Sashe 35
Mumnunar Dabia Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Islaha kuwa ta gama jera abinci ta manta da lalitar saka kudi ta koma gida ta dauro ta a saman cikinta tana tafiya a hankali ta harde hannayenta a baya tana sanye cikin riga da skert yan kanti da siririn mayafi a kanta,tana tafiya tana walagigi a hanya ga rana,a hankali take tafiya,Hajiya Kulu ce ta iske ta a hanya tace ke Islaha koma gida ki kula da bakin nan da nayi ban san halin su ba kar su dankara min sata.
Daga nan Islaha ta juya gida tana tafiya a hanya tana ta faman tunanin Sahil,tsaki ta ja tace kai bazan iya ba Abuja zan tafi gobe wlh,wayarta ta kalla kamar ta kunna sai ta fasa kawai.
Sahil kuwa har wajen da Islaha take siyar da abinci yaje ba kowa sai Hajiya Kulu,tsayawa yayi a wajen yana ta faman kalle kalle,Hajiya kulu ta kalle shi tace Alhaji wa kake nema ko tambaya kake yi ne? Sahil ba komai kawai ya furta ya juya ya bar wajen.
Kamar ya dora hannu a kai ya kwala ihu haka ya juya gashi ba wani bayani da aka sake masa,Taxi ya shiga ya wuce gidan Alhaji Umaru.
Islaha kuwa shiri tayi tace gwara ma naje can Abuja kawai na huta sai dai kawai su ganni ba zato,zuwa yamma bayan Hajiya Kulu ta dawo Islaha ta sanar mata zata je Abuja gobe,Hajiya Kulu tayi murmushi tace yan mata ba kunya za aje wajen saurayi to idan kinje kun shirya dai ki dawo yafi mutunci ya dinga zuwa zance,Islaha tace ae ai dama.
Bangaren Sahil kuwa yana zuwa gidan Alhaji Umaru a lekki gidane duniya guda Aljannar duniya sai ka bace a gidan sabo da girman gidan,duk wani alatu akwai,iso security ya masa kasancewar an san da zuwansa me gidan ya fada musu.
Har palon Alhaji Umaru katafaren gaske in banda kamshi da sanyi ba abinda ke tashi,Kujera ya nema ya zauna ba kowa a palon sai shi daya,can bayan kamar 5mnt sai yaji karar takalmi me tsini an shigo palon,kallo daya yayiwa wajen yaga wata budurwa ce kyakyawa da ita baka ce amma tana da kyau da diri mashaallah,skin dinta me kyau sosai.
Sanye take cikin wata Jallabiyya fara ta mata wacce ake yayi me tsada ta mata kyau matuka,takalminta da mayafinta black,tayi acuci ta nada,Sahil take ta faman Satar kallo,a ranta tace wow,ban taba ganin me kyan wannan ba tunda nake a duniya,suturar jikinsa ta kalla ta wayance da duba abu a palon kamar tayi mantuwa.
Gyaran gashinsa ta kalla tace ya Allah guy ne wannan na karshe ya iya wanka,dama da irin wannan a duniya?,ko kallonta Sahil baiyi ba,wayarsa ya dauka sabuwa Iphone wacce Sohail ya siya musu,Sohail ya kira a waya ya fada masa sun sauka lafiya,Sohail Alhmdllh film nake kallo sai anjima mayi magana ya kashe wayar tare da maida hankalinsa kan tv..
Maheera ce ta samu rana Sahil yayi tafiya Bum short ta saka da wata matsiyaciyar riga,shine ta fito ta wuce zata je kitchen har tafiya ta canja Sohail a ransa yace sai kace yar American film,fitowa tayi dauke da cup da lemo a ciki,kafin ta karaso ma Sohail yanzu ya saba a jikinsa take zama har ya gyara sai yaga ta zauna a gefensa amma sai da ta dora kanta a kafadarsa yace ai nasan ya zama dole ,Murmushi tayi ta mika masa lemon ya karba tare da furta na gode,Maheera tunawa tayi zata goge kayanta data wanke a washing machine,tashi tayi ta kwaso su ta jona ion,mikewa yayi yace kawo na goge miki.
