Sashe 36
Mumnunar Dabia Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Alhaji Umaru dariya ta kamashi yace wannan gaskiyar taka yasa zan baka 'yata ka aura...da sauri Sahil yace ni bani da wata gaskiya makaryaci ne,karya ce dani,Alhaji Umaru yayi dariya yace tashi ka tafi time din Flight dinka yayi amma ka sani kana da budurwa a nan ta biyu da zaka aura,kasan kuma idan na fadawa Daddy ko baka yarda ba sai dai kaji an daura auren,Sahil yace zata sha saki kuwa a ranar nidai ba ruwana, ina da budurwa fa,Alhaji Umaru a ransa yace a hankali zaka so Amatullah ne na riga na fahimci halayarku a hankali kuna ganewa,Shi dai Alhaji Umaru Sahil ya cancanta ya auri yarsa a wajensa.
Sahil bangarensa ya koma sai da ya karya yayi wanka ya fito cikin wasu kana nan kayan fadar irin kyan da yayi bata lokaci ne,part din Alhaji Umaru ya shiga ya same shi a palo tare da yarsa Amatullah sai shagwaba take yi, yace Sahil ka dage kai gida zaka tafi? Sahil yace papers din duk ba nayi abinda kace ba? ai mun gama kace zaka kirani idan wanda zamuyi aikin tare zaizo ko? Alhaji Umaru yace ae ai nufi na ka sake hutawa amma abinda ya kawo ka an gama shi tun jiya da dare,Sahil murmushi yayi yace nidai tafiya zanyi indai da wani abu kawai ka kirani,yace ai Abuja zaka yi aikin karka damu naga baka son Lagos.
Sallama ya masa,Amatullah harda cewa Yaya Sahil ka gaida gida sai munyi waya,Sahil yace ni bani da kanwa mace daga ni sai Sohail,Amal ce kuma yayar mu ce itama,Juyawa yayi ya tafiyarsa.
Sahil da kudade masu nauyi ya wuce airport driver ya kaishi,Alhaji Umaru ne ya tura masa,Sahil ya tambayi driver yace me ake siya a garin nan na tsaraba? Driver yace hausawa ai in zasu koma doya suke siya sai manja,da kwakar manja,coconut da garin kwaki shi zaka ga suna siya har Egusi suna siya.
Sahil yace kaini inda ake siyarwa,driver ya kaishi doya kadai ya siya ta kai guda ashirin manya,dankalin turawa ma da yawa, ya siyi egusi da yawa shima sabo me kyau,har garin kwaki wurin kwano uku ya siya,kwakar ruwa tafi goma,har kwakwar manja,yaga guava masu kyau ya siya,tarkace ya siya,ya kashe kudi sosai yace shi fa ba tafiya zai iyayi da su ba sai dai a sa a mota a kai can ya karba a Abuja,kayansa aka shirya masa waje daya aka saka a mota ya biya kudin kaya motar ma ta rigashi tafiya daga Lagos zuwa Abuja.
Yana hanya Islaha ma tana hanya a lokacin.
Ya riga ta zuwa kasancewar ita a mota ne,yana komawa Maheera ta bude kofa yace Amarya kina wulakanci a gidan nan karki kashe min dan uwa da wanka,dariya tayi Maheera tace ina tsarabar? Sahil yace ni ban taho da komai ba amma na sa a mota za a kawo in sunzo zasu kirani naje na karba,me ka siyo? idan an kawo zaki gani ya wuce dakinsa,Islaha sai gaf da magriba ta sauka,tana zuwa gidan su Adnan ta wuce,knocking tayi,Madam Oge ce ta fito tare da bude kofar tace can i help you? Ibrahim ne ya leko sai yaga Islaha yayi mamaki,yace ina kika shiga zuwana garinku sau uku kin gudu,Islaha tace ni ba wajenka nazo ba ina Maheera?
Ibrahim yace ta mutu,kyale shi tayi ta zaro wayarta zata kira Maheera yace muje na kaiki gidansu ma, tace idan kasan wasa kake ka kyale ni,yace ba wasa ai tayi aure,Islaha tace aure? da wuri haka har tayi aure har yaushe na bar gidan,wa ta aura?Ibrahim yace muje na kaiki,motarsa ya bude ta ajiye kayanta a baya ta shiga gaban mota yaja suka tafi.
