ya kashe masa jiki. Zai iya hakuri amma zuwa sunday kawai. Daga nan kuwa to sai dai ayita ta kare. Shi ba don yana ganin mutuncin Qasim din ba tun ranar da ya gansu da Asmau da a lokacin zai fada masa.
"Yarinya dake duk kin rikita min lissafi. Amma zan rama ne, sai kin shigo gidanki"
"Nima fa ka rikita min"
"Me kika ce?"
Zancen zuci ne ya fito fili tayi saurin toshe bakinta. Ta rasa inda zata sa kanta don kunya. Tana ji yana mata dariya don yasan bata so yaji abinda ta fada ba.
"I love you Matar Jikamshi. Nasan bazan kara samun nutsuwa ba idan ba aurenki nayi ba. Na riga na fadawa Hajiya amsarki nake jira a fadawa iyayena maza. Idan kika zabi Qasim zan tayar da yaki a zuciyarki"
Wani dadi ne taji yana ratsata. Ashe tana da rabon samun farinciki a rayuwarta. Ita ma tana son shi kuma ta shiryawa duk wani nau'i na gori da zai iya zuwa daga danginsa. Abinda ake gudu ya riga ya faru sai dai a kiyayi gaba.
" 'yarka da Yassar ma bazasu barni ba idan na zabi wani ba kai ba. Da ka tashi sai ka hada da zuciyata data Amatullah kuma harda ta kanina."
Da tasan irin yadda yake ji a ransa da ta rage yi masa magana ko don ta sassauta masa. Ajiyar zuciya yayi har tana jin sautin
"Say you love me please" ya fada cikin sanyin murya.
Yau daya zata sakaya kunyarta ta farantawa mai faranta mata "I do love you _Jikamshina_"
Kafin ya kara magana ta kashe wayar gabadaya don tasan zai sake kira. Kwanciya tayi akan gado tana juyi ita kadai zuciyarta kamar an wanke mata.
Shi kuwa rike yake da wayar a hannu yana murmushi. Hmmm bari dai ace an daura musu aure. Ranar Asmau zata san tana da masoyi. Zaiyi iya kokarinsa wurin nuna mata soyayya da cewar itama har yanzu tana da darajarta a cikin mata. Abinda ya wuce a baya sai ayi ta addua da fatan Allah Ya yafewa musulmi kurakuransu.
*****
Tana ta maimaita hirarsu a kwakwalwarta tana dariya Amatullah ta shigo
"Ummina Umma tana kiyanki"
Ai da sauri ta sauko daga kan gadon. Shaf ta manta Umma tace tana son ganinta.
Saurin da take yi yasa Amatullah tace "Ummi guduwa zamuyi ne? Me nene akan gadon?"
Asmau tayiwa kanta dariya sannan ta dauki Amatullah tana juyi da ita. Soyayyar Jikamshi ta zame mata wani bangare mai mahimmanci a rayuwarta. Tana juyin tana dariya.
Amatullah tana tayata duk da bata san dalilin murnar Ummin ta ba
"Ummi abin dadi ne ya fayu?"
"Shine zai faru in sha Allah Ama, muma Allah zai bamu rayuwa mai tsafta kamar kowa"
"In ce Alhamdulillah?" Amatullah ta tambaya
"Fadi kinji Aman Ummi"
Sai da ta gama murnarta ta kama hannun Amatullah suka fito. A falo ta barta ta karasa dakin Hajjo. Kafin ta shiga taji muryar Anti Bintu tana magana sama sama da ji kasan ranta a bace yake
"Yaya Bara wallahi Asmau tana son Ishaq. Don ta fada miki zata sallamesu duk su biyun kawaici ne kawai. Ita a tunaninta bata da wata kimar da namiji zai aureta. Don Allah kada ku shiga tsakaninsu. Hajjo kiyi mata magana "
Hajjo tace "Bintu nima ba wai naki Ishaq bane. Ki tuna wacece Asmau, tana da tabon da babu ruwan da zai wanke shi duk duniya. Qasim da iyayensa sun san komai game da ita kuma dazu muke ji ashe saboda ita yaki aure tuntuni wai kada kishiya tayi mata gori ko habaici"
Anti Bintu tace "to duk abinda yayi ai ba wai sunyi da ita zata aure shi bane. A yadda na kula da irin son da Ishaq yake mata ba zai hakura kai tsaye ba."
