Sashe 23
Mumnunar Dabia Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sohail yace ba gaki ba,ka taba ce min you love me ne da zaka kace nice....to I love you Sohail ya furta da sauri kafin ta rufe baki,Sahil dinfa ko kaine zaka yi auren ka rigashi sabo da kai kayi kudi? to ba Allah ne yace ayi ba tunda bashi da budurwa a kasa ba shike nan ba,a'a a daura dai auren tare ku aure ni ku biyu kawai ai kunce na ishe ku ko?
Kaga sai a raba muku kwana yau kai kazo mu kwana tare gobe Sahil yazo,Sohail yace ai kuwa da an rataye Sahil anyi hanging dinsa kawai an huta, yarinya na sani to namiji daya shi yake auren mata hudu mace namiji daya tal take aura.
To yanzu mata hudun zaka yi kenan? Sohail yace to a Office tv dina naji wa'azin Allah ne yace malam yace a taimaki mata sunyi yawa a gari idan da hali mutum yayi ta karawa har su kai hudu,kinga kece uwargida zan miki wannan alfarmar na aureki a farko daga baya sai a karo miki ta biyu a haka har na cike hudu na,Yan mata hudu rigis ni kadai gaskiya mun muku wayo mu.
Maheera tace wanne malami ne yayi wannan wa'azin? ban sanshi ba channel din a tv din Office dina take,Maheera a ranta tace dole na kira Alhaji Saminu a tsinke wannan Channel,ina so ya dinga jin wa'azi amma banda na kishiya,inda baida kai ai sai yace sai yayi, sai ya aure su.
Maheera tace Sohail ba haka malamin yake nufi ba,nufinsa idan mutum zai iya adalci kuma yana da kudi sosai,Sai zai iya adalci aka ce idan bazai iya ba yayi zamansa da guda dayarsa,Sohail yace aya da hadisi ya kawo to Hajiya.
Maheera tace uhmm ai shike nan yace ae ga kuma Hurul ayni yace na lahira suna can a lahira suna jirana gaskiya mun gama da ku mata kuyi hakuri 10-0 kawai.
Dariya ya bawa Maheera tace ashe kai mayen mata ne ban sani ba,daga kaga ka fara kudi shine ka fara zancen mata,Adnan shi da matarsa daya ta ishe shi abinsa gwanin sha'awa kai da mamanku take baturiya baka gaji halin turawa ba mace daya danginku suke yi,Sohail yace ni nasan wata mama ne ina ruwana da su.
Yaushe zaki tafi gidanku? Maheera tace ina nan bazan tafi ba,aikina zanyi,Sohail yace shike nan ki ta zama tunda ke bakya son ci gaba,tace ae naji mutumin da zaiyi mata hudu waye zai dogara da shi jeka can da matanka bada Maheera ba.
Maman su Maheera aka kwantar a asibiti ciwonta ya tashi,kannen Maheera ne suka kaita asibiti sai da suka kwana kudinsu ya kare sannan suka kira Maheera,tare da sanar mata.
Sohail kuma ya rigata sanin ma an kai Mama asibiti yau aljanun sun waiwayo,Zuwa yayi har asibitin ya dubata su Juwairiyya basu sanshi ba sai kallonsa suke yi,ya tambayi kudin nawa zasu biya? Suka ce dubu dari biyu da hamsim mun biya dubu hamsim,dubu hamsim dinsu ya basu yaje ya biya kudin komai da komai da duk wani magunguna da ake bukata masu tsada ya siya mata da yawa aka siya wanda zai dade bai kare ba.
Abincin masu ciwon sugar daban haka yasa aka masa list duk ya siyowa Mama,komai naci sai da ya siyo har na kannen Maheera abinda zasu ci lemuka da fruits da kayan shayi etc sai kudi ya basu yace ga wannan ku rike idan zaku siyi abinci,Suka ce mun gode.
Ammar yace dan Allah waye kai? Sohail yace sunana Sohail idan Maheera tazo ku fada mata ta sanni,suka ce to an gode.
Yana tafiya Maheera taje asibitin ko zama bata yi ba tace ya jikin maman? Bacci take tun rana,me suka ce za a biya?
Wani yazo ya biya komai kalli abinda ya siyo yace sunansa Sohail,kawai ganinsa muka yi yazo, Juwairiyya tace Aunty wani kyakyawa ne wlh,Sahil ne ya shigo kamar ana fada musu,Ammar yace yawwa gashi ma ya dawo,basu gane ba Sohail bane,ita kanta Maheera sai da yayi magana taga wushiyarsa yar karama ta gane Sahil ne.