Magana ya mata yace yaushe zan kai kudin aure ne? Islaha ta masa shuru,yace ke yanzu kinfi son mahaukaci sabo da kyau? tana jinsa yana ta zagin su Sohail tace wai wacce irin rayuwa ce wannan taku dan uwanka ubanku daya amma ku dinga irin wannan,wacce irin kiyayya ce haka,me suka muku? aji tsoron duniya gaskiya,banza ya mata sabo da kishin da yake taso masa.
Har Estate din Sohail ya kai Islaha a kofar gidan yayi parking yace sabo da son da nake miki na kawo ki amma badan haka ba babu abinda zai kawo ni,tana zaune a motar tace dan Allah ku daina yi musu haka yan uwanku ne fa,suna haka Sahil ya fito cikin motar ya kalla,kamar Islaha ya gani,gaban motar ta bude ta fito,Ibrahim yana ganin Sahil yayi murmushin mugunta,motar ya bude ya fito Islaha ta dauki jakarta ita kanta ganin Sahil wai haushinsa take ji ya koreta sai ta juya tana yiwa Ibrahim magana harda kirkiro dariya.
Sahil yana ganin haka ya wuce abinsa har ya tafi ya kasa hakura ya dawo, Ibrahim sai damka yaji kawai ya shake shi,kamar zai kashe shi,sai kakarin mutuwa yake,da hannu daya kacal ya shake shi amma sai da ya raba shi da kasa ya daga shi cak,Islaha ta saki ihu tana neman agaji,ga unguwa ba mutane,wasu samari ne suka ga abinda ke faruwa,idon Sahil ya canja sai huci yake jikinsa yana rawa,agaji suka kawo da kyar aka kwaci Ibrahim a hannun Sahil,Ibrahim yana hakki yana shafa wuyansa yace ni ka yiwa haka kana kanina? Wlh sai kasan kayi min haka, Sahil tsaki ya ja yace duk abinda zaka yi kayi,Ibrahim zai sake magana Sahil ya nufi inda yake,ai da gudu ya zaga tare da fadawa motarsa ya ja ya bar wajen a guje,yasan karfin aljanu ne da su yanzu sai su illata mutum a banza.
Islaha ya kalla ta kalle shi tsoro taji sosai yanda ya bata rai kamar zaiyi gunduwa gunduwa da ita haka ya koma ya nufi inda take idonsa sai zallar bacin rai a ciki,Juyawa tayi da gudu tana tibi tibi wai gudu take yi abinda taku daya zai kamata,Juyowa tayi taga ya biyota, wayyooo tace tana gudu,dariya ma ta bashi yanda take gudun.
Tsayawa yayi ta tsaya nesa da shi tana hakki tace karya nake ba kulashi nake ba,to dawo yace, Wayarta ta dakko ta kira Maheera,Maheera mamaki tayi tana kwance a palo taga kiran Islaha,dagawa tayi tare da furta Islaha kece? Ina kofar gida ki bude min dan Allah Sahil zai duke ni,Maheera ta bude kofar taga Islaha can nesa Sahil a nesa shima,Islaha ta shige ciki da gudu,Sahil yayi tafiyarsa inda zaije,farin ciki yake.
Yace yau duk garin nan ba wanda ya isa ya kaini nishadi,harda canja taku,yau kowa sai ya shiga uku da mutunci na.
Sohail kuwa ya tsaya siyowa Maheera kayan ciye ciye bai dawo gida da wuri ba sai da Sahil yaje ya karbo tsarabarsa ta lagos sannan Sohail shima yayi parking da motarsa ya fito sai ga Sahil a taxi da kaya a buhu har biyu manya,yace wai sai da ka siyo wani abu amma a mota ka dora mene haka? Sahil yace ina ruwanka na Maheera ne ba itace me girki ba,Me taxi din ya bawa kudi yace shigar min da shi ciki please,Sohail yace tab ya barsu a nan haka kawai ya shiga ya kallar min mata,Me taxi yayi murmushi,Sahil yace jeka to na bar maka kudin,yayi godiya ya tafi,da kansu suka dauki kayan suka shigar da su da kyar, su biyu amma daukan kaya ya zama aiki sai wahala suke sha a haka suka shigar da shi da kyar.
