Sashe 7
Mumnunar Dabia Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cikin yaranta babbar yarta Shema'u ta zama me kudi sabo da karuwanci,ita kanta kanwar mamanki da sauran yaranta sun zama masu kudi sun koma lagos da zama a nan suke rayuwa ba ruwan su da sa ido na hausawa da dangi,kece anyi anyi a fara koya miki kema ki fara kinki yarda,shine ta maida ki yar aikinta wanda yar aiki ma ta fiki daraja a wajen su,azaba suke gana miki,yanzu ma aikenki tayi kauyen ku kika kai sako shine zaki koma,sannan shekarunki ashirin da biyar 25, sannan abinda yasa suke so kema ki fara sabo da kina da kyau matuka gaki da diri me kyau komai naki yayi,duk wani namiji zai so ace ya mallake ki.
Kina son white color,kina son sakwara da miyar egusi,kina son wankan shadda,sannan period 4days kike yi....kuma....Islaha taji tonon sililin yayi yawa komai ya fada ba karya a ciki,ta dakatar da shi tace naji to,yace sannan kin gama secondary kin shiga NCE sai suka daina biya miki dole kika hakura da karatu.
Mukus tayi duk abinda ya fada ba karya ciki,abincin ta mika masa tace na koshi,lokacin ya karba ya fara cin abinsa,ido Islaha ta tsura masa tana kallonsa kamar mayya,na miki kyau ne? ta tsinci muryarsa ya furta ba tare da ya kalle ta ba,da sauri ta dauke kanta ta fara wasa da yatsunta tana yarfe hannu,dariya yayi ba shiri tare da kamo hannunta yace mu gani ciwo yake,a hankali cike da kunya ta zame hannunta,tambaya ya jefo mata ke baki da kayan wasa ne muyi wasa? Cike da mamaki tace wanne irin wasa? A gidan ku ba a siya miki doll Baby su Teddy,murmushi tayi tace da girman nawa? baki ya turo,jajayen lips dinsa suka birge ta,kanta ta sadda kasa sabo da kunya,sun dade a haka kafin mutanen motar su dawo suka ci gaba da tafiya abin su.
Sai washe gari da safe suka isa lagos,Islaha bayan sun sauka,ta tambayi Sahil ina zaka kai? yace gari mana ya juya dauke da jakarsa yayi tafiyarsa ko waigowa bai sake yi ba,baki ta tabe tayi tafiyarta itama.
Gidansu ta nufa a taxi tana zuwa Kanwar Mamanta da suke kira da Aunty ta ga ta shigo da safe,ranta a bace tace uban me kika tsaya yi Islaha baki dawo da wuri ba,aikin gidan nan uban wa zai miki? Islaha cikin tsoro tace kiyi hakuri kin san motar da kika ce na shiga bata da sauri ga tsaye tsaye shi yasa,ke dalla rufe mana baki cewar Khairat yar Aunty ta cikinta,a kalla zata kai 30yrs,kanwarta Khalisat ce tace wannan fa sam bata da saiti,Islaha tayi shuru dai ita,Aunty tace ai kuwa ga aiki nan ya taru sai ki fara,a gajiye Islaha take amma haka ta fara aikin gidan.
Gidane me kyau cikin estate duk gidajen layin iri daya ne,gidan yana da kyau a me rufin asiri dai a lagos duk da unguwar ta masu karamin karfi ce amma tayi kyau,Islaha sai da ta gyara gidan tsaf ta gama komai tazo ta dora girkin dare,Khairat tace wankin namu fa sai yaushe? Zanyi gobe inshaallah,da sauran rana a gari madam ki wanke mana kaya,Khalisat ce ta kawo mata kaya ta jibge,Islaha haka tana girki tana wankin sai da ta gama tas,Allah yasa ma kayan ba dirty,sai da ta gama komai sannan ta samu tayi wanka ta canja kaya cikin riga da wandonta yan gwanjo amma sun mata kyau sosai abinka da me kyau,abincin ta ebo taci ta koshi,tana palo Yaseer ya shigo babban dan gidan Aunty,Aunty tace Yaseer bana son wannan yarinya r da kace zaka aura Rukayya take ko,Yaseer ya kalli Mahaifiyar su ya furta amma kin san an sa rana fa!
