Sashe 46
Min Qalb Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sake goggodewa juna sukayi tareda maganganu dangane da gadon da Khalil yabari shidai kawu baida tacewa hakadai suka kammala kafin aka Kira Salman ta waya yadawo ya daukesa Dan maidashi gida.
***Ahankali tasanyawa kanta hkr ta rungumi qaddarar rasuwar mijinta tareda rungumar Abinda Allah yabata ta maida hankali gurin renon cikinta Wanda kusan yanzu tsakanin itada umme da iyami da anty zarah sai oga kwata kwata MD ZABEERA ba'a San yafi qwallafawa cikin Rai ba,
Iyami tuni tafara siyan robar wankan jariri dasu kujeran zaunawa akai ayi Masa wanka harma dasu kayan yajin abincin me jego Wanda kullum lissatafinta kenan,
Umme ma Kam tuni akai nisa gurin tariyar kayan jarirai hardasu kayan wasansa,
Anty zarah kuwa kayan me jegon tafi maida hankali gurin Dan siya
Sai oga MD ZABEERA Wanda ya damesu ya shanye gurin Tara siyayyar kayan jarirai har wainda sai ya iya tafiya da gudu kafin yayi amfani dasu dan sunfi qarfin jariri Wanda daki guda ake Tara kayan acikin sashen Amatun duk yayi tafiya yadawo scan ake Kai kayan Wanda yasa Tunanin Yama fisu zautuwa wannan Rabin ran Anty zarah din.
Tsakaninta dashi gaisuwa ne shima sai idan anci sa'a sun hade by mistake sbd saitayi fiyeda wata ko wata biyuma Bata gansa ba sbd sosai yanzu yarage zama sai yawan tafiye tafiye,
Dr Salman kuwa yayi tafiya baya qasar tun cikinta na wata hudu yayi tafiyar Amma kusan kullum ayini shida USI batasan Wanda yafi wani kiraba,
Cikinta yanzu Yana wata na bakwai Wanda yayi girma Dan daidai ba laifi Wanda yasa qafafuwanta Dan kumbura kadan shiyasa ma kullum ake fita da ita haraba tana Dan zagayowa sbd Dr Fatima tace taringa motsawa tana Dan zagayowa.
Duk wani bayani da update Akan lafiyar cikin Dr Fatima MD ZABEERA take Fara Kira sbd agurinsu tamkar shine mahaifin Abinda za'a Haifa din and kowa yasan irin shaquwarta da qaunar dake tsakaninsa da 'dan uwansa kafin ya rasu so koba a fada musu ba sunsan Babu Wanda zai dauki responsibilities na cikin Bayan shi barema Kuma shine yabada wannan odar ta komai asanar dashi har ranar haihuwar ma'ana EDD dinta duk yasani.
Zaune suke apalo itada anty salamatu da sai umme datazo dubata and kwana biyu tunda tashiga wata na takwas take fama da ciwon Kai me tsanani Dr Fatima tayita dubata ta sanar musu da tana fama da matsalar high BP ne Wanda Dole suyi monitoring dinsa sbd idan bai sauka ba yakoma normal to yanada wahala ta iya haihuwa da kanta saidai CS.
Magani umme ta miqa Mata ahankali ta karba tareda karbar robar ruwan dake gabanta ta bude ahankali tana Dan lumshe ido sbd ko Ido ta bude sosai kanta kamar zai tsage,
Maganin ta shanye tana ajiye robar daidai Dr Fatima na shigowa palon daukeda sallama suka juya dukkaninsu suka kalleta suna Mata sannu da zuwa Banda Amatun data kasa ko bude idanuwanta dake lumshe sai kawai taji hancinta na shaqo Mata qamshin imperial majesty sama sama,
Bata bude idanuwanta ba sbd tasan baitaba shigowaba Kuma tasan baida dalilin dazai sashi shigowa din dan Daman da cikin yadamu bawai ita ba to Kuma Dr Fatima ma kafin tafada musu komai dangane da cikin saita fada Masa tuntuni haka suke Dan haka Bata sakaran akwai Abinda zai taba sanyashi shigowa....