Maheera da Islaha sun shige bedroom sai labari suke bawa juna bayan rabuwa,Islaha tace ashe dai Allah ya buda gashi har kin auri Sohail saura muga ciki,Maheera murmushi tayi tace bayan ke ake jira ba abinda aka yi,Islaha ta bude baki Maheera tace wlh bama ko romance wai sai kin dawo Sahil ya aure ki,Islaha ta dinga dariya tace kinga ta kanki Maheera Allah ya kara hakuri,yanzu ni tunanina idan aka aureni nima aka ki yin komai fa muka dora a haka,Maheera tace a hankali zasu gane karki damu,kawai dai ki dinga hakuri da su tunda kin san halinsu.
Sahil bangarensa ya koma sai da ya karya yayi wanka ya fito cikin wasu kana nan kayan fadar irin kyan da yayi bata lokaci ne,part din Alhaji Umaru ya shiga ya same shi a palo tare da yarsa Amatullah sai shagwaba take yi, yace Sahil ka dage kai gida zaka tafi? Sahil yace papers din duk ba nayi abinda kace ba? ai mun gama kace zaka kirani idan wanda zamuyi aikin tare zaizo ko? Alhaji Umaru yace ae ai nufi na ka sake hutawa amma abinda ya kawo ka an gama shi tun jiya da dare,Sahil murmushi yayi yace nidai tafiya zanyi indai da wani abu kawai ka kirani,yace ai Abuja zaka yi aikin karka damu naga baka son Lagos.
Sallama ya masa,Amatullah harda cewa Yaya Sahil ka gaida gida sai munyi waya,Sahil yace ni bani da kanwa mace daga ni sai Sohail,Amal ce kuma yayar mu ce itama,Juyawa yayi ya tafiyarsa.
Sahil da kudade masu nauyi ya wuce airport driver ya kaishi,Alhaji Umaru ne ya tura masa,Sahil ya tambayi driver yace me ake siya a garin nan na tsaraba? Driver yace hausawa ai in zasu koma doya suke siya sai manja,da kwakar manja,coconut da garin kwaki shi zaka ga suna siya har Egusi suna siya.
Sahil yace kaini inda ake siyarwa,driver ya kaishi doya kadai ya siya ta kai guda ashirin manya,dankalin turawa ma da yawa, ya siyi egusi da yawa shima sabo me kyau,har garin kwaki wurin kwano uku ya siya,kwakar ruwa tafi goma,har kwakwar manja,yaga guava masu kyau ya siya,tarkace ya siya,ya kashe kudi sosai yace shi fa ba tafiya zai iyayi da su ba sai dai a sa a mota a kai can ya karba a Abuja,kayansa aka shirya masa waje daya aka saka a mota ya biya kudin kaya motar ma ta rigashi tafiya daga Lagos zuwa Abuja.
Yana hanya Islaha ma tana hanya a lokacin.
Ya riga ta zuwa kasancewar ita a mota ne,yana komawa Maheera ta bude kofa yace Amarya kina wulakanci a gidan nan karki kashe min dan uwa da wanka,dariya tayi Maheera tace ina tsarabar? Sahil yace ni ban taho da komai ba amma na sa a mota za a kawo in sunzo zasu kirani naje na karba,me ka siyo? idan an kawo zaki gani ya wuce dakinsa,Islaha sai gaf da magriba ta sauka,tana zuwa gidan su Adnan ta wuce,knocking tayi,Madam Oge ce ta fito tare da bude kofar tace can i help you? Ibrahim ne ya leko sai yaga Islaha yayi mamaki,yace ina kika shiga zuwana garinku sau uku kin gudu,Islaha tace ni ba wajenka nazo ba ina Maheera?
Ibrahim yace ta mutu,kyale shi tayi ta zaro wayarta zata kira Maheera yace muje na kaiki gidansu ma, tace idan kasan wasa kake ka kyale ni,yace ba wasa ai tayi aure,Islaha tace aure? da wuri haka har tayi aure har yaushe na bar gidan,wa ta aura?Ibrahim yace muje na kaiki,motarsa ya bude ta ajiye kayanta a baya ta shiga gaban mota yaja suka tafi.
Magana ya mata yace yaushe zan kai kudin aure ne? Islaha ta masa shuru,yace ke yanzu kinfi son mahaukaci sabo da kyau? tana jinsa yana ta zagin su Sohail tace wai wacce irin rayuwa ce wannan taku dan uwanka ubanku daya amma ku dinga irin wannan,wacce irin kiyayya ce haka,me suka muku? aji tsoron duniya gaskiya,banza ya mata sabo da kishin da yake taso masa.
