Sashe 38
Mumnunar Dabia Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sai da ya gama ya fito idonsa har ya canja yayi ja sabo da masifarsa ta kalle shi ba kaya,Maheera ta kalle shi ya dalla mata harara sai huci yake shi kadai,tace Sohail ni fa matarka ce, baka san me akeyi ba idan anyi aure? A haka zamu rayu kenan? tsaki ya ja tare da nuna ta da yatsa yace dan kawai kece amma duk ranar da kika min haka ko da wasa wlh sai kin gane duniyar nan juyawa take,Maheera ta zaro ido tace duk akan na kalleka kana wanka? An kalleka to wlh zan cire wannan towel din naga yanda zaka yi,Sohail yace da kuwa kin kwana a bayan Uwarki yau,Uwata fa kace ke kika jawo koma mene ai, ya sake jan tsaki ya juya yana shiryawa,Maheera ta dade a tsaye sannan ta bawa zuciyarta hakuri da ta tuna yanda suke,Wanka ta shiga ta fito yana ta shafa turare ya sanya 3qtr da riga armless yana ta fushi fuska ba rahma.
Maheera tana satar kallonsa tsokanarsa tayi tace Sweet goyani,wani mugun kallon ya mata,dariya tayi tace to na hakura shafa min mai yau daya dai,bai kula ta ba uzurinsa yake,bayansa ta tako ta tsaya tace haba Sweet ka manta aurena fa kayi,zamanka nake yi sabo da kai nazo nan nake zaune,na rabu da iyayena da kowa nawa na yarda na dawo wajenka,ka manta ni me shago ce fa,baki ya turo da shagwaba yace ai kece bakya ji na fada miki bana so,to na daina I'm sorry Sweet,rungume shi tayi daga ita sai towel, murmushi yayi ka fasa saka min bra din? yace ke wasa nake miki ina ni ina kallon wannan chamber taki,dariya tayi tace to jira na shirya sai ka dauke ni ka goyani,daga na miki sau biyu ke baki san kadan ba,dan Allah ta marairai ce masa,Okay to shirya,wayarsa ce tayi kara ya duba da sauri yaga a wajen aiki ne aka sake kara masa matsayi,ihu yayi yace kinga an kara min girma yanzu, Maheera murna tayi ta rungume shi suna ta murna,ya sake duba wayar yace tayani karanta turancin nan ance naje gobe zamu tafi Meeting rivers state ko?,Maheera tace Alhmdllh I'm so Happy,zamu kara zama masu kudi,Dama Oga yace yanzu indai aka canja min matsayi to babu zama kuma kullum tafiye tafiye zan dinga yi,Maheera ta dan ji damm sabo da ita ta saba da mijinta kullum suna tare suna kula da juna sannan so take a hankali ta dan ganar da shi yanda ake soyayyar aure ko Allah zai sa ya gane.
Islaha sai da su Maheera suka fito sannan suka samu labarin,Murna suka tayasu sosai,Sahil yafi kowa murna gashi shima zai fara nasa.
Maheera tace ke Islaha kece kika sha hanya kizo ga abinci fatan kuma kin kira Hajiya kulu,Na kira ta na fada mata muna tare.
Dining suka zauna Sahil yace shi bazai ci tuwo ba,Maheera tace amma sai ka fada min tun dazu na maka wani abin,Sohail yace yanzu ma ai tashi zaki yi ki masa ko da yunwa zaki bar min shi? Sahil yace Jullof din taliya zaki min da kifi,Maheera ba musu ta mike Islaha tace zauna naje nayi masa,Sahil yace ke kina da aure ne? Bana son ki dinga shiga hurumin da ba naki ba,aikin matar aure sai matar aure,mu yanzu muna da mata girki sai na me aure idan baki da aure kawai ke kazama ce.
Maheera haka ta shiga kitchen ta masa nasa ta kawo masa yace yawwa Sohail sa mata Albarka,Sohail yace Allah miki Albarka Allah yasa ki haifo min yan biyu,Maheera harda cewa ameen da sauri,yace taki ma samun cikin har yanzu shuru,Islaha dariya tayi a ranta tana jinjinawa Maheera da zaman auren nan yaki mata ciki yace itace taki samu.