Aunty tace ai baza ka aure ta ba gaskiya na tambayi malamai na sunce sam ba Alkhairi a auren ku sannan indai ka aureta sunce kai da arziki sai dai kaga ana yi,nasan tun tana karama kuke soyayya hasalima ta samu mazajen aure amma ta makale sai kai ta dinga jiranka tun bamu da kudi gashi muna da rufin asiri amma baza ka aure ta ba,malamai sunce babu alkhairi.
Islaha tana jinsu tace amma ai ba wanda ya isa ya hana wani arziki a duniya,Allah shike bayarwa shike hanawa,Aunty rankwashi ta zubawa Islaha tace wlh idan ina magana kina sa min baki sai naci ubanki, shuru Islaha tayi tana jinsu har Yaseer dinma katon jahili ya yarda da abinda uwarsa ta furta,yace to Aunty ai kuwa sai dai kije wajen Malamai a cirewa Rukayya so na a ranta,idan ba haka ba ta ya zan iya cewa na fasa? karka damu wannan me sauki ne za a sa taji bata sonka da kanta tace ta fasa,ya furta to shike nan tunda ba alkhairi me zanyi da ita yanda nake so nayi kudi ido rufe.
Sahil machine ya hau yace kasuwar 'yan tumatir zaka kaini,me machine kuwa ya kaishi babbar kasuwar tumatir dake Lagos,hausawa da yare ne damkam ana ta hada hada,Sahil ya tsaya rataye da jakarsa yana kallon abinda akeyi,gashi su baza su iya aikin karfi ba,wani ne a ciki ya kalli Sahil ya ganshi ya dade a tsaye,ya zaci wani shahararren me kudi ne yazo daga kasar waje zai siyi tumatir,da sauri ya karaso gabansa yace
Good day sir, Hausa Sahil yayi yace sannu da aiki,ashe kana jin hausa ai na zaci daga Tunisia ka sauka,Sahil yace no,okay kaya zaka siya ne? Mota nawa kake so?
Sahil ya kalle shi yace aiki nazo nema ni dan gidan malam shehu ne,mutumin ya kalli Sahil sama da kasa yace aiki? Irin wanda muke yi na karfi na sauke tumatir daga mota?
Sahil ya amsa da ae mana shi,ai gidanmu ma sabo da bani da kudi idan aka ga hadari ya taso har danyar daddawa ake kaimin dakina na kwana sabo da kasan life no balance at all,yanzu idan baka da shi a gidanku sai uwarka ta mutu baka sani ba.
Wanda suke magana me suna Aminu dariya ya dinga yi yace gaye kamarka sabo da talauci sai a kai daddawa dakinka na kwana?
Sahil yace sai dai in hadari bai taso ba amma yana tasowa za a kawota a faranti.
Mutumin yace au baka da ko sisi a haka?kalli fa kayan jikinka sai me kudi ke sa irinsu"
Sahil ya furta ae nema dai zanyi,dariya mutumin yayi sosai yace kalli kalarka fa zaka iya kuwa? Zan iya mana,mutumin yace sunana Aminu to kaifa? Sahil nake,yace indai aikin wahala ne baya wahala zaka samu,ka sauke duk kwando daya 50 Naira.
Sahil yace zanyi haka,Sahil suna da karfi wanda bana mutane ba ma amma na aikin banza da anzo wanda mutum zai amfani kansa da shi sai lalaci yazo ya lullube su karfin bazai zo ba sam,haka ya ajiye jakarsa ya ratsa ta cikin kwandunan tumatir,Aminu yace waccen motar zamu je,suna karasawa Sahil ya shige cikin katuwar trailer a dole ya fito neman kudi,kwandon tumatir ya duka zai daga amma yayi yayi amma ya kasa,matasa dake wajen suka dinga ihu da dariya.
Sahil zuciya ya sake yi ya yunkura zai dauka amma yin duniya ya kasa yana matsawa kansa ma sai ya fada saman sauran kwandunan,mutane wannan ya ja hankalinsu aka taru ana kallonsa yana ta faman nishi da haki,mutane suna ta tunanin hutu ne ya masa yawa kawai duba da kalar jikinsa ana gani an san ajebo ne,masifa suka fara masa ya sakko musu daga mota,haka ya sakko kawai jikinsa a sanyaye.
Wajen masu abinci ya nufa sabo da tun a mota bai ci komai ba,ya samu ya siyi jullof din shinkafa da yankan namansa biyu ya zauna yaci ya sha pure water sannan ya mike ya mike ya koma cikin kasuwar.