Umma kanta tasan wanda Asmau take so amma bazata iya yiwa Alh Adamu musu ba kamar yadda shima yaji nauyin Mal Musa. Idan ta biyewa Bintu jan zancen kawai za'ayi ta yi azo zumunci ya sami rauni.
"Bintu don Allah ki bar zancen nan. Komai ya kure tunda ranar lahadu zasu zo kawo kudi. Itama sai tayi hakuri ta karbi kaddara"
A fusace Anti Bintu ta mike "ni bazan zuba ido ina kallo a cuci yarinyar nan ba. Ba kwa tunanin kada *abinda ake gudu* ya sake faruwa? Don kaddara ta fada mata shikenan kuma bata da damar zabar wanda take so"
"Ba kya tunanin nan gaba matsala ta taso ko a kaina ko akan Amatullah"
"Hmmm Asmau kenan, ke kike da goben da har kike tunanin matsala? Yadda Allah Ya daidaita miki lamura yanzu, idan har wani abin ya taso a gaba Shi din dai zai mana magani. Kada ki manta nima ba 'yar aure bace amma Allah Ya hadani daku gashi babu wanda ya taba yi mim gori. Auren ma Hajjo ce ta hada. Zamana nake lafiya na manta da kazantar da na taso cikinta. Yadda na hadu daku da yardar Allah itama zata hadu da mutane nagari a rayuwarta"
Asmau ta sunkuyar da kanta kasa hawaye na taho mata. Duk matar da tayi zina ta gama cutar abinda ta haifa. Sai dai idan an hadu da mutane na kwarai. Kuma duk da haka haifewar itace tafi akan zubar da ciki wanda yake daidai da kisa idan an busawa jaririn rai. Mace sai ta sami rahmar Allah idan ta rungumi kaddararta ta bawa abinda ta haifa tarbiyar da ta dace da addininmu.
"Ki kara hakuri da rayuwa Asmau. Haka Allah Ya tsara miki. Ke kika zama ishara ga masu hankali wadanda idan sunji labarinki zasu san cewa biyewa sharrin yanar gizo da son zuciya halaka ne. Uwa uba babu wani alkhairi da yake tattare da shiga groups din nan na whatsapp ko facebook masu yada alfasha."
"Nagode Antina ta kaina. Allah Ya raba lafiya mu sha suna"
Dadi Zubaida taji da taga Asmau ta dan sake. Amatullah tana tsakar gida suna wasa da yaran Zubaidan.
"Tashi mu soya wainar fulawa"
Asmau ta zaro ido "yaushe muka gama cin abinci?"
Cikinta ta shafa "bani nake so ba kaninki ne ko kanwa"
"To kala masa sharri saboda bashi da baki. Ina fulawar take na hada?" Ta fada tana tashi.
Ranar dai sun wuni suna hira kuma taji dadin shawarar da Zubaida ta bata. Duniya kenan, Zubaida da ta tashi a matsayin 'yar magajiyar karuwai gashi Allah Ya sauya mata rayuwa. Sai bayan magariba Asmau tayi shirin tafiya. Dama Jafar yace zai dawo daukarta sai ya kira yace ayyuka sun masa yawa. Nan kuwa bata san suna can gidansu ana maganar aurenta bane.
Zubaida ta sake yi mata tuni akan lallai kada ta bari dama ta kubuce mata. Ta amince tayi aure
"Ni na kula sojan nan ba dai iya nuna kulawa ba. Zuwanki nan kunyi waya sau uku."
Murmushin Asmau ya tabbatar mata da zarginta na cewa shi take so. Har kofar gida ta rakata suka tafi titi suka shiga adaidaita sahu ita da Amatullah suka tafi gida..