MAHMOUD Kaine da kanka yau?""maganar umme data sanyata bude rufaffun idanuwanta cikin rashin sa'a sai acikin nasa daya zuba Mata akaro na farko daya kafeta idanuwansa Yana kallon cikinta daya Gama girma.
Cire idanuwanta cikin nasa tayi akaro na farko wata irin tsananin kunyarsa ya kamata sbd ganin irin kallon dayakewa cikinta
Ta 'dan muskuta ahankali tareda Dan Jan wuyar rigarta sama sbd budadden wuyane Dan doguwar rigace Mara nauyi Sam hannunta ma qarami ne irin na shimi.
Ahankali ya dauke kansa Yana zaunawa a kujerar dake fuskantar Tata ya kalli umme ya bude baki cikin yanayinsa na nutsuwa cikin sauti me taushi yace'
Barka da yau umme,
Na sameku lfy?
Lafiya kalau,
Yaushe kadawo ne Dan last time Dana tambaya zarah tacemin kana Turkish.
I came back this evening.
Allah sarki to sannu da hanya.
Thank you umme""ya furta cikin qaramin sauti sbd Sam kwata kwata rayuwarsa bai Saba da a nuna Masa kulawaba musamman daga gareta shiyasa yaji abin wani irin har baisan Yaya zai amsa Mata dinba Bayan da qananan kalmomi.
Kallon anty salamatu data kawo Masa drinks yayi tareda Dan girgiza Kai Yana cewa''
No thank you bana buqatan komai am ok.
Maida kallonsa yayi Kan umme cikin nutsuwa batareda ya kalli Amatu ba yace"
Umme Dr Fatima tayi bayanin komai dangane da yanayin da ita take ciki wanda yakamata asan asalin menene yasa takasa kwantar da hankalinta kodan sbd lafiyan Abinda yake tareda ita,
Meyasa bazaku fada Mata ta kwantar da hankalinta ba sbd high BP dinnan is a very serious issue and I can't.....sai yayi shiru yakasa qarasa fada ya 'dan kalli gefenta kadan tareda maida kallonsa Kan Dr Fatima yace"
Please make her understand illolin BP game ciki please.
Kallonsa Dr Fatima tayi kafin tajuyo ta kalli Amatun datake mamakin yanda Ashe dama Yana Magana haka sosai saidai maganar tasa tafi Kama da kamar ransa A 'dan bace yake.
Cikin damuwa ma umme itama tace"
Hakane kam Amatu Dan Allah ki cire damuwar idanma damuwar tsoron haihuwar kika saka aranki ki cire Zaki haihu lfy munanan munata Miki addua.
Idanuwanta be suka ciko da hawaye har suka Fara gangarowa Wanda yasa kowa zuba Mata idanuwansa cikin mamaki da damuwa,
Dr Fatima ce ta Kama hannunta tajata
daki tareda ce musu karsu damu zata Magana da Amatun zataji matsalarta.
Daki suka Shiga tareda rufo qofa suka bar su ummen zaune tsit cikin tsumayi.
Kiran wayarsa akayi ya miqe ya fice a natse tareda daukar wayar Yana Magana kamar bayason Yi ya nufi hanyar sashensu.
Kallon Amatu Dr Fatima tayi cikin nutsuwa da kulawa tace"
Amatu karki damu ni likitarki ce duk Abinda na tambaya kada kiji komai karki boye ki fadamin sbd lafiyanki da abindake cikinki mukeso Kuma kema nasan bazaki so komai yasameku ba, kinada matsalar da kikeji ne dangane da cikin?
Kokuma a jikinki?
Numfashi ta sauke tareda sauke kallonta daga Dr Fatima din ta bude bakinta dayayi nauyi tace"
Dr Fatima kaina ne ke tsananin ciwo sai Kuma kamar na daina Jin motsin cikin tun jiya.....
Kallonta Dr Fatima tayi da sauri cikin 'yar razana amm zamtowarta likita saita saki murmushi cikin kulawa da kwantarwa da Amatun hankali tace"
Jiya tun yaushe ne bakiji motsin ba?
Tun da yamma danaji bansake ji ba.
