Sashe 17
Mumnunar Dabia Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Islaha tace ban taba ganinku kunyi shiga haka ba kunyi kyau mashaallah,Sohail ne yace mun gode kin tabbatar munyi kyau? Islaha tace sosai ma yau mata sai....Sahil ne ya katse ta karki dami mutane,Maheera kallon Sohail tayi taji kamar kar ya fita ma yayi ta zama a gida,Haushi taji ta bata rai,Sohail yace baki ce komai ba tace me zance sai kun dawo Allah ya bada sa'a a samu aikin suka ce Ameen,wucewa zasu yi Sohail ya ja hancin Maheera yace kefa kika ce a nemi aiki kuma sai kiji haushi sabo da zan fita ko so na kike yi ne? Maheera da sauri tace ni haka nace ina sonka? Allah ya kiyaye aljanun karya suke yi da suka fada maka,Sohail dariya yayi yace shike nan dama ni Islaha nake so ba ke ba,Maheera ta dauke kai,Sahil yana jinsu yau yan maganar basa kansa ko uban waye in baiga dama ba bazai kula su ba ko me zaka ce,Haka suka fita Maheera ta zauna a saman kujera ranta a bace.
Islaha ta sheke da dariya tace lallai Maheera kina da aiki kuwa wlh,idan kika ce kar su fita ma ai bakya kaunar su aiki fa zasu nemo,Maheera ta mike bata ce komai ba suka gyara ko ina na gidan komai sai da suka yi.
Ibrahim ne ya fito sai faman kallon Islaha yake kamar maye,Islaha tana sane da shi ta kalle shi suka hada ido ya sakar mata murmushi tare da cewa kawo min tea,Wucewa tayi kitchen Maheera tana daki ta shiga wanka,Tea ta kawo masa yanda ya bukata,kallonta yayi yace zauna mana,da mamaki tace a nan din mu ai yan aiki ne,ni nace ki zauna ai.
Haka ta zauna a hankali sai kallonta yake yana murmushi,yace 'yar wanne state ce ke? Islaha tace taraba state Maheera kuma yar Adamawa ce asalinsu amma a sule ja suke da zama,Ibrahim yace ai ke wayayya ce naga alama,Islaha tace uhm bari naje zanyi aiki"
ba a son ransa ba yace okay kar na takura ki, mikewa tayi da sauri ta bar wajen ta wuce bangaren su,Ibrahim ya bita da kallo yana murmushi.
Sohail kuwa shigar da suka yi kamata yayi a gansu a mota amma a kafa suka fito,suka tsaya tare da zubawa hanya ido Sahil yace kabi hanyar dama ni nabi hanyar hagu kasan ba kowa zai dauke mu aiki har mu biyu ba a waje daya,Sohail yace ka kawo shawara kawai yabi hannun dama Sahil yabi hagu yana cewa duk wanda ya riga gamawa kawai ya wuce gida,mu hadu a gida.
Yanda suka fita neman aikin duk wani kamfani ko masana'anta sai sun shiga ciki suce aiki suke nema,Wani wajen ayi musu rashin mutunci,wani wajen kuma a rabu lafiya wani wajen kuma a kulle ko securitues su hana shiga.
Sohail ya gaji da tafiya da yawo tun sassafe suke abu daya har yamma tayi 4pm ma ta wuce domin idan lokacin sallah yayi masallaci suke shiga na kusa suyi sallah su dora daga inda suka tsaya.
Suit din ma duk sun cire ta saman sabo da wahala,har necktie din sun warware shi a haka kowannen su ke tafiya,last kamfani Sohail ya gani yace daga wannan gida zan koma sai kuma gobe idan Allah ya kaimu,Sohail ya iske kofar a kulle alamar ba mutane ya bubbuga shuru,yaci gaba da dukan kofa har ya gaji ga rana ya hada gumi,a bakin wajen ya zauna da folder a hannunsa ya zuba tagumi,mikewa yayi a hankali kamar zaiyi kuka ya shiga taxi ya nufi gida,Sahil kuwa har after 5 yana zaune a jikin bishiya yana ta bacci a haka ya jefar da folder a gefe,daga dan zama zai huta sai bacci,sai wurin 6pm ya farka ya tashi shima da kyar yake daga kafa ya shiga mota sai gida.