Abin mamaki tana zuwa ta tarar da Anti Bintu tazo da yaranta wai zasuyi weekend. Tayi murna sosai. Amatullah ma ta ganesu saboda haka ta saki jiki ana hira. Umma tace idan ta huta tazo dakin Hajjo tana son ganinta. Anti Bintu Asmau ta kalla tana dan murmushi, ko dai ta fadawa Umma zuwan Jikamshi Zaria ne. Karshenta maganar aure ce. Ta riga ta kudiri niyar bin shawarar Zubaida. Zata tsananta addua ta amince da Col. I M Jikamshi.
*****
Ko kayanta bata cire ba da ta shiga daki Jikamshi ya kirata kamar yasan tunaninsa take yi a wannan lokacin.
Daukar wayar tayi tare da yin sallama.
Shima lokacin yana gida ya tasa laptop a gaba yana kallon wasu hotuna da ya dauki Amatullah. Yana son yarinyar nan, ko babu komai ta dauke shi uba sannan gashi tayi sanadiyar hadashi da Umminta. Safinansa akwai shiga rai.
Sallamar Asmau ce ta katse masa tunani ya amsa mata cikin daddadar muryarsa.
"Matar Jikamshi kun dawo gida lafiya?"
"Lafiya kalau"
"I miss you so much"
"Duk wayar da muke yi tun safe?"
Yayi yar dariya "yanzu ke hirar waya ta isheki. Ni nafi son na ganki a gabana. By the way lokacin da na baki fa yayi. Anyi sati daya ya kuka yi da Qasim?"
Shiru tayi domin kuwa bata sami biyan bukata ba. Tayi kokarin nuna masa ya hakura da zancen aure sai ya rinka danganta abin da ko tana gudun aurensa saboda tunanin Abubakar ne. Karshe yace mata ta jira nan da lahadi komai zai zo karshe.
Col Ishaq yace "ya kika yu shiru? Kada kice min bakiyi komai ba."
Sautin muryarsa kamar baiji dadi ba tace "ka kara hakuri yace na jira zuwa ranar lahadi idan yazo kamai zai zo karshe"
"Ban fahimceki ba, komai zaizo karshe kamar yaya?"
Asmau kanta bata gane abinda Qasim yake nufi ba "nima dai haka yace min"
Col. Ishaq ya tashi daga kashingidar da yayi "look Matar Jikamshi, ni mutum ne kaifi daya. Idan kina jin nauyin fada masa saboda kusancin families dinku ni zan fada masa da kaina. Tunda naga ya cigaba da yi min text da waya nasan bai san alakarmu ba. Kinga kashe wayar kawai bari na kira shi na fada masa Ishaq da Asmau suna son juna don Allah ka nemi wata"
Bata san lokacin da ta kwashe da dariya ba "yanzu don Allah sai ka fada masa haka"?
"Kin dauka wasa nake yi, yara ne suke da lokacin wasa da soyayya."
Tace "kayi hakuri zuwa lahadin please"
Yadda take magana duk ya kashe masa jiki. Zai iya hakuri amma zuwa sunday kawai. Daga nan kuwa to sai dai ayita ta kare. Shi ba don yana ganin mutuncin Qasim din ba tun ranar da ya gansu da Asmau da a lokacin zai fada masa.
"Yarinya dake duk kin rikita min lissafi. Amma zan rama ne, sai kin shigo gidanki"
"Nima fa ka rikita min"
"Me kika ce?"
Zancen zuci ne ya fito fili tayi saurin toshe bakinta. Ta rasa inda zata sa kanta don kunya. Tana ji yana mata dariya don yasan bata so yaji abinda ta fada ba.
"I love you Matar Jikamshi. Nasan bazan kara samun nutsuwa ba idan ba aurenki nayi ba. Na riga na fadawa Hajiya amsarki nake jira a fadawa iyayena maza. Idan kika zabi Qasim zan tayar da yaki a zuciyarki"
Wani dadi ne taji yana ratsata. Ashe tana da rabon samun farinciki a rayuwarta. Ita ma tana son shi kuma ta shiryawa duk wani nau'i na gori da zai iya zuwa daga danginsa. Abinda ake gudu ya riga ya faru sai dai a kiyayi gaba.