Bai taba taya ta aiki ba tunda tazo sai yau,suna tsaye a wajen gugar yana ta mata guga a saman abin guga,ta bayansa ta koma ta rungume shi hannayenta ta saman kirjinsa,Sohail yace karki taba min nono na,dariya tayi inda ya saba da halin Maheera har ya gaji ya daina fada kyaleta yake yi,a haka yake mata gugar,sai da ya kusa gamawa yace na gaji karba tayi taci gaba da gogewa ya koma ta bayanta ya rungumeta,dariya tayi tace ai ba cewa nayi ka min ba yace ai na zaci karfi ake karawa na aiki shi yasa na miki ki goge da yawa.
Hannayensa ya maida saman kirjinta Maheera a ranta tace ya fara ganewa,kasa gugar tayi tace na gaji sai anjima a karasa,Sohail ya kalleta yace sannan ya dora bakinsa a kunnenta yace ke dai kice kin kasa ai na zaci ke jaruma ce,ki daina raina ni nasan me akeyi" cizonta yayi kadan a kunne,yar kara tayi tace da zafi fa tana shagwabe fuska dariya suka.
zama suka yi a kujerar dake palo Maheera ta kyale shi ya huta.
Sahil shi dai ko kallon budurwar baiyi ba yanda bata kulashi ba shima haka,wata Babbar mace ce ta shigo sanye cikin kaya na alfarma doguwar riga ce a jikinta yar kasar Dubai,sallama tayi Sahil ya kalleta,zama tayi da fara'a tace sannu da zuwa samari,Sahil da girmamawa ya gaida ta, tace ya hanya barka da zuwa,yace yawwa kawai,Me aiki ta kira tace ta kawo masa abinci da kayan sha,Sahil aka dinga jera masa kayan abinci a gabansa yace Mama ya isa haka,ya daga zuwana za a cutar dani" idan ba so kike cikina ya rude ba wanne zanci wanne zan bari a ciki,Dariyar Hajiya Suwaiba tayi tace duk sai an kawo ka zaba ai,Sahil yace yanzu haka kuma idan ba a cinye ba zubarwa zaku yi ko ga wasu can bayin Allah suna kwana da yunwa,tace ai akwai masu aiki.
Budurwar ta dawo jikin Mamanta ta wani lafe ta zauna ta kwanta a jikinta,Hajiya Suwaiba tace kin gaida bako kuwa? Sai lokacin tace ina yini, Sahil lfy ya furta kawa,sai da Alhaji Umaru ya fito sannan yasa aka raka Sahil dakinsa yace a kai masa abincin can ya huta tukun haka aka yi kuwa,sai bayan yayi wanka yaci abinci sannan zuwa dare ya koma part din Alhaji Umaru.
Washe gari Islaha tana idar da Sallar asubah ta shirya tsaf ta yiwa Hajiya Kulu sallama ta wuce tasha ta hau mota abinta sai Abuja,sai da suka kusa zuwa ma sannan ta kunna wayarta amma bata kira kowa ba,Bangaren Sahil kuwa shi da Alhaji Umaru ya kira shi,da takardu suka zauna duk wacce ya karanta ya fassara sai da yayi sharp sharp,ya cike duk abinda ya dace,Sahil yace to da abaya ne sanda bamu girma haka ba babu abinda zan iya karanta maka,Alhaji Umaru yace sauki ya samu ashe,dariya suka yi.
Washe gari da safe suka karasa aikin nasu Alhaji Umaru yace Sahil kai baza kayi auren ba? Sahil yace zanyi mana watarana,Alhaji Umaru yaji dadi ya furta, kaga 'yata? Yace na ganta wata marar tarbiyya bata da tarbiyya, Alhaji Umaru yace wlh rashin ji ne na yaran zamani ana mata fada daidai gwargwado,Sahil yace bakwa cin ubanta shi yasa ta fi karfinku, ya sunanta ma? Alhaji Umaru yace Amatullah,Sahil yace ai da kun sani Harira kuka saka mata tafi dacewa da sunan,Alhaji Umaru yayi dariya yace ita kadai na haifa a duniya,ina so ta samu tsayayyen namiji me Amana wanda zai tsaya mata ya kula da dukiyarta ko ba raina.
