Sashe 62
Abinda Ake Gudu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ya Salaam, bata kara magana ba ta kashe wayar ta fita neman pillow tana dariya. Haka ta dawo ta kwanta don bata samu ba. Shima dariyar kunyar da yasan taji ya gama ya gyara kwanciya yana tuno dan lokacinsu na dazu zuciyarsa na kara nutsuwa da zabin da Allah Yayi masa.
*****
Da safe sai da suka yi breakfast kowa ya shirya aka fara komawa gidan Umma wurin yini. Yau atampa ta saka anyi mata dinkin half-gown da plain zani. Ta kashe dauri ta yafa mayafi irin na kayan. Da ta fito falo guda aka saka amarya da farinjini.
Kujeru aka jera a waje da tabarmi da kafet. Sai ga Ado Gwanja ya iso da tawagarsa. Wannan aikin Sally ne 'yar Yaya Abu da Ab Kura kamar yadda suka saba kiran babbar 'yar Anti Lami. Sun dage sai sun gwangwaje suma a bikin nan. Tun kafin dawowar Asmau zumuncin 'yan uwan ya karu bayan tafiyar Kawu Rabe. 'Yan mata kuwa da su Shemau aka shiga filin rawa. Amarya dai sai janta akeyi amma ko da can bata iya sakin jiki tayi rawa balle yanzu da tun jiya Jikamshinta ya rada mata baya son rawar nan. Idan zatayi ta jira sai su kadai.
Ana ciye ciye biki na ta tafiya aka kira Sabira a waya sai ta fita da gudu tana murna. Anti Bintu tace "ke lafiyarki kuwa"
Sauri take ta karasa waje ta taro bakin tace "Anti Bintu 'ya'yan yayyen Mama ne daga Maiduguri. Mota ce tayi musu tsiya tun shekaranjiya suka so zuwa."
Ta fita ta taro 'yan uwanta tazo ta gabatar dasu wurin amarya Asmau.
"Wannan sunanta Fatima Goni ga kuma Amalus sai Halima Wasagu da Feey. Cousins dina da nace miki suna son zuwa biki"
Asmau fuska a sake ta gaisa dasu tana godiya da suka sami damar zuwa. Daga nan aka cigaba da taro har yamma.
Sai da magariba ta gabato aka sallami mai waka iyaye suka kira Asmau cikin dakin Hajjo. Jikinta ya gama sanyi ta shiga dakin suna zazzaune. Hajjo ce a tsakiya ga Mama Yalwa, Umma, Anti Bintu, Yaya Abu da Anti Lami don kara irin tasu harda Yaya Tagwai da Uwargida basu nuna mata kyama ba.
Nasiha ce suke mata wadda tasa ta kuka kamar an bude famfo. Hakuri ne kowacce take mata nuni dashi domin shine jigo a zaman aure duk son da kuke yiwa juna da miji to sai an kai zuciya nesa. Zama ne ake fatan yi har karshen rayuwa. Suka dora mata da ta jure ta kawar da kai ga dukkan maganar da zata ji musamman daga dangin miji. Haka Allah Ya kaddara mata dole ne kuma sai an sami masu yi mata wannan gorin. Hakuri, ladabi, biyayya, tsafta da iya girki kuma sai ta dage. Ishaq yayi mata karamci da yake sonta a haka ya aureta. Ta zage damtse ta kyautata masa.
Kowa ya fadi nasa Asmau tayi kukanta son rai. Bayan ta fita daga dakin ba jimawa Zubaida tazo ta kirata dakin Yassar. Abin mamaki Uwargida ce a dakin Zubaida ta rufe kofar. Sake bawa Asmau hakuri tayi da taso bata mata rayuwa
"idan naje muka gana da 'yan uwana zan koma Azare ne. Gidan nan ba zan barshi a cigaba da sabon Allah ba. Da kika ganni babana Limami ne. Da kuruciya muke sauka. Ina da ilimi na daidai gwargwado. Zanyi amfani dashi wurin bawa matan dake gidan shawara da koyar dasu sannan su koma gaban iyayensu. Ba ido gareni ba kada ayi abinda bazan gani ba. Za'a raya gidan da bautar Allah in sha Allah"
Asmau taji dadi sosai haka ma Zubaida. Uwargida tace "Asmau ina so ku saurareni da kyau. Nasan sana'ata ba mai kyau bace kuma ina ta rokon Allah gafara. Amma ina son sanar daku wasu 'yan sirrikan rike miji da muke amfani dasu a da muna raba mata da mazansu muna aikata haram. Wannan abin idan kunyi a gidan miji riba zaku samu da lada. Ku zama marasa kunya amma ba tsiwa da fitsara ba. Duk abinda miji yake so kiyi masa kada yaje nema a waje. Wani kinkime jiki da hijabi a dakin miji sai a sallah ko kunyi baki. Ku zauna da kayan da zasu ganku da kyau suji suna sha'awarku."