Maheera suna zaune suna kallo sai ga Sohail ya fado cikin dakin ransa a bace yana tafiya da kyar ya dafe kugu da hannu,bai ko kula kowa ba ya wuce tare da haurawa sama,suka bishi da kallo sun san ba nasara ba a dace ba shuru suka yi kawai,yana shiga bedroom ya zauna a kasa ya kwanta a kasan tile yana kallon sama hawaye suna ta faman sintiri daga idanuwan Sohail,ba a dade ba Sahil shima haka ya shigo yana nishin gajiya ya wuce bai ma kula da mutane a palon ba,Ya fada dakin su ya shiga,saman bed ya fada shi yana wash....
Islaha ce ta shirya abinci a tire ta nufi dakin zata kai musu,Adnan ya fito yace ke idan ba aiki ba me yake kawo ku sama? Sabo da kuyi mana sata ko? Uban me zakuyi?Islaha ba tsoro tace Oga ba wajenka zanzo ba gida dai ai ba kune kadai masu shi ba,twins ma suna da hakki domin gidan uban su ne suma,kun zauna ba tausayi ba imani sai azaftar da bayin Allah kuke yi,a tunanina ku masu nemo musu aikin yi ne don ganin rayuwar su ta inganta,ku tuna wallahi akwai Allah wannan zaluncin yayi yawa ku ko tausayi baku da shi, har matarka me wuya kamar na zabuwa ka bata dama tana fada musu abinda taga dama.
Abinci ne zan kai musu kuma wallahi ba wanda ya isa ya hanani na kai musu babu shi a duniya,Adnan baki bude yace Iyyeeeeeee.... fantastic,wato an kawo ki an taimakeki an baki aikin yi shine kike ganin kin isa,Islaha tace ni baku taimakeni ba,zaman Sahil nake yi wajensa nazo,karuwarsa ce ke? Islaha tace ae karuwarsa ce ni sai me? Ta ja tsaki ta juya zata wuce Adnan ya fisgota tare da kifa mata mari yayi ball da tire din abincin ya watse,ya zazzaro mata ido yace yan biyu na tsane su bana kaunar ganinsu.
Islaha tace wallahi Allah ya isa kuma sai na kai abinci sai na kuma hado wani na kai musu,Adnan yace ke ga me taurin kai ko zanyi maganinki a gidan nan zaki raina kanki ya sauka kasa,tace kai din banza zaman lagos fa nayi wallahi karr nake duk sai nayi maganinku a gidan nan kuma bazan bar gidan ba,nazo kenan.
Ta koma kitchen ta hado wani abincin ta haura sama har bedroom din su Sohail tayi knocking,Sohail yana daga kwance a kasa yace come in,a hankali ta tura kofar ta shiga ta gansu a haka bata ji dadi ba ta ajiye musu tace,rayuwa sai hakuri kowa da kaddararsa kuyi hakuri, inshaallah zaku samu aikin yi tana fadar haka ta fita ta basu waje.
Tana fita tazo ta gyara inda Adnan ya zubar mata da abinci.
Yan biyu sai dare suka yi tashi suka ci abincin sannan suka yi wanka ko fitowa basu sake yi ba suka zauna kawai suka fara baccinsu.
Maheera tana zaune ta mike itama ta nufi dakin su Sahil,Zayna ta dawo daga unguwa ta shigo tana karkada key din mota,Maheera ta kalleta kawai zata wuce Zayna tace ke ina zaki je wannan part din masu gida ne idan ba aiki ba waye ya aikeki? Maheera juyowa tayi zata dawo Islaha tace dalla jeki mu ba wanda zamu kyale, gidane baza mu fita ba wallahi bana tsoron kowa rayuwar lagos nayi iskanci ne kawai bana yi amma indai da baki za ayi magana ba wanda ya isa naji tsoronsa.
Zayna ta juyo a fusace da matukar mamaki tace ke......a gidan mijina? Gidan aure na kizo kina daga min murya an dauke ki aiki amma kizo ni kina daga min murya? Islaha tace miji manya muma zaman wasu muke duk da ba a daura ba zaman su muke,Zayna tace to kuwa sai nasa kin bar gidan nan bari Adnan din ya shugo,Islaha tace shima adnan din naci ubansa ai ta kansa na fara baki sani ba,inci uban mijin inci na matar duk na gama da ku,Maheera tace Islaha kiyi shuru,Islaha tace ke kike jin tsoron su wlh.
