Sashe 3
Mumnunar Dabia Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bayan shekaru biyu Su Sahil suka gama Secondary school dinsu,sun wani tasa sun girma sun kara kyau,lokacin kuma Sohail Allah ya yaye masa dalalar yawu tuni,ya daina abubuwa da yawa duk ya daina ya zama cikakken mutum amma fa akwai shirme,kana ganin yanda yake abubuwansa kasan kansa yana fisga, sai dai an daina wasu abubuwan manya wanda hakan ba karamin dadi yayiwa Asmau da Ali ba, idan yana abubuwa a rikice zaka san lallai fa wani abu na damunsa,a hankali shima Sahil kawai rana tsaka kansa ya fara tabuwa irin na Sohail,yanda Sohail ke shirmen shima haka yake yi, iri daya suke shiriritar su da Sohail,Asmau ta damu sosai tayi tayi Alhaji Ali ya tsaya a nema musu magani sosai amma yaki sam,ganin ma a haka basu da kokari basu san komai na duniya ba sai dai result kawai a school me kyau sune suke daukan na daya,amma idan ka tambaye su abu daya baza su iya fada maka ba,har shi Sahil din duk kokarinsa yanzu babu ya gudu bai san komai ba,shi yasa sam Alhaji Ali mahaifinsu bai damu da su ba.
Yana ganin ba abinda zasu iya tsinanawa a rayuwa kawai dai a basu ci da sha,ganinsu yake kamar ma ba mutane ba,komai baya sawa da su sai dai yaran Nadia sune mutane,ya dauki su Sohail ba wasu mutane ba,Asmau tun tana fada masa gaskiya har ta gaji,zai basu sutura ci da sha shike nan,su Ibrahim kuwa har kasuwan ci yasa ake koya musu suna gama school zai basu company guda shi da Adnan.
ita kuwa Nadia dan dalalar yawun ma da Sohail ya daina sai bacin rai take da Sohail ya samu lafiya,duk shirmen da suke bugawa shi da Sahil a haka cewa take lafiya suke.
Yau ma Mama gani tayi sun sha wankan kana nan kaya abinsu abinka da kuruciya,sun sha kyau kamar a sace su,tace ina zuwa kuma? Sohail yana daura agogo shi a dole shege yace filin ball zamu kalli wani match yana yarfe hannu,Sahil kuwa turare ya fesa yana wani jiji da kai,Mama dariya tayi kawai tace to a dawo lafiya manyan yara,suka amsa da Ameen,tace banda driving driver ya kaiku please,suka ce to sannan Sohail harda yiwa Mama kiss a kumatu ta make shi suka fita suna dariya,amma yanda suke kalle kalle da wuri wuri kasan ba lafiya kansu da tabi.
Driver ne ya kaisu har gidan su Zaynah suma katafaren gida a hadaddiyar unguwa,tasan da zuwansu ta sha gayunta,yanzu tunda sun gama secondary ana barinta tana zance,fitowa tayi sanye cikin doguwar rigar material,har ga Allah bata gane waye Sohail ba waye Sahil ba yau ta kasa ganewa sai taje ta rike hannun Sahil,Sohail yayi murmushi yace ke kin ganni nan tunda kema bakya iya ganewa,Murmushi Sahil yayi tare da fisge hannunsa,Zayna dafe goshinta tayi tare da furta oups I'm sorry,Sohail yace sai kace kin rike wani bare he is my blood tare zamu aure ki fa mu biyu,Sahil yace InshaAllah ki kwantar da hankalinki matar 'yan biyu ce ke,Zayna ta zaro ido tasan kansu da motsi shi yasa dariya suka yi sannan suka shiga cikin gidan,Sahil ya koma mota ya zauna yana danna waya abinsa,yana jiran Sohail,Sohail lekowa yayi yace kazo ka kama min,bazan iya zancen ba sai kace ni kadai zan aure ta ai har da kai a ciki,driver yana jinsu yana ta dariya,yace au dama wai zance kuka zo nan? Kuma mace daya zaku aura ku biyu? Sahil yace ta ishe mu rayuwar duniya ya bude mota ya fice ya bar driver yana ta dariya.