Zubaida da Asmau sai kunya aka fara sunkuyar da kai. Uwargida da taji sunyi shiru tace "kunga ni babarku ce. A bariki nayi amfani da wannan banga riba ba saboda aikin haramci ne. Amma ku gwada a gidan aure wallahi miji sai ya yaba muku. Da ajiye kunya mu kyautata musu muke raba auren soyayya. Matan hausawa kamar munfi kowa kunya. Muyi a waje sannan a gidan auren ma miji yana binki kina nokewa wai ke kin girma. Ai kullum ku nuna musu kamar yau kuka fara kasancewa tare. Sunayen soyayya na zamani samo ki kira abinki. Wani maigida ko baban wane an wuce wurin. Idan miji bai zo da kansa ba ke ki nemo shi. Hanyoyi gasu nan barkatai. Ku dan matso kada aji daga waje ace Uwargida zata bata ku. Allah Ya gani sharrin irinmu nake guje muku. "
Ai kuwa su Asmau sunji batu a bakin Uwargida. To dama kunya a wurin irinsu sai a hankali. Baro zance kawai take Zubaida ta gama jin kunya. Ko da ta gama bayani sai dai su kalli juna suyi murmushi.
*****
Wanka Asmau tayi saboda ance masu daukar amarya suna hanya. Amatullah kamar tasan ba da ita za'a tafi ba yau ta like mata. Da kyar da dabara Shemau ta hadata da yaranta tasa Yassar yayi saurin kai mata su gidanta. Nan da sati biyu sai a dawo da ita lokacin itama Asmau ta saba. Ana fita da ita kuwa Asmau tasa kuka. An rabata da Ama ji take gara kawai a bata ita su tafi tare. Da kyar tayi shiru ta shirya cikin wani material mara nauyi riga da skirt. Fuska tasha kwalliya sosai ga katon mayafi har ka ta lulluba. Jammu cikin kawayen Shemau ita ta matso kusa da Asmau ta damka mata wani abu kamar zuma kadan a kofi. Asmau ta dan dago kai ta kalleta.
"Nasan kin sha abubuwa da yawa shiyasa na zuba miki kadan. Kinsan yadda muke da Shemau kanwa na daukeki. Na bata sauran za'a ajiye a gidanki."
Wannan kayan idan batayi da gaske ba cikinta sai ya baci. Kowa da nasa kuma duk abu daya ne. Suna son daga darajarta a wurin miji. Kafa kai tayi ta shanye tsumin. Jammu tayi dan murmushin jindadi. Tasan nan gaba Asmau sai ta nemeta da kanta. Sirrinsu ne na Sokoto.
******
Dirar motoci aka ji wanda yayi daidai da faduwar gaban Asmau. Shikenan ta zama matar aure. Auren da ta fitar da rai ashe tana da rabonsa. Gashi zata bar Umma ta kama rayuwar ibada.
Su Mami ne suka zo daukar amarya da wasu 'yan uwansu manya. Da aka tashi fita da kyar aka bambare Asmau daga jikin Umma, ita ma Umma kukan take. Su Anti Bintu ma da Mama Yalwa sunyi nasu kukan. Motoci sunfi goma daga bangaren ango banda na dangin amarya masu motar gida da ta haya. Mata ne kawai suka cika gidan. Biki yayi albarka. Mutan Jikamshi sun dauki amaryarsu Asmau.
A motarsu daga wanda yake ja wani soja ne abokin aikin Col. Ishaq sai Walida a gaba. A baya kuma Yaya Abu ce da Mama Yalwa suka saka Asmau a tsakiya.
Gida ne flat mai kyau tun daga waje ga filawoyi sun fito ta saman katanga. Gate din a bude yake da yake bazai dauki motoci sama da uku ba dole aka bar wurin da za'a shigo da motar amarya. Tun a nan zaka san anzo gidan amarya saboda kamshin dake tasowa daga ciki. Wannan aikin su Shemau, ne da Rashida, Sabira da Suwaiba. Mata sai son barka ake gida yayi kyau sosai. A cikin falon aka kai Asmau wurin wasu mata iyaye ga Col. Ishaq ta bangaren Hajiya da babansu. Anyi barkwanci suka kare da nasiha. Babu mai iya tanka Asmau domin sun sha gargadi a wajen iyaye maza. Col. Ishaq yana da kwarjini basa son bata masa, ihsani ya sami tangarda.