Sake wani murmushin me sauti tayi tareda dafa hannun Amatun tace"
Kinga wannan ba wani matsalane babba ba zamu duba mugani inshallah baby lafiyansa kalau
Bayan wannan menene Kuma matsalar?
Dagowa tayi ta kalleta kafin tayi qasa da Ido cikin damuwa tace"
Ciwon Mara saikuma gashi dazu Naga jini kadan kadan kaman Yana zuwa.
Kama ne kokuma kingani din?
Nagani""tafada Kai tsaye tana bayyanarda damuwarta.
Ok Amatu kinaji karki damu sosai Dan akan wannan insha Allah yanzu zanje dake asibiti zandubaki acan sbd Kinga gskia lokacin haihuwarki bai Isa yiba ana haihuwane at 36weeks zuwa 40weeks harma fiye amma ke Kinga yanzu kina cikin 33weeks atleast Koda za'ayi haihuwar gaggawa ne Kikai ko 35weeks haka so yanxu zanje dake asibiti zamu duba matsalar mugani Amma kema saikin taimaka kin rage damuwar komai aranki sbd Kinga damuwace tasaka BP dinki rising and hawan BP Kuma na iya leading to komai so please Amatu kicire damuwa inshallah komai zaizo yanda ake so ake Kuma fata kinji ko??
Ajiyar zuciya ta sauke ahankali kafin ta daga Kai tana cewa Inshallah Dr.
Dr Fatima ce kawai ta fito tabaro Amatun cikin daki dan tashirya tafito su tafi.
Zama Dr Fatima tayi ta fuskanci umme data zuba Mata Ido tana tsumayin jiran Abinda zata fada musu
ta Dan sauke numfashi cikin yanayi na damuwa kadan tace"
Gskia akwai matsala dangane da yanda tace batajin motsin cikin gakuma zuban jini datace Dan haka inaga asibiti zamu Bata gado ta kwanta mufara monitoring BP dinta da lafiyar babyn har musamu takai lokacin haihuwar saidaima bazance ga komaiba yanzu sainaje asibiti munyi scanning munkuma dubata mungani musan meye abinyi.
Ajiyar zuciya umme ta sauke jiki a mace yace"
To Allah yasa miji alkhairi
Min barwa Allah komai
Allah yayi Mana jagora.
Amin anty salamatu da Dr Fatima sukace Suma jiki amace.
Dr Fatima ce ta miqe tafara ficewa tana latsa Kiran MD Dan sanar Masa halinda ake ciki.
Cikin doguwar rigar jikinta ta fito sai dogon hijabin data sanyo.
Fitowa sukayi umme na riqeda hannunta sbd qafafuwanta dasuka kumbura sosai daqyar take takasu ga mararta datai nauyi tana Mata ciwo.
Baqar JUGUAR RANGE ROVER suka tarar pake a bakin qofar palon akunne sai qyalli take tana aiki duk da Basa ganin Wanda ke ciki kowannensu Saida ya ayyana MAHMOUD ZABEERA ne sbd shikadaine ke dukan irin wainnan motacin a zabeera duk da kowa na dukan kalar nasa arzikin.
Shine da kansa yake tuqa motar
Umme ta bude baya Amatun tashiga ahankali Yana kallonsu ta mirror kafin anty salamatu tashiga
Umme tace suje zataje ta shirya zatazo daga baya.
Jan motar yayi suka wuce Yana tuqin ahankali kamar Wanda ya dauko me naquda.
Koda suka Isa Dr Fatima ta shirya komai Nan take aka karbeta akai nufi labour room da ita Dan acan zasu dubata suyi Mata scanning.
Anty salamatu ana Shiga da Amatun ta daga waya takira kawu tafada Masa tana kashewa saiga Kiran iyami cewa gatanan zuwa.
