← Book details Mumnunar Dabia Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 5 OF 46

Sashe 5

Mumnunar Dabia Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Sai da ya nuna musu ko ina na gidan sannan suka koma palo,Sohail yace wash na gaji,Ibrahim ne ya shigo yana magana yace ai ba hutu ne ya kawo ku ba,kai bari kuji aikinku a gidan nan
Gyara gidan nan ku share ko ina ku goge,sannan kuyi mana wanki da guga, kuyi girki,ku wanke mana motoci kullum,bude gate da kullewa,komai da kuka sani na gyara gida da kula da shi kune zaku yi shi kunji,su Sahil suka ce sun ji,su kansu ganin basu san komai ba sun hakura da rayuwar, tunda ana kiransu da mahaukata gani suke basu da amfani a duniya,gani suke ba abinda zasu iya tabukawa a duniya,shi yasa suka hakura kawai tunda sunga kowa baya daukan su a mutane,kuma suma abinda suke yi da abinda suke ganin suna yi sai yasa suke ganin lallai ba daidai suke da kowa ba,suka riki aikinsu hannu bibiyu,sun zama 'yan aiki ta karfi, sun fara musu bauta ba ji ba gani har sun kai matakin samari na gaske ya isa ace sun kammala degree din su amma sun kare a bautar yan uwan su, sun kwashe shekaru biyu suna bauta musu.

Su Sohail sun girma sosai dan sunfi ma su adnan girman jiki da tsayi,kai in ba fada maka aka yi ba baka isa ka gane wane Sahil wane Sohail ba sai wanda ya mugun saninsu zai iya tantancewa shima ba ko yaushe ba,kansu daya,tsayinsu daya cif,kibarsu da jikinsu komai irinsu daya kai daya babu banbanci,sun ajiye saje da gemu madaidaici,gasu jajir da su,ga tsayi gasu su ba ramammu ba sannan baza ace suna da kiba ba,idanuwansu masu kyau farare tas,gasu da yalwar gashin gira da sumar kansu me kyau da baki sai sheki suke yi kawai,kana ganinsu kasan ba wahala a tare da su,sai dai suna bautuwa sosai, ko waye ya kalle su bazai so ya dauke idonsa a kansu ba,gasu da kwarjini da cikar zati,gasu da tsafta ta gaske ga daukan wanka tunda ana basu sutura da cima me kyau,komai iri daya suke yinsa,kawai banbancinsu Sahil yana da wushirya yar kadan shi kuwa Sohail baida ita banda wannan basu da banbancin da za a gane waye Sahil waye Sohail,halayyar su ma tazo kusan daya,Sohail yafi fara'a,Sahil baida wata fara'a sai dai in suna tare da Sohail kawai zaka ga yana dariya, 'yan mata kuwa basa tunanin ma sun kai mutanen da har zasu iya son mace bare su aure ta wannan yasa ma su ba ruwansu da mata basa harkar su.

Ci gaban labari

Ibrahim ne ya shiga kwalawa Sahil kira "Sahil" "Sahil" kamar zai fasa gidan,Sahil ya fito da gudu a gigice,dake su ba wahala sun gigice sun rude,sanye yake cikin gajeren wando da riga armless maroon,Ibrahim yana wani gadara ya sha wata azababbiyar shadda fara yana shining yace baka da hankali,jakin ina ne kai kalli takalmin da koge min,brown nace ka goge? Na fada maka meeting zanje black nace ka goge min amma ka goge min brown useless,karbi ka goge wannan,kuma idan 15mnt tayi baka goge ba wlh sai ka gane kurenka stupid,Jikin Sahil yana rawa ya karba yace kana nufin a goge wannan? a'a goshin uwarka zaka goge min,Sahil yace uwata ai bata nan ina zan ganta na goge maka goshinta? Dan Allah ka taimake ni ina zanga Mummy na goge maka goshinta? Kuma kasan Mama ta rasu,dama Mama tana raye wlh sai naje Kano na goge maka goshin nata,cike da mamaki Ibrahim ya tsaya sololo yana kallon Sahil,yau ya tabbatar Sahil basu da hankali,tsaki yaja yace "Sahil" yace na'am ka goge min takalmi zan fita, a goge dai ko kace? Sahil ya sake tambaya,Ibrahim ya hasala sosai ya sake dakawa Sahil tsawa ya juya ya tafi gogewa.