Tace dan uwansa ne fa ba shi bane wannan Sahil ne waccen Sohail,Su Ammar suka ce ikon Allah basu da banbanci,Sahil zuwa yayi ya ja kujera ya zauna ya tambaya ya jikin Maman? tace da sauki,Su Ammar suka gaida shi yayi musu ya me jiki.
Sahil harda cewa kaiii Mama tana jin jiki wannan kibar tata bata Allah bace ciwon ne ya hura ta karku dauka jin dadi ne yasa tayi kiba haka, suka ce ae haka likita yace,Allah ya bata lafiya ya furta,20k ya basu yace sa suyi wani abun,suka ce kaima sai ka bamu?
Yace ya zanyi Sohail yace na baku ba yin kaina bane Sohail ne ya min dole yace lallai na baku,ba wani kudi ne da mu ba rufin asirin Allah ne,Maheera ta boye dariyarta tace to mun gode ka gaida gida,yace a'a sai kace mahaukaci zance gida ance ana gaisheka gida ba mutum ba ba komai ba kice na gaishe shi bazan yi ba ya fice yana cewa Mama Allah ya baki lafiya kiba haka kamar ta jin dadi kai ciwo da wuya yake,sai kace kibar sihiri kafafu tutum tutum haka.
England
Wata dattijuwa ce zaune a garden din gidanta tare da wani tsohon bature Halley Maman su Sohail,Mijinta ta kalla Ivan,cikin harshen turanci tace ina so zanje Nigeria zuwa nan da wata uku,tun daga yarana dana bada su na zaci idan nayi aure zan sake haihuwa ban sake haihuwa ba tunda na aure ka wanda a baya ina da kuruciya bani da aiki sai club da holewa na sa a gaba,yaro na daya bashi da lafiya suka dameni na bawa ubansu shi ya sake ni,yanzu ni nasan nayi kuskure suna can sun zama musulmai,bana so kuma su kasance musulmai gaskiya,bana son musulunci,bayan haka yanzu basu sanni ba ina bukatar yarana su sanni na jasu a jiki.
Na nemi ubansu rannan da kyar na samu number dinsa wajen abokinsa Harry na kira yana ji nice ya kashe wayarsa,yanzu Nigeria zan tafi na ja yarana a jikina su san wace ni tunda ban haifi wasu ba.
Mijinta Ivan yace kinyi ganganci kuma baki yi daidai ba,yanzu baza su saurare ki ba,baza ki iya canja musu addini ba,indai hakane Halley har yanzu to baki hankali ba,na zaci ma zaki ce bari kije ki basu hakuri su karbe ki a matsayin uwa amma ke ta addini kike yi,sannan kuma tunda baki haifi wasu ba shine zaki neme su,yaran naki kisan da marar lafiya baki tausaya musu ba,baki da hankali Ivan ya mike ya wuce ciki ya barta iskar lambu na fifita mata sisirin dogon wuyanta ,Halley tace zan je dai naga yarana ya suka koma yanzu,murmushi tayi tana tunano su.
Online ta hau ta shiga searching sunansu ko zata gansu,har cikin friends din mahaifin su Sohail ta shiga ko zata gansu bata san uban ma bata su yake ba,shi dai kawai ya basu ci da sutura shine kawai,text ta turawa Alhaji Ali ya turo mata pics din yaranta yana ganin haka yayi blocking number dinta gaba daya ya shiga harkarsa.
Islaha kuwa kwananta daya da asuba Lalai ta tasheta tace maza kiyi sallah kije ki cika gidan nan da ruwa,Islaha tace Abdulrazaqu fa ai shi naga yana ebo miki tunda shine namiji a gidan nan kuma danki ne na cikinki sai yau zaki ce ni, Lalai tace to ke naga dama zan dafa na baki kici a kwance ne,Islaha brush tayi tayi alwala da sallah ta zauna azkhar dinma Lalai damunta tayi ta tashi haka,da kuturin iyayi mu zaki nunawa addini zaki zauna kina mismis da baki.
Tashi Islaha tayi ta dauki botiki duk garin babu budurwa me girmanta da shekarunta sai kallonta akeyi,gashi kasan ba yar garin bace kana ganinta yar birni ce,rijiyar da suke iban ruwan ta karasa,kowa da gugansa yake zuwa.