Aminu ya kira ya tambaye shi dan Allah a ina kuke kwana? Aminu yayi dariya tare da nuna masa wasu dakuna na langa langa yace kaga wannan dakunan a haka duk shekara kasan nawa muke hadawa muna biya? Sahil ya tambaya nawa? Yace dubu dari biyu kalli dai dakine kamar container,a haka ma munfi mu ashirin a ciki wani kusan a kan wani yake kwana,sannan ka jira kaga wasu a inda suke kwana.
Sahil yayi mamaki ya koma gefe ya zauna,ga hadari ya hado sosai,yana zaune aka fara yayyafi sai yaga duk wasu suna saka rigar ruwa ga dare yayi wasu a cikin kurar ruwa da suke turawa ta eban kaya a ciki yaga sun saka kwali sun kwanta,wasu yan achaba a saman machinan su suka hau da rigar ruwa suka kwanta ruwa na dukan su,abin babu kyan gani yanda wasu a hausawan mu da gatansu da komai amma suke tafiya suna zubarwa da arewa mutunci,baza ka taba ganin yare a haka a wulakance a arewa ba da sunan neman kudi amma yan arewa duk inda kaskanci yake suna can,kana magana ace neman kudi ne,neman kudi sai mutum ya jefa rayuwarsa a hadari bayana a arewa ma wani yana da jarin da yafi zamansa a can.
Sahil dare yayi yana wata yar runfa a tsaye ya fake ga mutane sunyi yawa,wasu yan shaye shaye ne suka zo da gudu suka hankado Sahil cikin ruwan suka tsaya a rumfar babu inda Sahil zai fake gashi dare yayi ga ruwa ana tsinkawa kamar da bakin kwarya,waige waige ya fara cikin ruwan amma ba inda zai shiga,gani yayi babu amfanin tsaiwarsa kawai yabi ta cikin ruwan yana tafiya wanda bai san inda ya dosa ba,ruwa na dukansa yana ji wayarsa tana ringing yasan Sohail ne ke kiransa yaji ya sauka lafiya ba damar daga waya.
Yana ta tafiya cikin ruwan har ya bar layin ya shiga wani layin me kyau wanda bai san a ina yake ba,dai dai wani katafaren hotel yazo zai dan fake a jikin katangarsu, cikin tsararen hotel din ya kalla ya samu ya rakube ya fake a jikin wajen ya tsuguna! a haka yayi baccinsa har rana ta fito bai sani ba,karar mota ce tasa ya bude idonsa,kafafunsa har kumbura suka yi sosai,da kyar ya iya mikewa tsaye ya sake kallon cikin hotel din kenan
Kina son white color,kina son sakwara da miyar egusi,kina son wankan shadda,sannan period 4days kike yi....kuma....Islaha taji tonon sililin yayi yawa komai ya fada ba karya a ciki,ta dakatar da shi tace naji to,yace sannan kin gama secondary kin shiga NCE sai suka daina biya miki dole kika hakura da karatu.
Mukus tayi duk abinda ya fada ba karya ciki,abincin ta mika masa tace na koshi,lokacin ya karba ya fara cin abinsa,ido Islaha ta tsura masa tana kallonsa kamar mayya,na miki kyau ne? ta tsinci muryarsa ya furta ba tare da ya kalle ta ba,da sauri ta dauke kanta ta fara wasa da yatsunta tana yarfe hannu,dariya yayi ba shiri tare da kamo hannunta yace mu gani ciwo yake,a hankali cike da kunya ta zame hannunta,tambaya ya jefo mata ke baki da kayan wasa ne muyi wasa? Cike da mamaki tace wanne irin wasa? A gidan ku ba a siya miki doll Baby su Teddy,murmushi tayi tace da girman nawa? baki ya turo,jajayen lips dinsa suka birge ta,kanta ta sadda kasa sabo da kunya,sun dade a haka kafin mutanen motar su dawo suka ci gaba da tafiya abin su.
Sai washe gari da safe suka isa lagos,Islaha bayan sun sauka,ta tambayi Sahil ina zaka kai? yace gari mana ya juya dauke da jakarsa yayi tafiyarsa ko waigowa bai sake yi ba,baki ta tabe tayi tafiyarta itama.