" 'yarka da Yassar ma bazasu barni ba idan na zabi wani ba kai ba. Da ka tashi sai ka hada da zuciyata data Amatullah kuma harda ta kanina."
Da tasan irin yadda yake ji a ransa da ta rage yi masa magana ko don ta sassauta masa. Ajiyar zuciya yayi har tana jin sautin
"Say you love me please" ya fada cikin sanyin murya.
Yau daya zata sakaya kunyarta ta farantawa mai faranta mata "I do love you _Jikamshina_"
Kafin ya kara magana ta kashe wayar gabadaya don tasan zai sake kira. Kwanciya tayi akan gado tana juyi ita kadai zuciyarta kamar an wanke mata.
Shi kuwa rike yake da wayar a hannu yana murmushi. Hmmm bari dai ace an daura musu aure. Ranar Asmau zata san tana da masoyi. Zaiyi iya kokarinsa wurin nuna mata soyayya da cewar itama har yanzu tana da darajarta a cikin mata. Abinda ya wuce a baya sai ayi ta addua da fatan Allah Ya yafewa musulmi kurakuransu.
*****
Tana ta maimaita hirarsu a kwakwalwarta tana dariya Amatullah ta shigo
"Ummina Umma tana kiyanki"
Ai da sauri ta sauko daga kan gadon. Shaf ta manta Umma tace tana son ganinta.
Saurin da take yi yasa Amatullah tace "Ummi guduwa zamuyi ne? Me nene akan gadon?"
Asmau tayiwa kanta dariya sannan ta dauki Amatullah tana juyi da ita. Soyayyar Jikamshi ta zame mata wani bangare mai mahimmanci a rayuwarta. Tana juyin tana dariya.
Amatullah tana tayata duk da bata san dalilin murnar Ummin ta ba
"Ummi abin dadi ne ya fayu?"
"Shine zai faru in sha Allah Ama, muma Allah zai bamu rayuwa mai tsafta kamar kowa"
"In ce Alhamdulillah?" Amatullah ta tambaya
"Fadi kinji Aman Ummi"
Sai da ta gama murnarta ta kama hannun Amatullah suka fito. A falo ta barta ta karasa dakin Hajjo. Kafin ta shiga taji muryar Anti Bintu tana magana sama sama da ji kasan ranta a bace yake
"Yaya Bara wallahi Asmau tana son Ishaq. Don ta fada miki zata sallamesu duk su biyun kawaici ne kawai. Ita a tunaninta bata da wata kimar da namiji zai aureta. Don Allah kada ku shiga tsakaninsu. Hajjo kiyi mata magana "
Hajjo tace "Bintu nima ba wai naki Ishaq bane. Ki tuna wacece Asmau, tana da tabon da babu ruwan da zai wanke shi duk duniya. Qasim da iyayensa sun san komai game da ita kuma dazu muke ji ashe saboda ita yaki aure tuntuni wai kada kishiya tayi mata gori ko habaici"
Anti Bintu tace "to duk abinda yayi ai ba wai sunyi da ita zata aure shi bane. A yadda na kula da irin son da Ishaq yake mata ba zai hakura kai tsaye ba."
Umma kanta tasan wanda Asmau take so amma bazata iya yiwa Alh Adamu musu ba kamar yadda shima yaji nauyin Mal Musa. Idan ta biyewa Bintu jan zancen kawai za'ayi ta yi azo zumunci ya sami rauni.
"Bintu don Allah ki bar zancen nan. Komai ya kure tunda ranar lahadu zasu zo kawo kudi. Itama sai tayi hakuri ta karbi kaddara"
A fusace Anti Bintu ta mike "ni bazan zuba ido ina kallo a cuci yarinyar nan ba. Ba kwa tunanin kada *abinda ake gudu* ya sake faruwa? Don kaddara ta fada mata shikenan kuma bata da damar zabar wanda take so"