Sashe 37
Mumnunar Dabia Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sohail ne ya kwalawa maheera kira me shago tashi tayi ta fito, murmushi suka sakarwa juna tace yau kuma me shago nake? ta tambaya tare da rungume shi gashin kansa ya sosa tare da mika mata ledar,tace me yasa kake sosa gashi ne? Kwarkwata ce dani maybe,Sahil ya kawo miki tsaraba yace kiyi ta girki,dariya tayi tace ya dai kawo maka kaine me gida ai naku ne ba na Maheera ba,Kitchen suka shiga ya nuna mata buhu biyu ko budewa ba ayi ba,ta furta ashe abin na yi ne ,daurin da aka yiwa buhun ta kwance da wuka taga doya tace dama tamu bata fi daya ba gaskiya yayi kokari tab ga tsada,ta duba dayan taga dankalin turawa d,a ciki kuma ga ledar bacco biyu,ta fito da su daya taga garin kwakwi yellow dariya suka yi har Sohail yace ke wannan daraja ce da shi yanzu ajiye mana abinmu idan yunwar yamma ko ta rana ta taso ai ko da marmari shanye abinmu zamu yi, Maheera tace har Eba zan na yi ma,aka fito da Egusi da yawa,ga kwakwar manja ga kwakwar ruwa,ga kuma Guava,ga manja,Maheera tayi dariya tace ni wannan Lagos indai haka ne a dinga zuwa wlh,Islaha tana zaune a bedroom Sahil ya shigo tsoro taji ganin ya danna key a kofa.
Islaha sai zare ido take,ina kika tafi? Ya tambaya yana daga tsaye tace wai ranar da na tafi bayan an gama party? Wanne party? Waye yayi party? Islaha tace party fa wanda Sohail ya samu aiki har kuka ce ayi musanyan budurwa ka tuna? Wanne mahaukaci ne ke musayar budurwa kin taba ji anyi? Party yaushe muka hada wani party kuma? Islaha tace to ranar kuka ce na tafi da kanka kace na tafi wallahi zata yi kuka,ae wannan nasan ni nace sai nace ki tafi da dare? Zuciya nayi Allah ya gani ni yanzu ma ba dan kai nazo ba Wajen Maheera nazo,uhm naga alama ai cewa kika yi baza ki iya zama ba a wajen Hajiya kulu dole sai kinzo kin ganni mu fa ba a mana karya,Kasan Hajiya Kulu ne? Harararta yayi yace ban sani ba,kauyenku kika tafi ai,gidan Lalai,duk abinda suka yi da Lalai sai da ya bata labari ,tun da ba a fada masa ba sai yanzu da ta riga ta dawo,Islaha tace naci wahala a hannun Lalai har kanta hannuna yayi sabo da daka,Sahil yace tab Lalai sai ta kwana a tsaye tana daga yau,Islaha tace Kyaleta na yafe mata,ni ban yafe ba ya furta.
Yar uwata ce fa dattijuwa nace na yafe mata,ni ban yafe ba babu ruwana da wata Lalai, Kofar Islaha ta mike zata bude ya rike hannunta yace Lagos din me ya kaiki siyar da abinci? Tunda ka sani mene na tambaya kai fa ka koreni,ni ba wajenka nazo ba yanzu,wajen Maheera nazo jibi kuma zan tafiya ta naci gaba da tuwo tuwo na a bakin tasha kowa ya ganni, kuma shigar banza nake yi,dariya Sahil yayi yace to dan kinyi shigar banza ai ba sabon abu bane da dan bente ma na taba ganinki ,naji to ka bude kofar,Sohail ma da yake kwana da mace ba abinda ya mata har yanzu bare ni,kullum baccin asara suke yi,Islaha tayi dariya tace dan Allah ka kyale su suyi sunnar su mene sai an jira mu? Sahil yace me? ai ko ni Allah ya tsare ni da kallon Taskirar mace bare Sohail,dariya Islaha tayi tace to shike nan ai, muje ni yunwa nake ji,kofar ya bude suka fito,Maheera tana kitchen tana girki Sohail yana zaune ya ja kujera ya zauna bazai tayata aikin ba ko daya,Islaha ce ta shigo tace me zan gani haka kai da zaka mike ka tayata,Sohail yace so kike na zama mijin tace Allah ya kiyaye tuwo fa take yi kawai sai na fara tuka tuwo,Maheera tana tuka tuwon shinkafart tana jinsu.