Zayna sama ta wuce tana huci.
Maheera bedroom ta koma tana yiwa Islaha fada gidansu fa muka zo cin arziki muke,kuma kin san biyana akeyi ina da matsala a gidanmu nima indai rashin kunya ce na iya amma sabo da Iyayena da yan uwana nake hakura ina biyayya.
Amma ni duk layinmu ma tsoro na ake ji amma rayuwa da yanayi yasa na sakko,ki dain jansu da fada ki bari mu cimma buri sai mu fara bude musu munanan halayen mu,dariya Islaha tayi tace ina da hot temper bazan iya shuru ba kiyi hakuri amma zan fara mugunta a gidan nan,zaki ga tsiyar da zan dinga yi musu inda kika ga bera haka zan dawo
Wayar Maheera ce tayi kara ta duba taga kanwarta ce Juwairiyya ta daga tace yan university ya aka yi? Juwairiyya tayi dariya tace Alhmdllh Aunty kayan abincina ya kare sannan akwai wani kudi zamu biya 15k na escortion zamu je wani kamfani,Maheera tace kin san wata yayi nisa Juwairiyya bani da ki sisi wlh yanzu gashi jiya kudin hannuna na turawa Ammar ya siyowa Mama magungunanta su ma abincin su ya kusa karewa sai an siyi wani, Juwairiyya tace Aunty kina kokari ma an gode Allah ya buda bari mu jira mu gani me Allah zaiyi,nima zan duba idan na samu zaki ga Alert cewar Maheera,to Aunty na gode cewar Juwairiyya ta kashe wayar.
Islaha ta tambaya kudi za a bata? wai haka tace ni yanzu ma ban san ya zanyi ba,Islaha tace ga 20k cikin kudin asusuna ki tura mata tunda kinga ni ba abinda zan siya,Idan na karbe miki kudi ke kuma fa?
Islaha tace ba komai ai mun zama daya,rayuwa ce fa ni nasan wataran wa zai taimake ni? Kema kina taimako duk me taimako Allah baya hanashi sabo da haka karbi kawai.
Maheera karba tayi tana ta godiya tana jin dadi.
Washe gari Adnan ya samu Ibrahim yana masa magana akan Islaha lallai ya koreta ta bar musu gida taci mutuncinsa taci mutuncin matata.
Ibrahim yace Islaha kuma? Ae itace,
Gaskiya ba halinta bane kuma ma ai yarinya ce baka ganin bata da wayo kawai kayi hakuri zuwa wani lokaci su Sohail ne suke ziga ta,Adnan yace yarinyar nan bata da hankali fa,Ka dai dan kara hakuri tukun,fafur Ibrahim ya hana a kore ta shi baya ganin laifin Islaha sabo da sonta yake tsakani da Allah kuma burin aurenta yake.
Islaha ta sheke da dariya tace lallai Maheera kina da aiki kuwa wlh,idan kika ce kar su fita ma ai bakya kaunar su aiki fa zasu nemo,Maheera ta mike bata ce komai ba suka gyara ko ina na gidan komai sai da suka yi.
Ibrahim ne ya fito sai faman kallon Islaha yake kamar maye,Islaha tana sane da shi ta kalle shi suka hada ido ya sakar mata murmushi tare da cewa kawo min tea,Wucewa tayi kitchen Maheera tana daki ta shiga wanka,Tea ta kawo masa yanda ya bukata,kallonta yayi yace zauna mana,da mamaki tace a nan din mu ai yan aiki ne,ni nace ki zauna ai.
Haka ta zauna a hankali sai kallonta yake yana murmushi,yace 'yar wanne state ce ke? Islaha tace taraba state Maheera kuma yar Adamawa ce asalinsu amma a sule ja suke da zama,Ibrahim yace ai ke wayayya ce naga alama,Islaha tace uhm bari naje zanyi aiki"
ba a son ransa ba yace okay kar na takura ki, mikewa tayi da sauri ta bar wajen ta wuce bangaren su,Ibrahim ya bita da kallo yana murmushi.
Sohail kuwa shigar da suka yi kamata yayi a gansu a mota amma a kafa suka fito,suka tsaya tare da zubawa hanya ido Sahil yace kabi hanyar dama ni nabi hanyar hagu kasan ba kowa zai dauke mu aiki har mu biyu ba a waje daya,Sohail yace ka kawo shawara kawai yabi hannun dama Sahil yabi hagu yana cewa duk wanda ya riga gamawa kawai ya wuce gida,mu hadu a gida.