Adnan kuwa cikin shirinsa ya fito zai fita ya samu motarsa da yace zai hau da alama ba a wanke ta ba,Sohail ya dinga kwalawa kira,Sohail ya fito, yana zuwa Adnan ya fara bala'i kai dan uwarka wacce motar nace ka wanke? yace bakar na wanke,haka nace? ae cewa kayi na wanke maka fara kawai ni kuma na wanke bakar tafi kyau, Adnan ya zaro ido yace are you mad? Ni in saka abu ka canja min zabi,ba komai ai zaka aikata ai kafi kowa hauka da ciwon aka haife ka dalla bani key ya fisge key dinsa ya wuce ya shiga motarsa ya tafi,Sohail ya juya ya wuce kitchen ya duba ba abubuwa da yawa wanda yana bukata yayi amfani da su wajen girkin da zasu yi, yana shirin fita ya siyo kawai Ibrahim ya dawo ya kulle kitchen din yace tunda baku da hankali sai kunyi kwana bakwai baku ci abinci a gidan nan ba,sai dai ku siya da kudinku useless ya juya ya tafi,Sahil ya kalli Sohail suka yi shuru basu ce kala ba.

Yau haka suka yini basu ci komai ba a gidan gashi su Ibrahim a waje zasu ci hadadde abinsu,su kuwa basu ma da kudin ko sisi sabo da kawai komai sai dai su gani an siya musu har sutura ba a basu kudin su siya an maida su kamar yara,idan ma sunce a basu kudi baya wuce 1k, Sahil dazu kace zaka je shopping ina kudin? Sohail yace ai kasan kayan abincin dama idan munje su suke transfer da kansu sai dai kawai mu karbo a shagon,Sahil yace na tuna kuma gashi har yamma tayi likis wlh yunwa nake ji, fita zamu yi ko zamu samu wani abu,Sahil yace nifa na gaji da wannan rayuwar bro gidan nan zan bari na gudu kawai,Idan ka tafi ina zaka je? Wa kake da shi? Sohail ya tambaya,Kazo mu gudu kawai,Sohail yace ba inda zanje ni,ina zani bamu da hankali ance waye zai zauna damu a haka,Sahil yace to zan tafi na barka ni domin gwara naje na bautawa wasu wlh,Sohail yace a dawo lafiya ma dinga waya.

Tafiya suke yi kawai a titi har sai da suka bar layinsu suka bar unguwar ma baki daya,sai da suka shiga wata unguwar suka samu wani shago karami da shi kamar container ce ma har sun wuce Sohail yace muje kaga wata a ciki kamar zamu samu wani abu,dawowa suka yi da baya wata budurwa ce kyakyawa ajin karshe ta saka face mask tana zaune a ciki,tana danna waya,ganinta da suffar musulmi suka furta salamu alaykum cewar Sohail,Sahil kuwa ya hade rai yana gefe a tsaye.

Amsawa tayi sannan tace me za a baka? Sohail bai kulata ba, wani botikin gyada fari me murfi dake gabanta ya fara yin kida da hannu biyu yana kida da bokitin,ta tsaya tana kallon ikon Allah!