Sahil yace maza sai dai su tuka nasu a Taskira,Sohail kunnensa ya toshe da sauri,Maheera tace Sahil babu kunyar sirika,Sahil yace gamu muma Daddy fa har England yaje ya tuka ya dawo,Sohail ya tashi yace karka koya mana iskanci,Ai Daddy shi ba Bismillah bare a'uzu shi yasa muka zo a haka,sai da Sahil ya bari Islaha ta dawo yace ni ai da nine nayi aure baka yi ba wlh bazan jiraka ba,ba dan iska bane ni da zauna ina jiranka,Maheera ta kalli Sahil haka kace Sahil? haka nace me yasa kuka jira ni,Islaha tayi dariya tace ai kunga sai ku dauki darasi.
Sohail yace an fada ma jiranka nake dama nima fakewa nake baza a ganni ba kaya ba,Maheera tace Allah ya kyauta kawai ta kasa gane ina suka dosa suyi gaba su dawo baya.
Yau Lalai da yamma ta kawo surfen masara ta zuba a turmi ta fara surfe abinta tunda ta fara bata tsaya ba daka kawai take ba hutu ko digo har dare yayi masarar tayi dugu dugu a turmi,ga uban zufa ta hada amma wani kaimi take karawa a dakan duf duf duf duf daka ba tsayawa, Abdulrazaqu ya shigo tun daga kofar gida yake jin daka na tashi ga dare yayi,maganar duniya Lalai ta kasa cewa kala kawai sai daka take, Abdulrazaqu ya riketa amma taki dainawa sai zazzaginsa da tayi tace wlh ka sake rikeni sai na tsine maka ka fita ka bar gidan nan zan tsine maka, Abdulrazaqu ya fice da sauri yana tambaya me yake faruwa ne da Lalai,Lalai taci gaba da Daka abinta makwafta na ji an rasa daga ina ake jin luguden daka,gashi kauye basa daka da dare sannan karamin gari ne kusan kowa sai yaji.
Abdulrazaqu gidan yan uwa da makwafta ya shiga tare da kiransu su kawo dauki Aljanu sun shigi Lalai,mutane suka taru a gidan Lalai amma kowa ya kasa kwace tabarya,duk wanda yaje jikinta sai ta zubar da shi a kasa yaji rauni,malam Ishu suka kira shi kuma ba malamin kirki bane kawai tsubbu ya iya,shima ya shigo da babbar riga da rawaninsa yaje da Niyyar dakatar da Lalai,hannu tasa ta bugar da shi nan take ta bazar da shi a kasa ya fadi baki duk ya fashe sai jini,mutane suna ganin haka suka ce yo Malami ma bai sha ba bare mu suka firgita suka fara tserewa aka rasa wanda zai dakatar da Lalai.
Allah sarki Abdulrazaqu shine ya zauna a gefe yana kallon Lalai tana ta faman daka kafin safiya Masara ta koma gari tilis hade da dusar, hannunta duk ya ruruce,tana daka ana tuna mata dakan da ta saka Islaha a kanta,kawai maganganu ake mata a kunne akan wahalar da ta bawa Islaha,sai da gari ya waye anyi kiran sallah sannan Lalai ta zube a wajen sumammiya, Abdulrazaqu yayi kanta da gudu yana bata agaji.