Sohail suka shiga palo Zayna suna hirar school din su,Sahil yace I love you Zayna, Zayna ta zaro ido tace kaga saurayina fa,Sohail ya bata rai yace shima yana sonki ai tare muke son ki idan bakya sonsa nima bakya so na to shike nan na daina kulaki,Zayna tace sai kace akuya ce ni ta ya zan so maza biyu ni bazan iya ba,to shike nan nima na daina sonki wlh,Sahil a fusace ya mike kamar zai mare ta ya daki table sai da ta tsorata,yace da Sohail muje,Sohail ya mike yace kinwa kanki ki rasa mu karki sake kula mu.
Zayna tace to sai me aikin banza mahaukata da ku ma,nan a makaranta kake dalalar da yawu,dama dan kana da kyau nake kulaka amma me zanci da mahaukata,Sahil ne ya dawo ya rike Zayna ya kwashe ta da mari,ya fara dukanta sai da ya mata lilis tana ihu yan gidan su suka fito da gudu,Sohail ya jawo Sahil.
Maman zayna tace amma ku dai kunyi asara ai zaku aikata mahaukatan banza,kowa ya fito yana tambaya lafiya sai ace ai mahaukatan nan ne sai ace ohhh Allah sarki ai mahaukata ne a kyale su,su Sahil ko a jikin su dan ance musu mahaukata suka yi tafiyar su.
Sai dare suka koma gida , Mama suka iske Fada ta fara tace dan iskanci sai yanzu zaku dawo,Sahil yace wai Mama a koma bamu nono mana kawai a huta ace muna maza zamu fara university ba inda zamu je muyi dare sai kace mata,Sohail yana jinsu ya saka Earpiece dinsa zai toshe kunne,Mama ta rike kunnen sa tare da murdewa dariya ya hau yi dake yafi Sahil fara'a shi,bana so ne a samu matsala ku lalace,karatu zaku fara fa, kafadar Mama Sahil ya dafa kamar wata sa'arsa yace ba abinda zai faru, Mama tace Allah yasa,Abinci fa? Mun koshi mun ci burger dazu,tace to Good night ayi adduar bacci kar a manta.
Sam su Sohail basu taba tambayar ina maman su ba,ko wacece ba ruwan su ko zancen basu taba yi ba.
Bayan wasu watanni Sohail da Sihil aka kai su private University dake Germany suna can suna karatunsu amma dai sai dai result me kyau basu san komai na karatun ba har yanzu
Har suka shiga level 2 sannan suka zo hutu gida.
Suna zuwa hutu suka samu anyiwa Amal aure ta auri wani hamshakin me kudi dattijo ne gidanta daban,Adnan ma yayi aure an masa aure,ko fada musu ba ayi ba sabo da ana ganin basu da muhimmanci,basu da amfani a duniya haka mahaifinsu da sauran yan uwa ke gani,basu ma ce me yasa ba a fada musu ba sai murna ma da suka yi Adnan yayi aure da Amal,Mama Asmau itace komai dinsu a gidan sabo da ita ne ba a iya taka su.
Hajiya Asmau yau shiri suka yi ita da kishiyarta Nadia zasu je Kaduna bikin 'yan uwan Nadia a danginta dake ita yar kaduna ce,Asmau Kara zata yi mata,su biyu driver ya tuka a mota suka tafi cikin ikon Allah a hanya motar su tayi hatsari bayan tayi dugu dugu motar nan take ta kama da wuta,da kyar aka samu ma aka kashe wutar,babu wanda ya tsira a motar gaba daya sun mutu da Nadia da Asmau har driver,Alhaji Ali sai mummunan labari yaji,nan take ya fadi a sume aka kaishi asibiti.
Su Adnan kuka kamar ba gobe,su 'yan biyu ma basu san me ake yi ba suna daki suna game tunda Mama ta tafi basu fito ba,mutuwar ma sabo da iskanci ba wanda ya kula su Sohail bare a fada musu kawai ba mutane bane,Alhaji ya farfado da shi aka hada matan nasa wanda duk sun kone kurmus,sai sassan jikin su kadan,hayaniya da kuka ne yayi yawa Sohail ya mike sanye daga shi sai gajeren wando ya fito yana lekowa yaga mutane dankam mata sun cika ko ina na gidan.