A boye Maheera tace dan Allah Islaha kiyi sauri a daura muku aure ko na samu sauki da twins ki daure ki janye min dayan ki rage min,Islaha tace bai ce ba zance yazo aure ni ne.
Washe gari Sohail da sassafe suka yi Sallama yabi flight suka wuce,Sahil ne ya kaishi airport din tare da Alhaji Saminu suka tafi sabo Sohail sai ana sasu a hanya.
Kwanan Islaha daya tal a gidan Hajiya kulu ta kira tace ya kamata fa ki dawo gobe tunda kin ganshi idan sonki yake yaje ya kai kudin aure danginki,bata yi musu ba tace to zan dawo Inshaallah,Sahil yana ji ya fito yace naji kamar kina cewa gobe zaki koma lagos,ae haka Hajiya Kulu tace,kamar abin kirki yace kira min ita muyi magana,Kiran Hajiya kulu tayi a waya tace ga Sahil zaku gaisa,ya karba bayan sun gaisa yace wai yarki ce Islaha? tace a'a Allah ne ya hadamu to na raba ku,dan Allah ki kyaleta ta sarara,Hajiya kulu tace kaji yaro dan ubanka sanda ka koreta waye ya riketa,ai ni sirikarka ce,Sahil yace sirikita tana kushewa ta rasu bani da wata sirika,dama ni haka nake so ba ruwana da kunya ki zare min ido nima zare miki zanyi,Hajiya Kulu tun a nan tace Islaha zata yi babban ganganci da rayuwarta yanzu wannan zata aura shi yasa tace ba normal yake ba,ai kuwa zata yi kuka da idonta watarana.
Sahil tuni ya kashe wayar yace sai dai ki jira Sohail ya dawo mu tafi kauyenku da yan uwan Daddy a kai kudi,Islaha tace wlh baza su daura ba Ibrahim zasu bani,Sahil yace zasu daura ki kyale su dai dai muke da su,Islaha tace to shike nan,Amma baka kyauta ba da ka yiwa Hajiya Kulu haka ka bata hakuri,Tunani ya lula yace sai kuma naga ban kyauta ba,sake kiranta to,Islaha ta sake kira tace dan Allah Hajiya kiyi hakuri,Hajiya kulu tace na fahimta ai karki damu Islaha,Wayar ya karba yace kiyi hakuri naga ban kyauta ba zanyi hakuri na kalle ki a sirikata watarana idan ta kama
Hajiya Kulu ta jinjina kai tace ba komai na gode ta kashe wayar tace tab a haka yarinyar nan zata kai kanta.
Maheera ita bakuwa tayi tana can tare da kawarta ce tazo Sadiya,suna zaune a bedroom,Sadiya tace Maheera wani zance naji ance wai mijinki mahaukaci ne? ance basu da hankali gaba dayansu,ana ta gulmar a gari, Maheera fuska ta bata tace nifa bana son munafunci kizo har gidana kice da mijina mahaukaci,munafukar banza indai wannan ne ya kawo ki tashi ki bar min gida,Sadiya tace daga fadar gaskiya,Islaha tana palo tare da Sahil taga ya jawo belt a jikin wandonsa ya boye a bayansa ya mike ya tare kofar palo ta fita.
Sadiya ce ta fito zata tafi sum sum Sahil ya tare hanya yace munafuka to naji duk abinda kika ce,wato mu mahaukata ne,ke ubanki mene bayayi naga chacha yake yi tun yana matashi yake chacha har yanzu bai daina ba,shine kika taho munafunci gidan masu aure zaki rusa musu aure dama haka kuke yi kuna ziga mutane,Sadiya Tsoro taji tace kayi hakuri,bazan hakura ba cewar Sahil,mijinta yana can ya tafi nema kinzo kina munafunci zaki ziga masa mata,Belt dinsa ya fito da ita nan take ya zugawa Sadiya daya,ta saki ihu kafin ta shanye ya kara mata,yace gobe kya kuma zuwa gulma gidan wasu yaci gaba da zuba mata belt ta ko ina tana ihu tana rokonsa, gashi ya tare hanyar fita,da kyar Islaha ta bude mata kofa ta fice da gudu ya taka zai bita Islaha ta rike shi tana dariya,Maheera ma data fito dariya take tace wlh ka birgeni,yace ai laifin ki ne da jaye jaye.