Ruwan ta jawo ta cika botiki duk maza ne a wajen sun fito iban ruwa kafin su tafi gona wasu su tafi kiwo,Islaha tana gama Iba ta dauka ta kai gida haka ta dinga jidon ruwa sai da ta cika ko ina na gidan sannan Lalai ta bata dumamen tuwo da wani dan koko a kofi kamar na yaron yaye tace gashi nan.
Islaha tace kaddara kenan in ba kaddara ba me zai sa naci wannan tuwon,Lalai ce ma zata yi wani girki ta bani naci,Lalai tana ji tace uban wa ya kawo ki gidan,ji nake ke kika kawo kanki kinibabbiyya.
Islaha haka tana kushewa ta cinye tuwo ta shanye koko tace dan dai kawai na rayu ne wlh da bazan ci ba,Lalai ta fito tana masifa sai kije kiyi wanke wanke ko a banza zan zauna ina dafawa ina baki kina ci.
Islaha taje tayi wanke wankenta tayi shara ta gyara gidan,Lalai tace saura daka, mu kin san a nan sai munyi sissika,surfe ma da hannu muke yi a turmi sai ki fito ai,Islaha ta dauki tabarya ta tsaya a jikin katon turmi,Lalai ta zuba dawa tace bismillah mu fara wannan dai zan tayaki,kyazo kici a kwance ne,sabo da Allah sai dai a baki kici ki koshi, sa jiki yi da jiki maza saka tabarya,Islaha ta saka tabarya daya chakwal chakwal sam bata iya ba,Lalai ta sa tata tace yar bibiyu zamu yi muje zuwa a hankali zaki goge.
Islaha ta dinga yi suna yi a haka da Lalai kaikayi yana tashi zuwa jikinsu, Abdulrazaqu ne ya shigo sai faman zagasu yake yana karewa Islaha kallo yana sannunku da aiki,Islaha ashe kin dawo nan da zama yana wage baki,da wata hularsa bokoko.
Lalai tace tayi aure taki ka ganta nan kalar bazawara, Abdulrazaqu yace ai watakil rabon na gida ne shi yasa Allah ya dawo da ita,yin Allah ne,Islaha..Islaha...kaga Islaha sarkin aiki cewar Abdulrazaqu,Islaha haushin Abdulraqu ya gama kamata da irin kallon da yake mata.
A cikin gidan ya nemi jikin bishiya ya zauna sai faman kallonta yake yana murmushi baki a bude,Islaha ta gaji amma sai da aka gama daka da ita,sannan Lalai ta kwaso danyen rogon da Abdulrazaqu ya kawo ta mikawa Islaha wuka tace maza mu fere shi za a dafa yau aci da kuli.
Kaga sai a raba muku kwana yau kai kazo mu kwana tare gobe Sahil yazo,Sohail yace ai kuwa da an rataye Sahil anyi hanging dinsa kawai an huta, yarinya na sani to namiji daya shi yake auren mata hudu mace namiji daya tal take aura.
To yanzu mata hudun zaka yi kenan? Sohail yace to a Office tv dina naji wa'azin Allah ne yace malam yace a taimaki mata sunyi yawa a gari idan da hali mutum yayi ta karawa har su kai hudu,kinga kece uwargida zan miki wannan alfarmar na aureki a farko daga baya sai a karo miki ta biyu a haka har na cike hudu na,Yan mata hudu rigis ni kadai gaskiya mun muku wayo mu.
Maheera tace wanne malami ne yayi wannan wa'azin? ban sanshi ba channel din a tv din Office dina take,Maheera a ranta tace dole na kira Alhaji Saminu a tsinke wannan Channel,ina so ya dinga jin wa'azi amma banda na kishiya,inda baida kai ai sai yace sai yayi, sai ya aure su.
Maheera tace Sohail ba haka malamin yake nufi ba,nufinsa idan mutum zai iya adalci kuma yana da kudi sosai,Sai zai iya adalci aka ce idan bazai iya ba yayi zamansa da guda dayarsa,Sohail yace aya da hadisi ya kawo to Hajiya.
Maheera tace uhmm ai shike nan yace ae ga kuma Hurul ayni yace na lahira suna can a lahira suna jirana gaskiya mun gama da ku mata kuyi hakuri 10-0 kawai.
Dariya ya bawa Maheera tace ashe kai mayen mata ne ban sani ba,daga kaga ka fara kudi shine ka fara zancen mata,Adnan shi da matarsa daya ta ishe shi abinsa gwanin sha'awa kai da mamanku take baturiya baka gaji halin turawa ba mace daya danginku suke yi,Sohail yace ni nasan wata mama ne ina ruwana da su.