Yanda suka fita neman aikin duk wani kamfani ko masana'anta sai sun shiga ciki suce aiki suke nema,Wani wajen ayi musu rashin mutunci,wani wajen kuma a rabu lafiya wani wajen kuma a kulle ko securitues su hana shiga.
Sohail ya gaji da tafiya da yawo tun sassafe suke abu daya har yamma tayi 4pm ma ta wuce domin idan lokacin sallah yayi masallaci suke shiga na kusa suyi sallah su dora daga inda suka tsaya.
Suit din ma duk sun cire ta saman sabo da wahala,har necktie din sun warware shi a haka kowannen su ke tafiya,last kamfani Sohail ya gani yace daga wannan gida zan koma sai kuma gobe idan Allah ya kaimu,Sohail ya iske kofar a kulle alamar ba mutane ya bubbuga shuru,yaci gaba da dukan kofa har ya gaji ga rana ya hada gumi,a bakin wajen ya zauna da folder a hannunsa ya zuba tagumi,mikewa yayi a hankali kamar zaiyi kuka ya shiga taxi ya nufi gida,Sahil kuwa har after 5 yana zaune a jikin bishiya yana ta bacci a haka ya jefar da folder a gefe,daga dan zama zai huta sai bacci,sai wurin 6pm ya farka ya tashi shima da kyar yake daga kafa ya shiga mota sai gida.
Maheera suna zaune suna kallo sai ga Sohail ya fado cikin dakin ransa a bace yana tafiya da kyar ya dafe kugu da hannu,bai ko kula kowa ba ya wuce tare da haurawa sama,suka bishi da kallo sun san ba nasara ba a dace ba shuru suka yi kawai,yana shiga bedroom ya zauna a kasa ya kwanta a kasan tile yana kallon sama hawaye suna ta faman sintiri daga idanuwan Sohail,ba a dade ba Sahil shima haka ya shigo yana nishin gajiya ya wuce bai ma kula da mutane a palon ba,Ya fada dakin su ya shiga,saman bed ya fada shi yana wash....
Islaha ce ta shirya abinci a tire ta nufi dakin zata kai musu,Adnan ya fito yace ke idan ba aiki ba me yake kawo ku sama? Sabo da kuyi mana sata ko? Uban me zakuyi?Islaha ba tsoro tace Oga ba wajenka zanzo ba gida dai ai ba kune kadai masu shi ba,twins ma suna da hakki domin gidan uban su ne suma,kun zauna ba tausayi ba imani sai azaftar da bayin Allah kuke yi,a tunanina ku masu nemo musu aikin yi ne don ganin rayuwar su ta inganta,ku tuna wallahi akwai Allah wannan zaluncin yayi yawa ku ko tausayi baku da shi, har matarka me wuya kamar na zabuwa ka bata dama tana fada musu abinda taga dama.
Abinci ne zan kai musu kuma wallahi ba wanda ya isa ya hanani na kai musu babu shi a duniya,Adnan baki bude yace Iyyeeeeeee.... fantastic,wato an kawo ki an taimakeki an baki aikin yi shine kike ganin kin isa,Islaha tace ni baku taimakeni ba,zaman Sahil nake yi wajensa nazo,karuwarsa ce ke? Islaha tace ae karuwarsa ce ni sai me? Ta ja tsaki ta juya zata wuce Adnan ya fisgota tare da kifa mata mari yayi ball da tire din abincin ya watse,ya zazzaro mata ido yace yan biyu na tsane su bana kaunar ganinsu.
Islaha tace wallahi Allah ya isa kuma sai na kai abinci sai na kuma hado wani na kai musu,Adnan yace ke ga me taurin kai ko zanyi maganinki a gidan nan zaki raina kanki ya sauka kasa,tace kai din banza zaman lagos fa nayi wallahi karr nake duk sai nayi maganinku a gidan nan kuma bazan bar gidan ba,nazo kenan.
Ta koma kitchen ta hado wani abincin ta haura sama har bedroom din su Sohail tayi knocking,Sohail yana daga kwance a kasa yace come in,a hankali ta tura kofar ta shiga ta gansu a haka bata ji dadi ba ta ajiye musu tace,rayuwa sai hakuri kowa da kaddararsa kuyi hakuri, inshaallah zaku samu aikin yi tana fadar haka ta fita ta basu waje.