Tunda Sohail ya tafi sam ko time din waya baya samu,Maheera duk ta damu kanta ita ya daina sonta,gashi har an kwashe 5days bai dawo ba,sai a kwana na shida ya dawo yana dawowa yace zasu tafi Dubai next week,Maheera ta fashe da kuka wiwi a bedroom,Sohail ya fito daga wanka yace menene Sweet? Me ya faru?
Ni wallahi wannan kudin ya ishe mu rayuwa me ake bukata ga gidan zama kana aikinka daidai misali,muna ci muna koshi Alhmdllh yanzu ace wannan bai isa ba,shike nan an dauke min mijina waya ma ta gagara,kana can zaka dinga yawo a gari mata shike nan daga nan wata ta ganka ni na shiga uku na lalace.
Sohail yace kwantar da hankalinki Sweet kince zamu haihu wannan kudin fa mu nake nemawa neman da nake yi dan wa nake yi? Shekara da shekaru tunda muka taso a bauta muke da wahala ana neman aiki sanadinki na samu aiki gashi munyi aure to mene dan an kara nema wasu kudin sabo da rayuwar gaba mu samu muji dadi da yaran da zamu haifa gaba,Maheera tana kuka ta sakko kasa ta zauna zaman dirshan ta cire dankwali ta jefar,gashinta da ya sha gyara yana sheki ya bayyana,tana ni dan Allah ka hakura wannan ya ishe mu muna zaman mu kullum ni bana so kayi nisa,okay...okay...to nace kayi min ciki na samu na cika gidan nan da yara idan ina ganin yarana ko zaka yi tafiya bazan damu sosai ba,kace ba yanzu ba na rasa inda kasa gaba tsakani da Allah ko tabani baka yi kuma shine dan kulawar ma yanzu ka samu canji sai dai kasashen waje wallahi Allah ni bana so dan Allah ka tausaya min ,Kafafunsa ta rike tana kuka,Sohail ya tsaya yana kallon ikon Allah ta haukace gaba daya.
Yace na dade ina ji ana cewa muna da aljanu ashe ba mu kadai bane,yanzu daga tafiya sau daya? Wasu matan mazajen fa wasu sai su kwashe 6months basu zo gida ba kuma suka hakura,mikewa tayi tsaye ta rirrike shi ni bazan iya ba,ba irinsu bace ni na saba da mijina kullum muna tare sai dai a barni ni kadai dan Allah ni wannan aikin kwai jaraba zai rabani da mijina Allah ya isa tsakanina da Alhaji Saminu.
Maheera tana satar kallonsa tsokanarsa tayi tace Sweet goyani,wani mugun kallon ya mata,dariya tayi tace to na hakura shafa min mai yau daya dai,bai kula ta ba uzurinsa yake,bayansa ta tako ta tsaya tace haba Sweet ka manta aurena fa kayi,zamanka nake yi sabo da kai nazo nan nake zaune,na rabu da iyayena da kowa nawa na yarda na dawo wajenka,ka manta ni me shago ce fa,baki ya turo da shagwaba yace ai kece bakya ji na fada miki bana so,to na daina I'm sorry Sweet,rungume shi tayi daga ita sai towel, murmushi yayi ka fasa saka min bra din? yace ke wasa nake miki ina ni ina kallon wannan chamber taki,dariya tayi tace to jira na shirya sai ka dauke ni ka goyani,daga na miki sau biyu ke baki san kadan ba,dan Allah ta marairai ce masa,Okay to shirya,wayarsa ce tayi kara ya duba da sauri yaga a wajen aiki ne aka sake kara masa matsayi,ihu yayi yace kinga an kara min girma yanzu, Maheera murna tayi ta rungume shi suna ta murna,ya sake duba wayar yace tayani karanta turancin nan ance naje gobe zamu tafi Meeting rivers state ko?,Maheera tace Alhmdllh I'm so Happy,zamu kara zama masu kudi,Dama Oga yace yanzu indai aka canja min matsayi to babu zama kuma kullum tafiye tafiye zan dinga yi,Maheera ta dan ji damm sabo da ita ta saba da mijinta kullum suna tare suna kula da juna sannan so take a hankali ta dan ganar da shi yanda ake soyayyar aure ko Allah zai sa ya gane.