Sahil yana ji yace Allah yasa ka samu me Amanar a zamanin nan,yanzu tsayayyun maza sun kare a duniya sai irinmu lusarai masu matacciyar zuciya,wai dan kar ace ya aure ta,yaci gaba yanzu dan ta'adda mutum daya da zai zare wuka duk guduwa zamuyi,a gaban mutane a gari da rana zaka ga ana kwacen waya da sauran su amma ba me iya katabus sai kallo shi dai tunda ba kansa bala'in ya fada ba babu ruwansa,ai mu yanzu a kasar nan mun koma idan jifa ya wuce kanka to ya fada kan uban kowa, kayi addua kawai Allah ya bata na gari, idan zata ta mike ma ta mike ta kula da dukiyar tata da kanta,what man can do woman can do better,ai yanzu mata ma sun jajirce sun daina kashe zuciyar su,tunda kace har phd ne da ita ai bata da matsala ba sai ta samu miji me kular mata da dukiya ba.
Alhaji Umaru yace ai bata da wayo ne bata san ta duniya ba sam bata san rayuwa ba,Wannan laifinku ne ku kai yar banza kauye a bata horo me tsanani,Alhaji Umaru dariya yayi duk ta inda ya bullo Sahil yana da amsa,gajiya yayi yace kai me zai hana ka aureta wlh zan baka ita,ni na yarda da kai na aminta da kai.
Sahil yace gaskiya kana sona Ogan Daddy,kuma naji dadi,banga wanda ya ganmu ya so mu haka ba, ka bani aiki a halin da nake ciki kuma ka yarda dani,baka kasan waye ni ba kace zaka bani kyakyawar yarka na gode Allah ya saka da Alkhairi amma kayi hakuri wlh ba wai ina kin jininka bane na riga na bawa wata zuciyata yanzu haka tana wajenta babu wacce zan bawa Amatullah, Alhaji Umaru murmushi yayi yace na fahimceka kuma ina maka murna amma namiji ai mijin mace hudu ne,bayan ka auri zabinka zaka iya auren Amatullah ba damuwa,Sahil gumi ya goge yace ni dai Islaha masifaffiya ce baza ta yarda ba gaskiya,bazan ma iya adalci ba,ni bani da adalci,Alhaji Umaru yace kana namijin? Sahil yace ni Azzalumi ne gaskiya zan zalunci yarka,kawai a bata wani ba tsayayye bane ni.
Daga nan Islaha ta juya gida tana tafiya a hanya tana ta faman tunanin Sahil,tsaki ta ja tace kai bazan iya ba Abuja zan tafi gobe wlh,wayarta ta kalla kamar ta kunna sai ta fasa kawai.
Sahil kuwa har wajen da Islaha take siyar da abinci yaje ba kowa sai Hajiya Kulu,tsayawa yayi a wajen yana ta faman kalle kalle,Hajiya kulu ta kalle shi tace Alhaji wa kake nema ko tambaya kake yi ne? Sahil ba komai kawai ya furta ya juya ya bar wajen.
Kamar ya dora hannu a kai ya kwala ihu haka ya juya gashi ba wani bayani da aka sake masa,Taxi ya shiga ya wuce gidan Alhaji Umaru.
Islaha kuwa shiri tayi tace gwara ma naje can Abuja kawai na huta sai dai kawai su ganni ba zato,zuwa yamma bayan Hajiya Kulu ta dawo Islaha ta sanar mata zata je Abuja gobe,Hajiya Kulu tayi murmushi tace yan mata ba kunya za aje wajen saurayi to idan kinje kun shirya dai ki dawo yafi mutunci ya dinga zuwa zance,Islaha tace ae ai dama.
Bangaren Sahil kuwa yana zuwa gidan Alhaji Umaru a lekki gidane duniya guda Aljannar duniya sai ka bace a gidan sabo da girman gidan,duk wani alatu akwai,iso security ya masa kasancewar an san da zuwansa me gidan ya fada musu.
Har palon Alhaji Umaru katafaren gaske in banda kamshi da sanyi ba abinda ke tashi,Kujera ya nema ya zauna ba kowa a palon sai shi daya,can bayan kamar 5mnt sai yaji karar takalmi me tsini an shigo palon,kallo daya yayiwa wajen yaga wata budurwa ce kyakyawa da ita baka ce amma tana da kyau da diri mashaallah,skin dinta me kyau sosai.