Yaushe zaki tafi gidanku? Maheera tace ina nan bazan tafi ba,aikina zanyi,Sohail yace shike nan ki ta zama tunda ke bakya son ci gaba,tace ae naji mutumin da zaiyi mata hudu waye zai dogara da shi jeka can da matanka bada Maheera ba.
Maman su Maheera aka kwantar a asibiti ciwonta ya tashi,kannen Maheera ne suka kaita asibiti sai da suka kwana kudinsu ya kare sannan suka kira Maheera,tare da sanar mata.
Sohail kuma ya rigata sanin ma an kai Mama asibiti yau aljanun sun waiwayo,Zuwa yayi har asibitin ya dubata su Juwairiyya basu sanshi ba sai kallonsa suke yi,ya tambayi kudin nawa zasu biya? Suka ce dubu dari biyu da hamsim mun biya dubu hamsim,dubu hamsim dinsu ya basu yaje ya biya kudin komai da komai da duk wani magunguna da ake bukata masu tsada ya siya mata da yawa aka siya wanda zai dade bai kare ba.
Abincin masu ciwon sugar daban haka yasa aka masa list duk ya siyowa Mama,komai naci sai da ya siyo har na kannen Maheera abinda zasu ci lemuka da fruits da kayan shayi etc sai kudi ya basu yace ga wannan ku rike idan zaku siyi abinci,Suka ce mun gode.
Ammar yace dan Allah waye kai? Sohail yace sunana Sohail idan Maheera tazo ku fada mata ta sanni,suka ce to an gode.
Yana tafiya Maheera taje asibitin ko zama bata yi ba tace ya jikin maman? Bacci take tun rana,me suka ce za a biya?
Wani yazo ya biya komai kalli abinda ya siyo yace sunansa Sohail,kawai ganinsa muka yi yazo, Juwairiyya tace Aunty wani kyakyawa ne wlh,Sahil ne ya shigo kamar ana fada musu,Ammar yace yawwa gashi ma ya dawo,basu gane ba Sohail bane,ita kanta Maheera sai da yayi magana taga wushiyarsa yar karama ta gane Sahil ne.
Tace dan uwansa ne fa ba shi bane wannan Sahil ne waccen Sohail,Su Ammar suka ce ikon Allah basu da banbanci,Sahil zuwa yayi ya ja kujera ya zauna ya tambaya ya jikin Maman? tace da sauki,Su Ammar suka gaida shi yayi musu ya me jiki.
Sahil harda cewa kaiii Mama tana jin jiki wannan kibar tata bata Allah bace ciwon ne ya hura ta karku dauka jin dadi ne yasa tayi kiba haka, suka ce ae haka likita yace,Allah ya bata lafiya ya furta,20k ya basu yace sa suyi wani abun,suka ce kaima sai ka bamu?
Yace ya zanyi Sohail yace na baku ba yin kaina bane Sohail ne ya min dole yace lallai na baku,ba wani kudi ne da mu ba rufin asirin Allah ne,Maheera ta boye dariyarta tace to mun gode ka gaida gida,yace a'a sai kace mahaukaci zance gida ance ana gaisheka gida ba mutum ba ba komai ba kice na gaishe shi bazan yi ba ya fice yana cewa Mama Allah ya baki lafiya kiba haka kamar ta jin dadi kai ciwo da wuya yake,sai kace kibar sihiri kafafu tutum tutum haka.
England
Wata dattijuwa ce zaune a garden din gidanta tare da wani tsohon bature Halley Maman su Sohail,Mijinta ta kalla Ivan,cikin harshen turanci tace ina so zanje Nigeria zuwa nan da wata uku,tun daga yarana dana bada su na zaci idan nayi aure zan sake haihuwa ban sake haihuwa ba tunda na aure ka wanda a baya ina da kuruciya bani da aiki sai club da holewa na sa a gaba,yaro na daya bashi da lafiya suka dameni na bawa ubansu shi ya sake ni,yanzu ni nasan nayi kuskure suna can sun zama musulmai,bana so kuma su kasance musulmai gaskiya,bana son musulunci,bayan haka yanzu basu sanni ba ina bukatar yarana su sanni na jasu a jiki.
Na nemi ubansu rannan da kyar na samu number dinsa wajen abokinsa Harry na kira yana ji nice ya kashe wayarsa,yanzu Nigeria zan tafi na ja yarana a jikina su san wace ni tunda ban haifi wasu ba.