Islaha sai da su Maheera suka fito sannan suka samu labarin,Murna suka tayasu sosai,Sahil yafi kowa murna gashi shima zai fara nasa.
Maheera tace ke Islaha kece kika sha hanya kizo ga abinci fatan kuma kin kira Hajiya kulu,Na kira ta na fada mata muna tare.
Dining suka zauna Sahil yace shi bazai ci tuwo ba,Maheera tace amma sai ka fada min tun dazu na maka wani abin,Sohail yace yanzu ma ai tashi zaki yi ki masa ko da yunwa zaki bar min shi? Sahil yace Jullof din taliya zaki min da kifi,Maheera ba musu ta mike Islaha tace zauna naje nayi masa,Sahil yace ke kina da aure ne? Bana son ki dinga shiga hurumin da ba naki ba,aikin matar aure sai matar aure,mu yanzu muna da mata girki sai na me aure idan baki da aure kawai ke kazama ce.
Maheera haka ta shiga kitchen ta masa nasa ta kawo masa yace yawwa Sohail sa mata Albarka,Sohail yace Allah miki Albarka Allah yasa ki haifo min yan biyu,Maheera harda cewa ameen da sauri,yace taki ma samun cikin har yanzu shuru,Islaha dariya tayi a ranta tana jinjinawa Maheera da zaman auren nan yaki mata ciki yace itace taki samu.
A boye Maheera tace dan Allah Islaha kiyi sauri a daura muku aure ko na samu sauki da twins ki daure ki janye min dayan ki rage min,Islaha tace bai ce ba zance yazo aure ni ne.
Washe gari Sohail da sassafe suka yi Sallama yabi flight suka wuce,Sahil ne ya kaishi airport din tare da Alhaji Saminu suka tafi sabo Sohail sai ana sasu a hanya.
Kwanan Islaha daya tal a gidan Hajiya kulu ta kira tace ya kamata fa ki dawo gobe tunda kin ganshi idan sonki yake yaje ya kai kudin aure danginki,bata yi musu ba tace to zan dawo Inshaallah,Sahil yana ji ya fito yace naji kamar kina cewa gobe zaki koma lagos,ae haka Hajiya Kulu tace,kamar abin kirki yace kira min ita muyi magana,Kiran Hajiya kulu tayi a waya tace ga Sahil zaku gaisa,ya karba bayan sun gaisa yace wai yarki ce Islaha? tace a'a Allah ne ya hadamu to na raba ku,dan Allah ki kyaleta ta sarara,Hajiya kulu tace kaji yaro dan ubanka sanda ka koreta waye ya riketa,ai ni sirikarka ce,Sahil yace sirikita tana kushewa ta rasu bani da wata sirika,dama ni haka nake so ba ruwana da kunya ki zare min ido nima zare miki zanyi,Hajiya Kulu tun a nan tace Islaha zata yi babban ganganci da rayuwarta yanzu wannan zata aura shi yasa tace ba normal yake ba,ai kuwa zata yi kuka da idonta watarana.
Sahil tuni ya kashe wayar yace sai dai ki jira Sohail ya dawo mu tafi kauyenku da yan uwan Daddy a kai kudi,Islaha tace wlh baza su daura ba Ibrahim zasu bani,Sahil yace zasu daura ki kyale su dai dai muke da su,Islaha tace to shike nan,Amma baka kyauta ba da ka yiwa Hajiya Kulu haka ka bata hakuri,Tunani ya lula yace sai kuma naga ban kyauta ba,sake kiranta to,Islaha ta sake kira tace dan Allah Hajiya kiyi hakuri,Hajiya kulu tace na fahimta ai karki damu Islaha,Wayar ya karba yace kiyi hakuri naga ban kyauta ba zanyi hakuri na kalle ki a sirikata watarana idan ta kama
Hajiya Kulu ta jinjina kai tace ba komai na gode ta kashe wayar tace tab a haka yarinyar nan zata kai kanta.