Gidansu ta nufa a taxi tana zuwa Kanwar Mamanta da suke kira da Aunty ta ga ta shigo da safe,ranta a bace tace uban me kika tsaya yi Islaha baki dawo da wuri ba,aikin gidan nan uban wa zai miki? Islaha cikin tsoro tace kiyi hakuri kin san motar da kika ce na shiga bata da sauri ga tsaye tsaye shi yasa,ke dalla rufe mana baki cewar Khairat yar Aunty ta cikinta,a kalla zata kai 30yrs,kanwarta Khalisat ce tace wannan fa sam bata da saiti,Islaha tayi shuru dai ita,Aunty tace ai kuwa ga aiki nan ya taru sai ki fara,a gajiye Islaha take amma haka ta fara aikin gidan.
Gidane me kyau cikin estate duk gidajen layin iri daya ne,gidan yana da kyau a me rufin asiri dai a lagos duk da unguwar ta masu karamin karfi ce amma tayi kyau,Islaha sai da ta gyara gidan tsaf ta gama komai tazo ta dora girkin dare,Khairat tace wankin namu fa sai yaushe? Zanyi gobe inshaallah,da sauran rana a gari madam ki wanke mana kaya,Khalisat ce ta kawo mata kaya ta jibge,Islaha haka tana girki tana wankin sai da ta gama tas,Allah yasa ma kayan ba dirty,sai da ta gama komai sannan ta samu tayi wanka ta canja kaya cikin riga da wandonta yan gwanjo amma sun mata kyau sosai abinka da me kyau,abincin ta ebo taci ta koshi,tana palo Yaseer ya shigo babban dan gidan Aunty,Aunty tace Yaseer bana son wannan yarinya r da kace zaka aura Rukayya take ko,Yaseer ya kalli Mahaifiyar su ya furta amma kin san an sa rana fa!
Aunty tace ai baza ka aure ta ba gaskiya na tambayi malamai na sunce sam ba Alkhairi a auren ku sannan indai ka aureta sunce kai da arziki sai dai kaga ana yi,nasan tun tana karama kuke soyayya hasalima ta samu mazajen aure amma ta makale sai kai ta dinga jiranka tun bamu da kudi gashi muna da rufin asiri amma baza ka aure ta ba,malamai sunce babu alkhairi.
Islaha tana jinsu tace amma ai ba wanda ya isa ya hana wani arziki a duniya,Allah shike bayarwa shike hanawa,Aunty rankwashi ta zubawa Islaha tace wlh idan ina magana kina sa min baki sai naci ubanki, shuru Islaha tayi tana jinsu har Yaseer dinma katon jahili ya yarda da abinda uwarsa ta furta,yace to Aunty ai kuwa sai dai kije wajen Malamai a cirewa Rukayya so na a ranta,idan ba haka ba ta ya zan iya cewa na fasa? karka damu wannan me sauki ne za a sa taji bata sonka da kanta tace ta fasa,ya furta to shike nan tunda ba alkhairi me zanyi da ita yanda nake so nayi kudi ido rufe.
Sahil machine ya hau yace kasuwar 'yan tumatir zaka kaini,me machine kuwa ya kaishi babbar kasuwar tumatir dake Lagos,hausawa da yare ne damkam ana ta hada hada,Sahil ya tsaya rataye da jakarsa yana kallon abinda akeyi,gashi su baza su iya aikin karfi ba,wani ne a ciki ya kalli Sahil ya ganshi ya dade a tsaye,ya zaci wani shahararren me kudi ne yazo daga kasar waje zai siyi tumatir,da sauri ya karaso gabansa yace
Good day sir, Hausa Sahil yayi yace sannu da aiki,ashe kana jin hausa ai na zaci daga Tunisia ka sauka,Sahil yace no,okay kaya zaka siya ne? Mota nawa kake so?
Sahil ya kalle shi yace aiki nazo nema ni dan gidan malam shehu ne,mutumin ya kalli Sahil sama da kasa yace aiki? Irin wanda muke yi na karfi na sauke tumatir daga mota?
Sahil ya amsa da ae mana shi,ai gidanmu ma sabo da bani da kudi idan aka ga hadari ya taso har danyar daddawa ake kaimin dakina na kwana sabo da kasan life no balance at all,yanzu idan baka da shi a gidanku sai uwarka ta mutu baka sani ba.
Wanda suke magana me suna Aminu dariya ya dinga yi yace gaye kamarka sabo da talauci sai a kai daddawa dakinka na kwana?
Sahil yace sai dai in hadari bai taso ba amma yana tasowa za a kawota a faranti.