Dawowa yayi ya saka jallabiya yace kai Sahil gida fa ana ta kuka an cika gida ko menene oho,Sahil yana ji yace kar fa abar nan ce tazo gidan nan yau,ai kuwa ina jin ma itace tazo din cewar Sohail,yace tabbas ta karaso bari muji wa tazo ta dauke,Allah yasa Umma Nadia ce,Sahil yace 3qtr ma zan saka dan iskan zaman makoki zanyi naji a jikina Umma Nadia ce,3qtr ya sha me tsada da tshirts dinsa wata grey,shi kuwa Sohail jallabiya ce fara a jikinsa,a jikin Mirror suka tsaya suna taje sumar su ,Sahil ya shafa man lebensu na maza me kyau,Sohail ya hau fesa turare sai da suka gama suka bude kofa tare da fitowa wai zaman Makokin Nadia zasu yi.
Mata aka zuba musu ido yuuuuuuuu kamar za a cinye su sabo tsananin kyawunsu,suna zuwa Main palo suka ga yan uwan Mama Asmau da yawa suna ta kuka,wani palon kuma yan uwan Nadia ne,Amal tana ta rusa uban ihu a cikin su,Sohail yace cikin rada da alama Umma Nadia ce,Sahil yace akwai rawar bungalo yau da galala,suka dawo ta parlon da yan uwan Mama suke domin sun fi sanin su,Sohail ne yaji ana cewa Allah sarki sune yaran Asmau wanda ta raina,Allah sarki sunyi rashi,Allah kaji kan Asmau, mutuniyar arziki,Sohail yaci wani wawan birki yace wa naji kuna cewa? Sai lokacin ya tuna ai tare suka tafi unguwa da Nadis, Yanda yayi maganar cikin tsawa da karaji sai da suka firgita,Sahil yaje ya rike wata tsohuwa cikin dangin Asmau yace wacece ta mutu? Dattijuwar tana hawaye tace Nadia ce da Asmau duka matan mahaifinku sunyi hadarin mota Allah ya musu rasuwa gasu can ana sallatar su.
Sohail yace wai Maman mu har da ita ta rasu? Suka ce ae,sumarsa ya hargitsa ba tare da ya sani bama,ya fara kokarin cire rigarsa da ya fesa mata turare yana hawaye nan take idonsa yayi jajir, Sahil kuka yake wiwi sosai yake kuka,ana ta basu hakuri,Dattijuwar tace sai hakuri,Sahil cikin karaji yace baza muyi hakurin ba,wallahi bazan hakura ba sai munyi kukan.
Da kyar da lallashi suka tashi suka nufi wajen makokin,Alwala suka yi suka bi sawu aka sallaci gawar Mama da Umma da su,ana sallar suna ta sharbar kuka sam basu iya sallar ba sai kace mata.
Yana ganin ba abinda zasu iya tsinanawa a rayuwa kawai dai a basu ci da sha,ganinsu yake kamar ma ba mutane ba,komai baya sawa da su sai dai yaran Nadia sune mutane,ya dauki su Sohail ba wasu mutane ba,Asmau tun tana fada masa gaskiya har ta gaji,zai basu sutura ci da sha shike nan,su Ibrahim kuwa har kasuwan ci yasa ake koya musu suna gama school zai basu company guda shi da Adnan.
ita kuwa Nadia dan dalalar yawun ma da Sohail ya daina sai bacin rai take da Sohail ya samu lafiya,duk shirmen da suke bugawa shi da Sahil a haka cewa take lafiya suke.
Yau ma Mama gani tayi sun sha wankan kana nan kaya abinsu abinka da kuruciya,sun sha kyau kamar a sace su,tace ina zuwa kuma? Sohail yana daura agogo shi a dole shege yace filin ball zamu kalli wani match yana yarfe hannu,Sahil kuwa turare ya fesa yana wani jiji da kai,Mama dariya tayi kawai tace to a dawo lafiya manyan yara,suka amsa da Ameen,tace banda driving driver ya kaiku please,suka ce to sannan Sohail harda yiwa Mama kiss a kumatu ta make shi suka fita suna dariya,amma yanda suke kalle kalle da wuri wuri kasan ba lafiya kansu da tabi.