Daga nan aka wuce da ita dakinta wanda Umma tayi namijin kokari wurin sayan kayan kawata shi. kanta a rufe yake tana hawaye har aka zaunar da ita a bakin gado. Wata da tace gidanta na jikin na Asmau mai suna Husna tazo ta dan bude fuskar amarya tana murmushi
"Masha Allah amarya Allah Ya bada zaman lafiya. Idan kina da matsala ki rinka nemana. In kina so ma ni kullum sai na shigo na taimaka miki."
Ainau dake gefe tayi dariya, Husna baki san wannan angon ba.
Sai da aka hada da magiya aka samu matan suka fara fita. Gidan ba babba bane sosai. Daidai mata da miji da 'ya'yansu. Gida ya watse sai makusantan Asmau. Har lokacin bata bude fuskarta ba.
Walida tace "kinga ki tashi kiyi sallar isha in da hali kiyi wanka ki canza kaya. Kinsan saboda mutane dakin yayi zafi gaki a kunshe cikin mayafi"
"Nima abinda zan fada mata kenan. An taho da kayanki sai ki sami 'yar rigar bacci mai kyau ki saka"
Asmau bata san lokacin da ta bude lullubin tana kallon Zulaiha ba harda harara. Dariya suke mata sosai Zulaiha tace "meye na hararata, ki tashi ko na tonaki wallahi"
Zubaida tace "don Allah tona" sauran suka rinka naci ita kuma Zulaiha tana ta ja musu rai. Da yake yau bakin yayi lakwas Asmau bata ce komai ba ta shiga inda aka nuna mata bandakin dake cikin dakinta. Sai hamdala take, ko a toilet ba karamin kashe kudi aka yi ba. Duk kayan toilet Abdulhalim ne yayi mata su. Wanka tayi da alwala ta mayar da rigarta akan tawul din. Tana fitowa duk an ragu sai yayarta Shemau. Za'ayi sirri na 'yan uwa ta nuna mata inda ta ajiye kayan gyaran da aka bata a wata drawer
"Don Allah kada ki rinka yi musu shan koshi. Komai sama sama yafi ko don kada ki sha wanda zai illata ki. Ga wannan kuma ki saka"
*****
Da safe sai da suka yi breakfast kowa ya shirya aka fara komawa gidan Umma wurin yini. Yau atampa ta saka anyi mata dinkin half-gown da plain zani. Ta kashe dauri ta yafa mayafi irin na kayan. Da ta fito falo guda aka saka amarya da farinjini.
Kujeru aka jera a waje da tabarmi da kafet. Sai ga Ado Gwanja ya iso da tawagarsa. Wannan aikin Sally ne 'yar Yaya Abu da Ab Kura kamar yadda suka saba kiran babbar 'yar Anti Lami. Sun dage sai sun gwangwaje suma a bikin nan. Tun kafin dawowar Asmau zumuncin 'yan uwan ya karu bayan tafiyar Kawu Rabe. 'Yan mata kuwa da su Shemau aka shiga filin rawa. Amarya dai sai janta akeyi amma ko da can bata iya sakin jiki tayi rawa balle yanzu da tun jiya Jikamshinta ya rada mata baya son rawar nan. Idan zatayi ta jira sai su kadai.
Ana ciye ciye biki na ta tafiya aka kira Sabira a waya sai ta fita da gudu tana murna. Anti Bintu tace "ke lafiyarki kuwa"
Sauri take ta karasa waje ta taro bakin tace "Anti Bintu 'ya'yan yayyen Mama ne daga Maiduguri. Mota ce tayi musu tsiya tun shekaranjiya suka so zuwa."
Ta fita ta taro 'yan uwanta tazo ta gabatar dasu wurin amarya Asmau.
"Wannan sunanta Fatima Goni ga kuma Amalus sai Halima Wasagu da Feey. Cousins dina da nace miki suna son zuwa biki"
Asmau fuska a sake ta gaisa dasu tana godiya da suka sami damar zuwa. Daga nan aka cigaba da taro har yamma.
Sai da magariba ta gabato aka sallami mai waka iyaye suka kira Asmau cikin dakin Hajjo. Jikinta ya gama sanyi ta shiga dakin suna zazzaune. Hajjo ce a tsakiya ga Mama Yalwa, Umma, Anti Bintu, Yaya Abu da Anti Lami don kara irin tasu harda Yaya Tagwai da Uwargida basu nuna mata kyama ba.