Dariya yayi ya tsaya yace to ya aka yi? Ya ake ciki? mene da ke na ci?

tace ga gyada,akwai biscuits,bread,cake etc gasu nan dai,Sohail ya kalleta suka hada ido"
dariya tayi yanda yake leke leke a wajen yana kalle kalle yana sosa gashinsa,"
yace bamu da kudi ne magana ta Allah bamu ci komai ba,ki taimaka ki bamu bashi in na samu zan kawo miki.
budurwar ta kare musu kallo tace guys kamar ku ace baku ci komai ba?
ke karki kara ce mana gayu mu ba gayu bane cewar Sahil yana hade hade rai, Sohail yace bama gane komai ki bamu please

Budurwar ta lula tunanin oganta idan ta bada bashi,haka tayi shahada tace me zan baku a ciki? Sahil yace Cake da lemo da gyada,Sohail yace da bread dinma da wani abubuwan har da biscuits duk zamu ci,Mikewa tayi,amma Sohail har ya bude botikin ya kwaso gyadar da yawan gaske ko irgawa baiyi ba,tace hey dan tsaya mana please.

Leda ta dakko ta dakko bread ya sa hannu zai fisge ta doke masa hannu ya janye hannunsa da sauri ya harare ta, ta zuba musu cake manya biyu,ta zuba musu gyada guda hudu ta dari biyar biyar ta saka musu bread kato slize bread,sai lemo biyu,Sahil yace a kara da yogurt ta saka musu biyu ,sai da ta hada duk abinda suka ce sannan tace da Sohail miko min wayarka"
wayar ya mika mata ta dakko littafi tayi rubutu tace sa hannu a nan,ya karbi biro ya sa hannu tace kuje idan kun kawo kudi sai na baka wayarka.

Ran Sahil ya baci sarkin zuciya yace bata kayanta,Sohail yace kyaleta lets go,suka juya suka tafi abinsu, har sunyi nisa Sahil ya dawo yace da budurwar marar mutunci tare da sa yatsa ya dungure mata kai, ya juya ya tafi abinsa,dariya budurwar tayi kawai tana cewa ikon Allah.

Kayan da suka karba a hannunta sai da suka yi kwana biyu bata ga keyar su ba shi suke ci,sai da ya kare Sohail yace bari naje na karbo mana bashi,Sahil yana gida Sohail ya tafi shi daya,budurwar yau tazo kenan da abincinta a flask cikin wata leda Viva,taga Sohail tace kaine yau? yace ae bashi na dawo ki bani na bar miki wayar tawa ki dinga bani abinci,kallonsa tayi tace wai kai ya sunanka ma? Yace Sohail,tace ina dayan? Yayi mamaki data gane su,yace ta ya kika gane mu? dayan ai yana da wushirya sannan bai son wasa baya fara'a,yace lallai kina da kwakwalwa,amma ta daya kike zuwa a ajinku? dariya tayi,ya sunanki ke? No barshi na sani sunanki Maheera,
A ina ka san sunana? ta furta tana kallonsa,yace bani alawa to na sha,robar alawar ta bude ta bashi daya kyauta,ledar Viva ta mika masa tace dauki kaje gobe ka kawo min flask dina,me zan baka bashi? Sai da yayi tunani sosai sannan yace Yogurt,ya sake lulawa tunani yace cakes,yawwa ehmmm na tuna da lemo,sai da ta gama zubawa yace da biscuits,cike da gajiyawa ta zuba ta bashi ya tafi.

Yana tafiya ta zauna tana mamakin anya kalau suke kuwa? Abinda suke yi sam baiyi kama da na mutane normal ba a shekarun su,sunansa ta nanata "Sohail da Sahil" uhm nice name ta jawo wayarta tana dannawa.

Sohail yana komawa abincin da Maheera ta basu a flask suka bude tuwon shinkafa ne miyar egusi da nama yanka hudu a ciki,gashi tuwon da yawa zai ishe su ma,fara ci suka yi da sauri da sauri yanda suka saba cin abinci basa amfani da spoon yawanci,Sohail yace babar su ta iya girki,da alama makarantar koyon girki tayi,Sahil yace ei ga dadin tsiya ba.
Chapter 5 · 0% Book details