Sahil ya takurawa Islaha kamar jela ta shiga kitchen ya bita,Maheera kawo na tayaki cewar Islaha,Sahil yace a'a ki barta tayi abinta itace matar aure itace nauyi ya hau kanta,idan ma bata yi ba mijinta ne zai sha wahala,Islaha tace harda mu fa za aci,wa yace tace tuwo zata yi ai kinibibi ne sabo da taga kinzo shine ta tsiro da tuwo,Sohail ka tayata mana duk bautar da ka yiwa su Adnan sai matarka zaka kasa tayawa kuma kullum tare kuke bacci,gashi nan hannunka da jikinka duk sun kara laushi sabo da yanda Maheera take takura maka da rungume rungume,Maheera tace yaushe rabon da naji kana hira haka tunda Islaha ta tafi sai yau Sahil.
Sohail yana jinsu yace kanku ake ji,Islaha tukunyar miya ta bude tace me ya rage? yanzu fa zanyi ki nika min Egusi,Sahil hannun Islaha ya bige yace da nasan haka za ayi bazan kawo tsarabar nan ba ko hutawa bata yi ba,kina ganin yarinya ta taho zubar da mutuncinta ki takura mata,Islaha dariya tayi ta rufe baki,Sohail tashi yayi yace duk kuje baza a zauna ana wulakanta min mata ba.
Mikewa yayi ya taya Maheera girkin suka gama su Islaha suna palo taki magana sosai wai yanga take nan ramawa take a haka wulakanci take yiwa Sahil a ganinta,bayan kulashi take yi.
Sahil ne ya sata a gaba yana kallonta ya zuba tagumi yana kallonta kamar ya samu tv,Sohail ne ya fito ya tsaya a gaban Islaha,Sahil ya ture shi gefe ba tare da yayi magana ba yaci gaba da kallonsa,Islaha har gajiya tayi da kallon jarabar da yake mata,Sohail yace kai wannan kallon ya wuce na musulunci sabo da kaga araharta kawai a tura a kai kudi danginta a huta wannan wanne irin abu ne sai ka sa budurcinta ya lalace ai.
Dariya suke mugun bawa Islaha,Maheera tana gamawa ta wuce tace bari nayi wanka Sohail yace muje kiyi wankan ki bani na saka miki brazia burina kenan ni kullum na dinga sakawa mata ita,Maheera tace au ba ni kadai ba mata ma? yace to yanzu ina zanje na sawa wata idan ba ke ba,jeki ina kallo ai yanda kike sawa nayi degree,ka daina jin kunyar tawa? Jin kunyar marar kunya asara ne muje kawai amma ni zan fara wanka tace naji jeka,Toilet ya shiga sai data bari yana wanka ta bude toilet din,da sauri ya tsuguna yana zuba mata ruwan masifa kamar zai cinye ta,masifar da yayi bata taba ganin Sohail yayi fada ba sai yau,ba shiri ta fito ta zauna a gefen bed ta zuba tagumi tace wai mijinka guda wannan wacce masifa ce.
Islaha sai zare ido take,ina kika tafi? Ya tambaya yana daga tsaye tace wai ranar da na tafi bayan an gama party? Wanne party? Waye yayi party? Islaha tace party fa wanda Sohail ya samu aiki har kuka ce ayi musanyan budurwa ka tuna? Wanne mahaukaci ne ke musayar budurwa kin taba ji anyi? Party yaushe muka hada wani party kuma? Islaha tace to ranar kuka ce na tafi da kanka kace na tafi wallahi zata yi kuka,ae wannan nasan ni nace sai nace ki tafi da dare? Zuciya nayi Allah ya gani ni yanzu ma ba dan kai nazo ba Wajen Maheera nazo,uhm naga alama ai cewa kika yi baza ki iya zama ba a wajen Hajiya kulu dole sai kinzo kin ganni mu fa ba a mana karya,Kasan Hajiya Kulu ne? Harararta yayi yace ban sani ba,kauyenku kika tafi ai,gidan Lalai,duk abinda suka yi da Lalai sai da ya bata labari ,tun da ba a fada masa ba sai yanzu da ta riga ta dawo,Islaha tace naci wahala a hannun Lalai har kanta hannuna yayi sabo da daka,Sahil yace tab Lalai sai ta kwana a tsaye tana daga yau,Islaha tace Kyaleta na yafe mata,ni ban yafe ba ya furta.