Mutumin yace au baka da ko sisi a haka?kalli fa kayan jikinka sai me kudi ke sa irinsu"
Sahil ya furta ae nema dai zanyi,dariya mutumin yayi sosai yace kalli kalarka fa zaka iya kuwa? Zan iya mana,mutumin yace sunana Aminu to kaifa? Sahil nake,yace indai aikin wahala ne baya wahala zaka samu,ka sauke duk kwando daya 50 Naira.
Sahil yace zanyi haka,Sahil suna da karfi wanda bana mutane ba ma amma na aikin banza da anzo wanda mutum zai amfani kansa da shi sai lalaci yazo ya lullube su karfin bazai zo ba sam,haka ya ajiye jakarsa ya ratsa ta cikin kwandunan tumatir,Aminu yace waccen motar zamu je,suna karasawa Sahil ya shige cikin katuwar trailer a dole ya fito neman kudi,kwandon tumatir ya duka zai daga amma yayi yayi amma ya kasa,matasa dake wajen suka dinga ihu da dariya.
Sahil zuciya ya sake yi ya yunkura zai dauka amma yin duniya ya kasa yana matsawa kansa ma sai ya fada saman sauran kwandunan,mutane wannan ya ja hankalinsu aka taru ana kallonsa yana ta faman nishi da haki,mutane suna ta tunanin hutu ne ya masa yawa kawai duba da kalar jikinsa ana gani an san ajebo ne,masifa suka fara masa ya sakko musu daga mota,haka ya sakko kawai jikinsa a sanyaye.
Wajen masu abinci ya nufa sabo da tun a mota bai ci komai ba,ya samu ya siyi jullof din shinkafa da yankan namansa biyu ya zauna yaci ya sha pure water sannan ya mike ya mike ya koma cikin kasuwar.
Aminu ya kira ya tambaye shi dan Allah a ina kuke kwana? Aminu yayi dariya tare da nuna masa wasu dakuna na langa langa yace kaga wannan dakunan a haka duk shekara kasan nawa muke hadawa muna biya? Sahil ya tambaya nawa? Yace dubu dari biyu kalli dai dakine kamar container,a haka ma munfi mu ashirin a ciki wani kusan a kan wani yake kwana,sannan ka jira kaga wasu a inda suke kwana.
Sahil yayi mamaki ya koma gefe ya zauna,ga hadari ya hado sosai,yana zaune aka fara yayyafi sai yaga duk wasu suna saka rigar ruwa ga dare yayi wasu a cikin kurar ruwa da suke turawa ta eban kaya a ciki yaga sun saka kwali sun kwanta,wasu yan achaba a saman machinan su suka hau da rigar ruwa suka kwanta ruwa na dukan su,abin babu kyan gani yanda wasu a hausawan mu da gatansu da komai amma suke tafiya suna zubarwa da arewa mutunci,baza ka taba ganin yare a haka a wulakance a arewa ba da sunan neman kudi amma yan arewa duk inda kaskanci yake suna can,kana magana ace neman kudi ne,neman kudi sai mutum ya jefa rayuwarsa a hadari bayana a arewa ma wani yana da jarin da yafi zamansa a can.
Sahil dare yayi yana wata yar runfa a tsaye ya fake ga mutane sunyi yawa,wasu yan shaye shaye ne suka zo da gudu suka hankado Sahil cikin ruwan suka tsaya a rumfar babu inda Sahil zai fake gashi dare yayi ga ruwa ana tsinkawa kamar da bakin kwarya,waige waige ya fara cikin ruwan amma ba inda zai shiga,gani yayi babu amfanin tsaiwarsa kawai yabi ta cikin ruwan yana tafiya wanda bai san inda ya dosa ba,ruwa na dukansa yana ji wayarsa tana ringing yasan Sohail ne ke kiransa yaji ya sauka lafiya ba damar daga waya.
Yana ta tafiya cikin ruwan har ya bar layin ya shiga wani layin me kyau wanda bai san a ina yake ba,dai dai wani katafaren hotel yazo zai dan fake a jikin katangarsu, cikin tsararen hotel din ya kalla ya samu ya rakube ya fake a jikin wajen ya tsuguna! a haka yayi baccinsa har rana ta fito bai sani ba,karar mota ce tasa ya bude idonsa,kafafunsa har kumbura suka yi sosai,da kyar ya iya mikewa tsaye ya sake kallon cikin hotel din kenan