Driver ne ya kaisu har gidan su Zaynah suma katafaren gida a hadaddiyar unguwa,tasan da zuwansu ta sha gayunta,yanzu tunda sun gama secondary ana barinta tana zance,fitowa tayi sanye cikin doguwar rigar material,har ga Allah bata gane waye Sohail ba waye Sahil ba yau ta kasa ganewa sai taje ta rike hannun Sahil,Sohail yayi murmushi yace ke kin ganni nan tunda kema bakya iya ganewa,Murmushi Sahil yayi tare da fisge hannunsa,Zayna dafe goshinta tayi tare da furta oups I'm sorry,Sohail yace sai kace kin rike wani bare he is my blood tare zamu aure ki fa mu biyu,Sahil yace InshaAllah ki kwantar da hankalinki matar 'yan biyu ce ke,Zayna ta zaro ido tasan kansu da motsi shi yasa dariya suka yi sannan suka shiga cikin gidan,Sahil ya koma mota ya zauna yana danna waya abinsa,yana jiran Sohail,Sohail lekowa yayi yace kazo ka kama min,bazan iya zancen ba sai kace ni kadai zan aure ta ai har da kai a ciki,driver yana jinsu yana ta dariya,yace au dama wai zance kuka zo nan? Kuma mace daya zaku aura ku biyu? Sahil yace ta ishe mu rayuwar duniya ya bude mota ya fice ya bar driver yana ta dariya.
Sohail suka shiga palo Zayna suna hirar school din su,Sahil yace I love you Zayna, Zayna ta zaro ido tace kaga saurayina fa,Sohail ya bata rai yace shima yana sonki ai tare muke son ki idan bakya sonsa nima bakya so na to shike nan na daina kulaki,Zayna tace sai kace akuya ce ni ta ya zan so maza biyu ni bazan iya ba,to shike nan nima na daina sonki wlh,Sahil a fusace ya mike kamar zai mare ta ya daki table sai da ta tsorata,yace da Sohail muje,Sohail ya mike yace kinwa kanki ki rasa mu karki sake kula mu.
Zayna tace to sai me aikin banza mahaukata da ku ma,nan a makaranta kake dalalar da yawu,dama dan kana da kyau nake kulaka amma me zanci da mahaukata,Sahil ne ya dawo ya rike Zayna ya kwashe ta da mari,ya fara dukanta sai da ya mata lilis tana ihu yan gidan su suka fito da gudu,Sohail ya jawo Sahil.
Maman zayna tace amma ku dai kunyi asara ai zaku aikata mahaukatan banza,kowa ya fito yana tambaya lafiya sai ace ai mahaukatan nan ne sai ace ohhh Allah sarki ai mahaukata ne a kyale su,su Sahil ko a jikin su dan ance musu mahaukata suka yi tafiyar su.
Sai dare suka koma gida , Mama suka iske Fada ta fara tace dan iskanci sai yanzu zaku dawo,Sahil yace wai Mama a koma bamu nono mana kawai a huta ace muna maza zamu fara university ba inda zamu je muyi dare sai kace mata,Sohail yana jinsu ya saka Earpiece dinsa zai toshe kunne,Mama ta rike kunnen sa tare da murdewa dariya ya hau yi dake yafi Sahil fara'a shi,bana so ne a samu matsala ku lalace,karatu zaku fara fa, kafadar Mama Sahil ya dafa kamar wata sa'arsa yace ba abinda zai faru, Mama tace Allah yasa,Abinci fa? Mun koshi mun ci burger dazu,tace to Good night ayi adduar bacci kar a manta.
Sam su Sohail basu taba tambayar ina maman su ba,ko wacece ba ruwan su ko zancen basu taba yi ba.
Bayan wasu watanni Sohail da Sihil aka kai su private University dake Germany suna can suna karatunsu amma dai sai dai result me kyau basu san komai na karatun ba har yanzu
Har suka shiga level 2 sannan suka zo hutu gida.
Suna zuwa hutu suka samu anyiwa Amal aure ta auri wani hamshakin me kudi dattijo ne gidanta daban,Adnan ma yayi aure an masa aure,ko fada musu ba ayi ba sabo da ana ganin basu da muhimmanci,basu da amfani a duniya haka mahaifinsu da sauran yan uwa ke gani,basu ma ce me yasa ba a fada musu ba sai murna ma da suka yi Adnan yayi aure da Amal,Mama Asmau itace komai dinsu a gidan sabo da ita ne ba a iya taka su.