Yar uwata ce fa dattijuwa nace na yafe mata,ni ban yafe ba babu ruwana da wata Lalai, Kofar Islaha ta mike zata bude ya rike hannunta yace Lagos din me ya kaiki siyar da abinci? Tunda ka sani mene na tambaya kai fa ka koreni,ni ba wajenka nazo ba yanzu,wajen Maheera nazo jibi kuma zan tafiya ta naci gaba da tuwo tuwo na a bakin tasha kowa ya ganni, kuma shigar banza nake yi,dariya Sahil yayi yace to dan kinyi shigar banza ai ba sabon abu bane da dan bente ma na taba ganinki ,naji to ka bude kofar,Sohail ma da yake kwana da mace ba abinda ya mata har yanzu bare ni,kullum baccin asara suke yi,Islaha tayi dariya tace dan Allah ka kyale su suyi sunnar su mene sai an jira mu? Sahil yace me? ai ko ni Allah ya tsare ni da kallon Taskirar mace bare Sohail,dariya Islaha tayi tace to shike nan ai, muje ni yunwa nake ji,kofar ya bude suka fito,Maheera tana kitchen tana girki Sohail yana zaune ya ja kujera ya zauna bazai tayata aikin ba ko daya,Islaha ce ta shigo tace me zan gani haka kai da zaka mike ka tayata,Sohail yace so kike na zama mijin tace Allah ya kiyaye tuwo fa take yi kawai sai na fara tuka tuwo,Maheera tana tuka tuwon shinkafart tana jinsu.
Sahil yace maza sai dai su tuka nasu a Taskira,Sohail kunnensa ya toshe da sauri,Maheera tace Sahil babu kunyar sirika,Sahil yace gamu muma Daddy fa har England yaje ya tuka ya dawo,Sohail ya tashi yace karka koya mana iskanci,Ai Daddy shi ba Bismillah bare a'uzu shi yasa muka zo a haka,sai da Sahil ya bari Islaha ta dawo yace ni ai da nine nayi aure baka yi ba wlh bazan jiraka ba,ba dan iska bane ni da zauna ina jiranka,Maheera ta kalli Sahil haka kace Sahil? haka nace me yasa kuka jira ni,Islaha tayi dariya tace ai kunga sai ku dauki darasi.
Sohail yace an fada ma jiranka nake dama nima fakewa nake baza a ganni ba kaya ba,Maheera tace Allah ya kyauta kawai ta kasa gane ina suka dosa suyi gaba su dawo baya.
Yau Lalai da yamma ta kawo surfen masara ta zuba a turmi ta fara surfe abinta tunda ta fara bata tsaya ba daka kawai take ba hutu ko digo har dare yayi masarar tayi dugu dugu a turmi,ga uban zufa ta hada amma wani kaimi take karawa a dakan duf duf duf duf daka ba tsayawa, Abdulrazaqu ya shigo tun daga kofar gida yake jin daka na tashi ga dare yayi,maganar duniya Lalai ta kasa cewa kala kawai sai daka take, Abdulrazaqu ya riketa amma taki dainawa sai zazzaginsa da tayi tace wlh ka sake rikeni sai na tsine maka ka fita ka bar gidan nan zan tsine maka, Abdulrazaqu ya fice da sauri yana tambaya me yake faruwa ne da Lalai,Lalai taci gaba da Daka abinta makwafta na ji an rasa daga ina ake jin luguden daka,gashi kauye basa daka da dare sannan karamin gari ne kusan kowa sai yaji.