Sanye take cikin wata Jallabiyya fara ta mata wacce ake yayi me tsada ta mata kyau matuka,takalminta da mayafinta black,tayi acuci ta nada,Sahil take ta faman Satar kallo,a ranta tace wow,ban taba ganin me kyan wannan ba tunda nake a duniya,suturar jikinsa ta kalla ta wayance da duba abu a palon kamar tayi mantuwa.
Gyaran gashinsa ta kalla tace ya Allah guy ne wannan na karshe ya iya wanka,dama da irin wannan a duniya?,ko kallonta Sahil baiyi ba,wayarsa ya dauka sabuwa Iphone wacce Sohail ya siya musu,Sohail ya kira a waya ya fada masa sun sauka lafiya,Sohail Alhmdllh film nake kallo sai anjima mayi magana ya kashe wayar tare da maida hankalinsa kan tv..
Maheera ce ta samu rana Sahil yayi tafiya Bum short ta saka da wata matsiyaciyar riga,shine ta fito ta wuce zata je kitchen har tafiya ta canja Sohail a ransa yace sai kace yar American film,fitowa tayi dauke da cup da lemo a ciki,kafin ta karaso ma Sohail yanzu ya saba a jikinsa take zama har ya gyara sai yaga ta zauna a gefensa amma sai da ta dora kanta a kafadarsa yace ai nasan ya zama dole ,Murmushi tayi ta mika masa lemon ya karba tare da furta na gode,Maheera tunawa tayi zata goge kayanta data wanke a washing machine,tashi tayi ta kwaso su ta jona ion,mikewa yayi yace kawo na goge miki.
Bai taba taya ta aiki ba tunda tazo sai yau,suna tsaye a wajen gugar yana ta mata guga a saman abin guga,ta bayansa ta koma ta rungume shi hannayenta ta saman kirjinsa,Sohail yace karki taba min nono na,dariya tayi inda ya saba da halin Maheera har ya gaji ya daina fada kyaleta yake yi,a haka yake mata gugar,sai da ya kusa gamawa yace na gaji karba tayi taci gaba da gogewa ya koma ta bayanta ya rungumeta,dariya tayi tace ai ba cewa nayi ka min ba yace ai na zaci karfi ake karawa na aiki shi yasa na miki ki goge da yawa.
Hannayensa ya maida saman kirjinta Maheera a ranta tace ya fara ganewa,kasa gugar tayi tace na gaji sai anjima a karasa,Sohail ya kalleta yace sannan ya dora bakinsa a kunnenta yace ke dai kice kin kasa ai na zaci ke jaruma ce,ki daina raina ni nasan me akeyi" cizonta yayi kadan a kunne,yar kara tayi tace da zafi fa tana shagwabe fuska dariya suka.
zama suka yi a kujerar dake palo Maheera ta kyale shi ya huta.
Sahil shi dai ko kallon budurwar baiyi ba yanda bata kulashi ba shima haka,wata Babbar mace ce ta shigo sanye cikin kaya na alfarma doguwar riga ce a jikinta yar kasar Dubai,sallama tayi Sahil ya kalleta,zama tayi da fara'a tace sannu da zuwa samari,Sahil da girmamawa ya gaida ta, tace ya hanya barka da zuwa,yace yawwa kawai,Me aiki ta kira tace ta kawo masa abinci da kayan sha,Sahil aka dinga jera masa kayan abinci a gabansa yace Mama ya isa haka,ya daga zuwana za a cutar dani" idan ba so kike cikina ya rude ba wanne zanci wanne zan bari a ciki,Dariyar Hajiya Suwaiba tayi tace duk sai an kawo ka zaba ai,Sahil yace yanzu haka kuma idan ba a cinye ba zubarwa zaku yi ko ga wasu can bayin Allah suna kwana da yunwa,tace ai akwai masu aiki.