Nasiha ce suke mata wadda tasa ta kuka kamar an bude famfo. Hakuri ne kowacce take mata nuni dashi domin shine jigo a zaman aure duk son da kuke yiwa juna da miji to sai an kai zuciya nesa. Zama ne ake fatan yi har karshen rayuwa. Suka dora mata da ta jure ta kawar da kai ga dukkan maganar da zata ji musamman daga dangin miji. Haka Allah Ya kaddara mata dole ne kuma sai an sami masu yi mata wannan gorin. Hakuri, ladabi, biyayya, tsafta da iya girki kuma sai ta dage. Ishaq yayi mata karamci da yake sonta a haka ya aureta. Ta zage damtse ta kyautata masa.
Kowa ya fadi nasa Asmau tayi kukanta son rai. Bayan ta fita daga dakin ba jimawa Zubaida tazo ta kirata dakin Yassar. Abin mamaki Uwargida ce a dakin Zubaida ta rufe kofar. Sake bawa Asmau hakuri tayi da taso bata mata rayuwa
"idan naje muka gana da 'yan uwana zan koma Azare ne. Gidan nan ba zan barshi a cigaba da sabon Allah ba. Da kika ganni babana Limami ne. Da kuruciya muke sauka. Ina da ilimi na daidai gwargwado. Zanyi amfani dashi wurin bawa matan dake gidan shawara da koyar dasu sannan su koma gaban iyayensu. Ba ido gareni ba kada ayi abinda bazan gani ba. Za'a raya gidan da bautar Allah in sha Allah"
Asmau taji dadi sosai haka ma Zubaida. Uwargida tace "Asmau ina so ku saurareni da kyau. Nasan sana'ata ba mai kyau bace kuma ina ta rokon Allah gafara. Amma ina son sanar daku wasu 'yan sirrikan rike miji da muke amfani dasu a da muna raba mata da mazansu muna aikata haram. Wannan abin idan kunyi a gidan miji riba zaku samu da lada. Ku zama marasa kunya amma ba tsiwa da fitsara ba. Duk abinda miji yake so kiyi masa kada yaje nema a waje. Wani kinkime jiki da hijabi a dakin miji sai a sallah ko kunyi baki. Ku zauna da kayan da zasu ganku da kyau suji suna sha'awarku."
Zubaida da Asmau sai kunya aka fara sunkuyar da kai. Uwargida da taji sunyi shiru tace "kunga ni babarku ce. A bariki nayi amfani da wannan banga riba ba saboda aikin haramci ne. Amma ku gwada a gidan aure wallahi miji sai ya yaba muku. Da ajiye kunya mu kyautata musu muke raba auren soyayya. Matan hausawa kamar munfi kowa kunya. Muyi a waje sannan a gidan auren ma miji yana binki kina nokewa wai ke kin girma. Ai kullum ku nuna musu kamar yau kuka fara kasancewa tare. Sunayen soyayya na zamani samo ki kira abinki. Wani maigida ko baban wane an wuce wurin. Idan miji bai zo da kansa ba ke ki nemo shi. Hanyoyi gasu nan barkatai. Ku dan matso kada aji daga waje ace Uwargida zata bata ku. Allah Ya gani sharrin irinmu nake guje muku. "
Ai kuwa su Asmau sunji batu a bakin Uwargida. To dama kunya a wurin irinsu sai a hankali. Baro zance kawai take Zubaida ta gama jin kunya. Ko da ta gama bayani sai dai su kalli juna suyi murmushi.
*****
Wanka Asmau tayi saboda ance masu daukar amarya suna hanya. Amatullah kamar tasan ba da ita za'a tafi ba yau ta like mata. Da kyar da dabara Shemau ta hadata da yaranta tasa Yassar yayi saurin kai mata su gidanta. Nan da sati biyu sai a dawo da ita lokacin itama Asmau ta saba. Ana fita da ita kuwa Asmau tasa kuka. An rabata da Ama ji take gara kawai a bata ita su tafi tare. Da kyar tayi shiru ta shirya cikin wani material mara nauyi riga da skirt. Fuska tasha kwalliya sosai ga katon mayafi har ka ta lulluba. Jammu cikin kawayen Shemau ita ta matso kusa da Asmau ta damka mata wani abu kamar zuma kadan a kofi. Asmau ta dan dago kai ta kalleta.