Maheera ita bakuwa tayi tana can tare da kawarta ce tazo Sadiya,suna zaune a bedroom,Sadiya tace Maheera wani zance naji ance wai mijinki mahaukaci ne? ance basu da hankali gaba dayansu,ana ta gulmar a gari, Maheera fuska ta bata tace nifa bana son munafunci kizo har gidana kice da mijina mahaukaci,munafukar banza indai wannan ne ya kawo ki tashi ki bar min gida,Sadiya tace daga fadar gaskiya,Islaha tana palo tare da Sahil taga ya jawo belt a jikin wandonsa ya boye a bayansa ya mike ya tare kofar palo ta fita.
Sadiya ce ta fito zata tafi sum sum Sahil ya tare hanya yace munafuka to naji duk abinda kika ce,wato mu mahaukata ne,ke ubanki mene bayayi naga chacha yake yi tun yana matashi yake chacha har yanzu bai daina ba,shine kika taho munafunci gidan masu aure zaki rusa musu aure dama haka kuke yi kuna ziga mutane,Sadiya Tsoro taji tace kayi hakuri,bazan hakura ba cewar Sahil,mijinta yana can ya tafi nema kinzo kina munafunci zaki ziga masa mata,Belt dinsa ya fito da ita nan take ya zugawa Sadiya daya,ta saki ihu kafin ta shanye ya kara mata,yace gobe kya kuma zuwa gulma gidan wasu yaci gaba da zuba mata belt ta ko ina tana ihu tana rokonsa, gashi ya tare hanyar fita,da kyar Islaha ta bude mata kofa ta fice da gudu ya taka zai bita Islaha ta rike shi tana dariya,Maheera ma data fito dariya take tace wlh ka birgeni,yace ai laifin ki ne da jaye jaye.
Tunda Sohail ya tafi sam ko time din waya baya samu,Maheera duk ta damu kanta ita ya daina sonta,gashi har an kwashe 5days bai dawo ba,sai a kwana na shida ya dawo yana dawowa yace zasu tafi Dubai next week,Maheera ta fashe da kuka wiwi a bedroom,Sohail ya fito daga wanka yace menene Sweet? Me ya faru?
Ni wallahi wannan kudin ya ishe mu rayuwa me ake bukata ga gidan zama kana aikinka daidai misali,muna ci muna koshi Alhmdllh yanzu ace wannan bai isa ba,shike nan an dauke min mijina waya ma ta gagara,kana can zaka dinga yawo a gari mata shike nan daga nan wata ta ganka ni na shiga uku na lalace.
Sohail yace kwantar da hankalinki Sweet kince zamu haihu wannan kudin fa mu nake nemawa neman da nake yi dan wa nake yi? Shekara da shekaru tunda muka taso a bauta muke da wahala ana neman aiki sanadinki na samu aiki gashi munyi aure to mene dan an kara nema wasu kudin sabo da rayuwar gaba mu samu muji dadi da yaran da zamu haifa gaba,Maheera tana kuka ta sakko kasa ta zauna zaman dirshan ta cire dankwali ta jefar,gashinta da ya sha gyara yana sheki ya bayyana,tana ni dan Allah ka hakura wannan ya ishe mu muna zaman mu kullum ni bana so kayi nisa,okay...okay...to nace kayi min ciki na samu na cika gidan nan da yara idan ina ganin yarana ko zaka yi tafiya bazan damu sosai ba,kace ba yanzu ba na rasa inda kasa gaba tsakani da Allah ko tabani baka yi kuma shine dan kulawar ma yanzu ka samu canji sai dai kasashen waje wallahi Allah ni bana so dan Allah ka tausaya min ,Kafafunsa ta rike tana kuka,Sohail ya tsaya yana kallon ikon Allah ta haukace gaba daya.
Yace na dade ina ji ana cewa muna da aljanu ashe ba mu kadai bane,yanzu daga tafiya sau daya? Wasu matan mazajen fa wasu sai su kwashe 6months basu zo gida ba kuma suka hakura,mikewa tayi tsaye ta rirrike shi ni bazan iya ba,ba irinsu bace ni na saba da mijina kullum muna tare sai dai a barni ni kadai dan Allah ni wannan aikin kwai jaraba zai rabani da mijina Allah ya isa tsakanina da Alhaji Saminu.