Har Estate din Sohail ya kai Islaha a kofar gidan yayi parking yace sabo da son da nake miki na kawo ki amma badan haka ba babu abinda zai kawo ni,tana zaune a motar tace dan Allah ku daina yi musu haka yan uwanku ne fa,suna haka Sahil ya fito cikin motar ya kalla,kamar Islaha ya gani,gaban motar ta bude ta fito,Ibrahim yana ganin Sahil yayi murmushin mugunta,motar ya bude ya fito Islaha ta dauki jakarta ita kanta ganin Sahil wai haushinsa take ji ya koreta sai ta juya tana yiwa Ibrahim magana harda kirkiro dariya.
Sahil yana ganin haka ya wuce abinsa har ya tafi ya kasa hakura ya dawo, Ibrahim sai damka yaji kawai ya shake shi,kamar zai kashe shi,sai kakarin mutuwa yake,da hannu daya kacal ya shake shi amma sai da ya raba shi da kasa ya daga shi cak,Islaha ta saki ihu tana neman agaji,ga unguwa ba mutane,wasu samari ne suka ga abinda ke faruwa,idon Sahil ya canja sai huci yake jikinsa yana rawa,agaji suka kawo da kyar aka kwaci Ibrahim a hannun Sahil,Ibrahim yana hakki yana shafa wuyansa yace ni ka yiwa haka kana kanina? Wlh sai kasan kayi min haka, Sahil tsaki ya ja yace duk abinda zaka yi kayi,Ibrahim zai sake magana Sahil ya nufi inda yake,ai da gudu ya zaga tare da fadawa motarsa ya ja ya bar wajen a guje,yasan karfin aljanu ne da su yanzu sai su illata mutum a banza.
Islaha ya kalla ta kalle shi tsoro taji sosai yanda ya bata rai kamar zaiyi gunduwa gunduwa da ita haka ya koma ya nufi inda take idonsa sai zallar bacin rai a ciki,Juyawa tayi da gudu tana tibi tibi wai gudu take yi abinda taku daya zai kamata,Juyowa tayi taga ya biyota, wayyooo tace tana gudu,dariya ma ta bashi yanda take gudun.
Tsayawa yayi ta tsaya nesa da shi tana hakki tace karya nake ba kulashi nake ba,to dawo yace, Wayarta ta dakko ta kira Maheera,Maheera mamaki tayi tana kwance a palo taga kiran Islaha,dagawa tayi tare da furta Islaha kece? Ina kofar gida ki bude min dan Allah Sahil zai duke ni,Maheera ta bude kofar taga Islaha can nesa Sahil a nesa shima,Islaha ta shige ciki da gudu,Sahil yayi tafiyarsa inda zaije,farin ciki yake.
Yace yau duk garin nan ba wanda ya isa ya kaini nishadi,harda canja taku,yau kowa sai ya shiga uku da mutunci na.
Sohail kuwa ya tsaya siyowa Maheera kayan ciye ciye bai dawo gida da wuri ba sai da Sahil yaje ya karbo tsarabarsa ta lagos sannan Sohail shima yayi parking da motarsa ya fito sai ga Sahil a taxi da kaya a buhu har biyu manya,yace wai sai da ka siyo wani abu amma a mota ka dora mene haka? Sahil yace ina ruwanka na Maheera ne ba itace me girki ba,Me taxi din ya bawa kudi yace shigar min da shi ciki please,Sohail yace tab ya barsu a nan haka kawai ya shiga ya kallar min mata,Me taxi yayi murmushi,Sahil yace jeka to na bar maka kudin,yayi godiya ya tafi,da kansu suka dauki kayan suka shigar da su da kyar, su biyu amma daukan kaya ya zama aiki sai wahala suke sha a haka suka shigar da shi da kyar.
Maheera da Islaha sun shige bedroom sai labari suke bawa juna bayan rabuwa,Islaha tace ashe dai Allah ya buda gashi har kin auri Sohail saura muga ciki,Maheera murmushi tayi tace bayan ke ake jira ba abinda aka yi,Islaha ta bude baki Maheera tace wlh bama ko romance wai sai kin dawo Sahil ya aure ki,Islaha ta dinga dariya tace kinga ta kanki Maheera Allah ya kara hakuri,yanzu ni tunanina idan aka aureni nima aka ki yin komai fa muka dora a haka,Maheera tace a hankali zasu gane karki damu,kawai dai ki dinga hakuri da su tunda kin san halinsu.