"Nasan kin sha abubuwa da yawa shiyasa na zuba miki kadan. Kinsan yadda muke da Shemau kanwa na daukeki. Na bata sauran za'a ajiye a gidanki."
Wannan kayan idan batayi da gaske ba cikinta sai ya baci. Kowa da nasa kuma duk abu daya ne. Suna son daga darajarta a wurin miji. Kafa kai tayi ta shanye tsumin. Jammu tayi dan murmushin jindadi. Tasan nan gaba Asmau sai ta nemeta da kanta. Sirrinsu ne na Sokoto.
******
Dirar motoci aka ji wanda yayi daidai da faduwar gaban Asmau. Shikenan ta zama matar aure. Auren da ta fitar da rai ashe tana da rabonsa. Gashi zata bar Umma ta kama rayuwar ibada.
Su Mami ne suka zo daukar amarya da wasu 'yan uwansu manya. Da aka tashi fita da kyar aka bambare Asmau daga jikin Umma, ita ma Umma kukan take. Su Anti Bintu ma da Mama Yalwa sunyi nasu kukan. Motoci sunfi goma daga bangaren ango banda na dangin amarya masu motar gida da ta haya. Mata ne kawai suka cika gidan. Biki yayi albarka. Mutan Jikamshi sun dauki amaryarsu Asmau.
A motarsu daga wanda yake ja wani soja ne abokin aikin Col. Ishaq sai Walida a gaba. A baya kuma Yaya Abu ce da Mama Yalwa suka saka Asmau a tsakiya.
Gida ne flat mai kyau tun daga waje ga filawoyi sun fito ta saman katanga. Gate din a bude yake da yake bazai dauki motoci sama da uku ba dole aka bar wurin da za'a shigo da motar amarya. Tun a nan zaka san anzo gidan amarya saboda kamshin dake tasowa daga ciki. Wannan aikin su Shemau, ne da Rashida, Sabira da Suwaiba. Mata sai son barka ake gida yayi kyau sosai. A cikin falon aka kai Asmau wurin wasu mata iyaye ga Col. Ishaq ta bangaren Hajiya da babansu. Anyi barkwanci suka kare da nasiha. Babu mai iya tanka Asmau domin sun sha gargadi a wajen iyaye maza. Col. Ishaq yana da kwarjini basa son bata masa, ihsani ya sami tangarda.
Daga nan aka wuce da ita dakinta wanda Umma tayi namijin kokari wurin sayan kayan kawata shi. kanta a rufe yake tana hawaye har aka zaunar da ita a bakin gado. Wata da tace gidanta na jikin na Asmau mai suna Husna tazo ta dan bude fuskar amarya tana murmushi
"Masha Allah amarya Allah Ya bada zaman lafiya. Idan kina da matsala ki rinka nemana. In kina so ma ni kullum sai na shigo na taimaka miki."
Ainau dake gefe tayi dariya, Husna baki san wannan angon ba.
Sai da aka hada da magiya aka samu matan suka fara fita. Gidan ba babba bane sosai. Daidai mata da miji da 'ya'yansu. Gida ya watse sai makusantan Asmau. Har lokacin bata bude fuskarta ba.
Walida tace "kinga ki tashi kiyi sallar isha in da hali kiyi wanka ki canza kaya. Kinsan saboda mutane dakin yayi zafi gaki a kunshe cikin mayafi"
"Nima abinda zan fada mata kenan. An taho da kayanki sai ki sami 'yar rigar bacci mai kyau ki saka"
Asmau bata san lokacin da ta bude lullubin tana kallon Zulaiha ba harda harara. Dariya suke mata sosai Zulaiha tace "meye na hararata, ki tashi ko na tonaki wallahi"
Zubaida tace "don Allah tona" sauran suka rinka naci ita kuma Zulaiha tana ta ja musu rai. Da yake yau bakin yayi lakwas Asmau bata ce komai ba ta shiga inda aka nuna mata bandakin dake cikin dakinta. Sai hamdala take, ko a toilet ba karamin kashe kudi aka yi ba. Duk kayan toilet Abdulhalim ne yayi mata su. Wanka tayi da alwala ta mayar da rigarta akan tawul din. Tana fitowa duk an ragu sai yayarta Shemau. Za'ayi sirri na 'yan uwa ta nuna mata inda ta ajiye kayan gyaran da aka bata a wata drawer
"Don Allah kada ki rinka yi musu shan koshi. Komai sama sama yafi ko don kada ki sha wanda zai illata ki. Ga wannan kuma ki saka"