Tana fita tazo ta gyara inda Adnan ya zubar mata da abinci.
Yan biyu sai dare suka yi tashi suka ci abincin sannan suka yi wanka ko fitowa basu sake yi ba suka zauna kawai suka fara baccinsu.
Maheera tana zaune ta mike itama ta nufi dakin su Sahil,Zayna ta dawo daga unguwa ta shigo tana karkada key din mota,Maheera ta kalleta kawai zata wuce Zayna tace ke ina zaki je wannan part din masu gida ne idan ba aiki ba waye ya aikeki? Maheera juyowa tayi zata dawo Islaha tace dalla jeki mu ba wanda zamu kyale, gidane baza mu fita ba wallahi bana tsoron kowa rayuwar lagos nayi iskanci ne kawai bana yi amma indai da baki za ayi magana ba wanda ya isa naji tsoronsa.
Zayna ta juyo a fusace da matukar mamaki tace ke......a gidan mijina? Gidan aure na kizo kina daga min murya an dauke ki aiki amma kizo ni kina daga min murya? Islaha tace miji manya muma zaman wasu muke duk da ba a daura ba zaman su muke,Zayna tace to kuwa sai nasa kin bar gidan nan bari Adnan din ya shugo,Islaha tace shima adnan din naci ubansa ai ta kansa na fara baki sani ba,inci uban mijin inci na matar duk na gama da ku,Maheera tace Islaha kiyi shuru,Islaha tace ke kike jin tsoron su wlh.
Zayna sama ta wuce tana huci.
Maheera bedroom ta koma tana yiwa Islaha fada gidansu fa muka zo cin arziki muke,kuma kin san biyana akeyi ina da matsala a gidanmu nima indai rashin kunya ce na iya amma sabo da Iyayena da yan uwana nake hakura ina biyayya.
Amma ni duk layinmu ma tsoro na ake ji amma rayuwa da yanayi yasa na sakko,ki dain jansu da fada ki bari mu cimma buri sai mu fara bude musu munanan halayen mu,dariya Islaha tayi tace ina da hot temper bazan iya shuru ba kiyi hakuri amma zan fara mugunta a gidan nan,zaki ga tsiyar da zan dinga yi musu inda kika ga bera haka zan dawo
Wayar Maheera ce tayi kara ta duba taga kanwarta ce Juwairiyya ta daga tace yan university ya aka yi? Juwairiyya tayi dariya tace Alhmdllh Aunty kayan abincina ya kare sannan akwai wani kudi zamu biya 15k na escortion zamu je wani kamfani,Maheera tace kin san wata yayi nisa Juwairiyya bani da ki sisi wlh yanzu gashi jiya kudin hannuna na turawa Ammar ya siyowa Mama magungunanta su ma abincin su ya kusa karewa sai an siyi wani, Juwairiyya tace Aunty kina kokari ma an gode Allah ya buda bari mu jira mu gani me Allah zaiyi,nima zan duba idan na samu zaki ga Alert cewar Maheera,to Aunty na gode cewar Juwairiyya ta kashe wayar.
Islaha ta tambaya kudi za a bata? wai haka tace ni yanzu ma ban san ya zanyi ba,Islaha tace ga 20k cikin kudin asusuna ki tura mata tunda kinga ni ba abinda zan siya,Idan na karbe miki kudi ke kuma fa?
Islaha tace ba komai ai mun zama daya,rayuwa ce fa ni nasan wataran wa zai taimake ni? Kema kina taimako duk me taimako Allah baya hanashi sabo da haka karbi kawai.
Maheera karba tayi tana ta godiya tana jin dadi.
Washe gari Adnan ya samu Ibrahim yana masa magana akan Islaha lallai ya koreta ta bar musu gida taci mutuncinsa taci mutuncin matata.
Ibrahim yace Islaha kuma? Ae itace,
Gaskiya ba halinta bane kuma ma ai yarinya ce baka ganin bata da wayo kawai kayi hakuri zuwa wani lokaci su Sohail ne suke ziga ta,Adnan yace yarinyar nan bata da hankali fa,Ka dai dan kara hakuri tukun,fafur Ibrahim ya hana a kore ta shi baya ganin laifin Islaha sabo da sonta yake tsakani da Allah kuma burin aurenta yake.