Hajiya Asmau yau shiri suka yi ita da kishiyarta Nadia zasu je Kaduna bikin 'yan uwan Nadia a danginta dake ita yar kaduna ce,Asmau Kara zata yi mata,su biyu driver ya tuka a mota suka tafi cikin ikon Allah a hanya motar su tayi hatsari bayan tayi dugu dugu motar nan take ta kama da wuta,da kyar aka samu ma aka kashe wutar,babu wanda ya tsira a motar gaba daya sun mutu da Nadia da Asmau har driver,Alhaji Ali sai mummunan labari yaji,nan take ya fadi a sume aka kaishi asibiti.
Su Adnan kuka kamar ba gobe,su 'yan biyu ma basu san me ake yi ba suna daki suna game tunda Mama ta tafi basu fito ba,mutuwar ma sabo da iskanci ba wanda ya kula su Sohail bare a fada musu kawai ba mutane bane,Alhaji ya farfado da shi aka hada matan nasa wanda duk sun kone kurmus,sai sassan jikin su kadan,hayaniya da kuka ne yayi yawa Sohail ya mike sanye daga shi sai gajeren wando ya fito yana lekowa yaga mutane dankam mata sun cika ko ina na gidan.
Dawowa yayi ya saka jallabiya yace kai Sahil gida fa ana ta kuka an cika gida ko menene oho,Sahil yana ji yace kar fa abar nan ce tazo gidan nan yau,ai kuwa ina jin ma itace tazo din cewar Sohail,yace tabbas ta karaso bari muji wa tazo ta dauke,Allah yasa Umma Nadia ce,Sahil yace 3qtr ma zan saka dan iskan zaman makoki zanyi naji a jikina Umma Nadia ce,3qtr ya sha me tsada da tshirts dinsa wata grey,shi kuwa Sohail jallabiya ce fara a jikinsa,a jikin Mirror suka tsaya suna taje sumar su ,Sahil ya shafa man lebensu na maza me kyau,Sohail ya hau fesa turare sai da suka gama suka bude kofa tare da fitowa wai zaman Makokin Nadia zasu yi.
Mata aka zuba musu ido yuuuuuuuu kamar za a cinye su sabo tsananin kyawunsu,suna zuwa Main palo suka ga yan uwan Mama Asmau da yawa suna ta kuka,wani palon kuma yan uwan Nadia ne,Amal tana ta rusa uban ihu a cikin su,Sohail yace cikin rada da alama Umma Nadia ce,Sahil yace akwai rawar bungalo yau da galala,suka dawo ta parlon da yan uwan Mama suke domin sun fi sanin su,Sohail ne yaji ana cewa Allah sarki sune yaran Asmau wanda ta raina,Allah sarki sunyi rashi,Allah kaji kan Asmau, mutuniyar arziki,Sohail yaci wani wawan birki yace wa naji kuna cewa? Sai lokacin ya tuna ai tare suka tafi unguwa da Nadis, Yanda yayi maganar cikin tsawa da karaji sai da suka firgita,Sahil yaje ya rike wata tsohuwa cikin dangin Asmau yace wacece ta mutu? Dattijuwar tana hawaye tace Nadia ce da Asmau duka matan mahaifinku sunyi hadarin mota Allah ya musu rasuwa gasu can ana sallatar su.
Sohail yace wai Maman mu har da ita ta rasu? Suka ce ae,sumarsa ya hargitsa ba tare da ya sani bama,ya fara kokarin cire rigarsa da ya fesa mata turare yana hawaye nan take idonsa yayi jajir, Sahil kuka yake wiwi sosai yake kuka,ana ta basu hakuri,Dattijuwar tace sai hakuri,Sahil cikin karaji yace baza muyi hakurin ba,wallahi bazan hakura ba sai munyi kukan.
Da kyar da lallashi suka tashi suka nufi wajen makokin,Alwala suka yi suka bi sawu aka sallaci gawar Mama da Umma da su,ana sallar suna ta sharbar kuka sam basu iya sallar ba sai kace mata.