Mijinta Ivan yace kinyi ganganci kuma baki yi daidai ba,yanzu baza su saurare ki ba,baza ki iya canja musu addini ba,indai hakane Halley har yanzu to baki hankali ba,na zaci ma zaki ce bari kije ki basu hakuri su karbe ki a matsayin uwa amma ke ta addini kike yi,sannan kuma tunda baki haifi wasu ba shine zaki neme su,yaran naki kisan da marar lafiya baki tausaya musu ba,baki da hankali Ivan ya mike ya wuce ciki ya barta iskar lambu na fifita mata sisirin dogon wuyanta ,Halley tace zan je dai naga yarana ya suka koma yanzu,murmushi tayi tana tunano su.
Online ta hau ta shiga searching sunansu ko zata gansu,har cikin friends din mahaifin su Sohail ta shiga ko zata gansu bata san uban ma bata su yake ba,shi dai kawai ya basu ci da sutura shine kawai,text ta turawa Alhaji Ali ya turo mata pics din yaranta yana ganin haka yayi blocking number dinta gaba daya ya shiga harkarsa.
Islaha kuwa kwananta daya da asuba Lalai ta tasheta tace maza kiyi sallah kije ki cika gidan nan da ruwa,Islaha tace Abdulrazaqu fa ai shi naga yana ebo miki tunda shine namiji a gidan nan kuma danki ne na cikinki sai yau zaki ce ni, Lalai tace to ke naga dama zan dafa na baki kici a kwance ne,Islaha brush tayi tayi alwala da sallah ta zauna azkhar dinma Lalai damunta tayi ta tashi haka,da kuturin iyayi mu zaki nunawa addini zaki zauna kina mismis da baki.
Tashi Islaha tayi ta dauki botiki duk garin babu budurwa me girmanta da shekarunta sai kallonta akeyi,gashi kasan ba yar garin bace kana ganinta yar birni ce,rijiyar da suke iban ruwan ta karasa,kowa da gugansa yake zuwa.
Ruwan ta jawo ta cika botiki duk maza ne a wajen sun fito iban ruwa kafin su tafi gona wasu su tafi kiwo,Islaha tana gama Iba ta dauka ta kai gida haka ta dinga jidon ruwa sai da ta cika ko ina na gidan sannan Lalai ta bata dumamen tuwo da wani dan koko a kofi kamar na yaron yaye tace gashi nan.
Islaha tace kaddara kenan in ba kaddara ba me zai sa naci wannan tuwon,Lalai ce ma zata yi wani girki ta bani naci,Lalai tana ji tace uban wa ya kawo ki gidan,ji nake ke kika kawo kanki kinibabbiyya.
Islaha haka tana kushewa ta cinye tuwo ta shanye koko tace dan dai kawai na rayu ne wlh da bazan ci ba,Lalai ta fito tana masifa sai kije kiyi wanke wanke ko a banza zan zauna ina dafawa ina baki kina ci.
Islaha taje tayi wanke wankenta tayi shara ta gyara gidan,Lalai tace saura daka, mu kin san a nan sai munyi sissika,surfe ma da hannu muke yi a turmi sai ki fito ai,Islaha ta dauki tabarya ta tsaya a jikin katon turmi,Lalai ta zuba dawa tace bismillah mu fara wannan dai zan tayaki,kyazo kici a kwance ne,sabo da Allah sai dai a baki kici ki koshi, sa jiki yi da jiki maza saka tabarya,Islaha ta saka tabarya daya chakwal chakwal sam bata iya ba,Lalai ta sa tata tace yar bibiyu zamu yi muje zuwa a hankali zaki goge.
Islaha ta dinga yi suna yi a haka da Lalai kaikayi yana tashi zuwa jikinsu, Abdulrazaqu ne ya shigo sai faman zagasu yake yana karewa Islaha kallo yana sannunku da aiki,Islaha ashe kin dawo nan da zama yana wage baki,da wata hularsa bokoko.
Lalai tace tayi aure taki ka ganta nan kalar bazawara, Abdulrazaqu yace ai watakil rabon na gida ne shi yasa Allah ya dawo da ita,yin Allah ne,Islaha..Islaha...kaga Islaha sarkin aiki cewar Abdulrazaqu,Islaha haushin Abdulraqu ya gama kamata da irin kallon da yake mata.
A cikin gidan ya nemi jikin bishiya ya zauna sai faman kallonta yake yana murmushi baki a bude,Islaha ta gaji amma sai da aka gama daka da ita,sannan Lalai ta kwaso danyen rogon da Abdulrazaqu ya kawo ta mikawa Islaha wuka tace maza mu fere shi za a dafa yau aci da kuli.