Budurwar ta dawo jikin Mamanta ta wani lafe ta zauna ta kwanta a jikinta,Hajiya Suwaiba tace kin gaida bako kuwa? Sai lokacin tace ina yini, Sahil lfy ya furta kawa,sai da Alhaji Umaru ya fito sannan yasa aka raka Sahil dakinsa yace a kai masa abincin can ya huta tukun haka aka yi kuwa,sai bayan yayi wanka yaci abinci sannan zuwa dare ya koma part din Alhaji Umaru.
Washe gari Islaha tana idar da Sallar asubah ta shirya tsaf ta yiwa Hajiya Kulu sallama ta wuce tasha ta hau mota abinta sai Abuja,sai da suka kusa zuwa ma sannan ta kunna wayarta amma bata kira kowa ba,Bangaren Sahil kuwa shi da Alhaji Umaru ya kira shi,da takardu suka zauna duk wacce ya karanta ya fassara sai da yayi sharp sharp,ya cike duk abinda ya dace,Sahil yace to da abaya ne sanda bamu girma haka ba babu abinda zan iya karanta maka,Alhaji Umaru yace sauki ya samu ashe,dariya suka yi.
Washe gari da safe suka karasa aikin nasu Alhaji Umaru yace Sahil kai baza kayi auren ba? Sahil yace zanyi mana watarana,Alhaji Umaru yaji dadi ya furta, kaga 'yata? Yace na ganta wata marar tarbiyya bata da tarbiyya, Alhaji Umaru yace wlh rashin ji ne na yaran zamani ana mata fada daidai gwargwado,Sahil yace bakwa cin ubanta shi yasa ta fi karfinku, ya sunanta ma? Alhaji Umaru yace Amatullah,Sahil yace ai da kun sani Harira kuka saka mata tafi dacewa da sunan,Alhaji Umaru yayi dariya yace ita kadai na haifa a duniya,ina so ta samu tsayayyen namiji me Amana wanda zai tsaya mata ya kula da dukiyarta ko ba raina.
Sahil yana ji yace Allah yasa ka samu me Amanar a zamanin nan,yanzu tsayayyun maza sun kare a duniya sai irinmu lusarai masu matacciyar zuciya,wai dan kar ace ya aure ta,yaci gaba yanzu dan ta'adda mutum daya da zai zare wuka duk guduwa zamuyi,a gaban mutane a gari da rana zaka ga ana kwacen waya da sauran su amma ba me iya katabus sai kallo shi dai tunda ba kansa bala'in ya fada ba babu ruwansa,ai mu yanzu a kasar nan mun koma idan jifa ya wuce kanka to ya fada kan uban kowa, kayi addua kawai Allah ya bata na gari, idan zata ta mike ma ta mike ta kula da dukiyar tata da kanta,what man can do woman can do better,ai yanzu mata ma sun jajirce sun daina kashe zuciyar su,tunda kace har phd ne da ita ai bata da matsala ba sai ta samu miji me kular mata da dukiya ba.
Alhaji Umaru yace ai bata da wayo ne bata san ta duniya ba sam bata san rayuwa ba,Wannan laifinku ne ku kai yar banza kauye a bata horo me tsanani,Alhaji Umaru dariya yayi duk ta inda ya bullo Sahil yana da amsa,gajiya yayi yace kai me zai hana ka aureta wlh zan baka ita,ni na yarda da kai na aminta da kai.
Sahil yace gaskiya kana sona Ogan Daddy,kuma naji dadi,banga wanda ya ganmu ya so mu haka ba, ka bani aiki a halin da nake ciki kuma ka yarda dani,baka kasan waye ni ba kace zaka bani kyakyawar yarka na gode Allah ya saka da Alkhairi amma kayi hakuri wlh ba wai ina kin jininka bane na riga na bawa wata zuciyata yanzu haka tana wajenta babu wacce zan bawa Amatullah, Alhaji Umaru murmushi yayi yace na fahimceka kuma ina maka murna amma namiji ai mijin mace hudu ne,bayan ka auri zabinka zaka iya auren Amatullah ba damuwa,Sahil gumi ya goge yace ni dai Islaha masifaffiya ce baza ta yarda ba gaskiya,bazan ma iya adalci ba,ni bani da adalci,Alhaji Umaru yace kana namijin? Sahil yace ni Azzalumi ne gaskiya zan zalunci yarka,kawai a bata wani ba tsayayye bane ni.