Abdulrazaqu gidan yan uwa da makwafta ya shiga tare da kiransu su kawo dauki Aljanu sun shigi Lalai,mutane suka taru a gidan Lalai amma kowa ya kasa kwace tabarya,duk wanda yaje jikinta sai ta zubar da shi a kasa yaji rauni,malam Ishu suka kira shi kuma ba malamin kirki bane kawai tsubbu ya iya,shima ya shigo da babbar riga da rawaninsa yaje da Niyyar dakatar da Lalai,hannu tasa ta bugar da shi nan take ta bazar da shi a kasa ya fadi baki duk ya fashe sai jini,mutane suna ganin haka suka ce yo Malami ma bai sha ba bare mu suka firgita suka fara tserewa aka rasa wanda zai dakatar da Lalai.
Allah sarki Abdulrazaqu shine ya zauna a gefe yana kallon Lalai tana ta faman daka kafin safiya Masara ta koma gari tilis hade da dusar, hannunta duk ya ruruce,tana daka ana tuna mata dakan da ta saka Islaha a kanta,kawai maganganu ake mata a kunne akan wahalar da ta bawa Islaha,sai da gari ya waye anyi kiran sallah sannan Lalai ta zube a wajen sumammiya, Abdulrazaqu yayi kanta da gudu yana bata agaji.
Sahil ya takurawa Islaha kamar jela ta shiga kitchen ya bita,Maheera kawo na tayaki cewar Islaha,Sahil yace a'a ki barta tayi abinta itace matar aure itace nauyi ya hau kanta,idan ma bata yi ba mijinta ne zai sha wahala,Islaha tace harda mu fa za aci,wa yace tace tuwo zata yi ai kinibibi ne sabo da taga kinzo shine ta tsiro da tuwo,Sohail ka tayata mana duk bautar da ka yiwa su Adnan sai matarka zaka kasa tayawa kuma kullum tare kuke bacci,gashi nan hannunka da jikinka duk sun kara laushi sabo da yanda Maheera take takura maka da rungume rungume,Maheera tace yaushe rabon da naji kana hira haka tunda Islaha ta tafi sai yau Sahil.
Sohail yana jinsu yace kanku ake ji,Islaha tukunyar miya ta bude tace me ya rage? yanzu fa zanyi ki nika min Egusi,Sahil hannun Islaha ya bige yace da nasan haka za ayi bazan kawo tsarabar nan ba ko hutawa bata yi ba,kina ganin yarinya ta taho zubar da mutuncinta ki takura mata,Islaha dariya tayi ta rufe baki,Sohail tashi yayi yace duk kuje baza a zauna ana wulakanta min mata ba.
Mikewa yayi ya taya Maheera girkin suka gama su Islaha suna palo taki magana sosai wai yanga take nan ramawa take a haka wulakanci take yiwa Sahil a ganinta,bayan kulashi take yi.
Sahil ne ya sata a gaba yana kallonta ya zuba tagumi yana kallonta kamar ya samu tv,Sohail ne ya fito ya tsaya a gaban Islaha,Sahil ya ture shi gefe ba tare da yayi magana ba yaci gaba da kallonsa,Islaha har gajiya tayi da kallon jarabar da yake mata,Sohail yace kai wannan kallon ya wuce na musulunci sabo da kaga araharta kawai a tura a kai kudi danginta a huta wannan wanne irin abu ne sai ka sa budurcinta ya lalace ai.
Dariya suke mugun bawa Islaha,Maheera tana gamawa ta wuce tace bari nayi wanka Sohail yace muje kiyi wankan ki bani na saka miki brazia burina kenan ni kullum na dinga sakawa mata ita,Maheera tace au ba ni kadai ba mata ma? yace to yanzu ina zanje na sawa wata idan ba ke ba,jeki ina kallo ai yanda kike sawa nayi degree,ka daina jin kunyar tawa? Jin kunyar marar kunya asara ne muje kawai amma ni zan fara wanka tace naji jeka,Toilet ya shiga sai data bari yana wanka ta bude toilet din,da sauri ya tsuguna yana zuba mata ruwan masifa kamar zai cinye ta,masifar da yayi bata taba ganin Sohail yayi fada ba sai yau,ba shiri ta fito ta zauna a gefen bed ta zuba tagumi tace wai mijinka guda wannan wacce masifa ce.