Tashin farko suna Gama dube dubensu suka gano ruwan dake riqeda babyn saura kadan su Gama tsiyayewa gashi lokaci baiyiba Dan ko kadan Bata Fara budewar haihuwa ba suna saka ran saidai CS gashi Kuma lokaci baiyiba da saura Dan haka mun yanke zamu riqeta anan muna kulawa da lafiyarsu har zuwa Nanda sati biyu tashiga 35to 36weeks sai ayi aikin saidai gskia babyn zaizo ba qwari muna fatan yazamto rashin qwarin kawai sbd irin hakan babies din yawanci na zuwa da matsaloli"""Dr Fatima ce take fadawa MAHMOUD ZABEERA hakan acikin office dinta bayan tabaro Amatun gurin nurses suna shifting dinta zuwa dakinda zasu ajiyeta.
***Ahankali tasanyawa kanta hkr ta rungumi qaddarar rasuwar mijinta tareda rungumar Abinda Allah yabata ta maida hankali gurin renon cikinta Wanda kusan yanzu tsakanin itada umme da iyami da anty zarah sai oga kwata kwata MD ZABEERA ba'a San yafi qwallafawa cikin Rai ba,
Iyami tuni tafara siyan robar wankan jariri dasu kujeran zaunawa akai ayi Masa wanka harma dasu kayan yajin abincin me jego Wanda kullum lissatafinta kenan,
Umme ma Kam tuni akai nisa gurin tariyar kayan jarirai hardasu kayan wasansa,
Anty zarah kuwa kayan me jegon tafi maida hankali gurin Dan siya
Sai oga MD ZABEERA Wanda ya damesu ya shanye gurin Tara siyayyar kayan jarirai har wainda sai ya iya tafiya da gudu kafin yayi amfani dasu dan sunfi qarfin jariri Wanda daki guda ake Tara kayan acikin sashen Amatun duk yayi tafiya yadawo scan ake Kai kayan Wanda yasa Tunanin Yama fisu zautuwa wannan Rabin ran Anty zarah din.
Tsakaninta dashi gaisuwa ne shima sai idan anci sa'a sun hade by mistake sbd saitayi fiyeda wata ko wata biyuma Bata gansa ba sbd sosai yanzu yarage zama sai yawan tafiye tafiye,
Dr Salman kuwa yayi tafiya baya qasar tun cikinta na wata hudu yayi tafiyar Amma kusan kullum ayini shida USI batasan Wanda yafi wani kiraba,
Cikinta yanzu Yana wata na bakwai Wanda yayi girma Dan daidai ba laifi Wanda yasa qafafuwanta Dan kumbura kadan shiyasa ma kullum ake fita da ita haraba tana Dan zagayowa sbd Dr Fatima tace taringa motsawa tana Dan zagayowa.
Duk wani bayani da update Akan lafiyar cikin Dr Fatima MD ZABEERA take Fara Kira sbd agurinsu tamkar shine mahaifin Abinda za'a Haifa din and kowa yasan irin shaquwarta da qaunar dake tsakaninsa da 'dan uwansa kafin ya rasu so koba a fada musu ba sunsan Babu Wanda zai dauki responsibilities na cikin Bayan shi barema Kuma shine yabada wannan odar ta komai asanar dashi har ranar haihuwar ma'ana EDD dinta duk yasani.
Zaune suke apalo itada anty salamatu da sai umme datazo dubata and kwana biyu tunda tashiga wata na takwas take fama da ciwon Kai me tsanani Dr Fatima tayita dubata ta sanar musu da tana fama da matsalar high BP ne Wanda Dole suyi monitoring dinsa sbd idan bai sauka ba yakoma normal to yanada wahala ta iya haihuwa da kanta saidai CS.
Magani umme ta miqa Mata ahankali ta karba tareda karbar robar ruwan dake gabanta ta bude ahankali tana Dan lumshe ido sbd ko Ido ta bude sosai kanta kamar zai tsage,
Maganin ta shanye tana ajiye robar daidai Dr Fatima na shigowa palon daukeda sallama suka juya dukkaninsu suka kalleta suna Mata sannu da zuwa Banda Amatun data kasa ko bude idanuwanta dake lumshe sai kawai taji hancinta na shaqo Mata qamshin imperial majesty sama sama,
Bata bude idanuwanta ba sbd tasan baitaba shigowaba Kuma tasan baida dalilin dazai sashi shigowa din dan Daman da cikin yadamu bawai ita ba to Kuma Dr Fatima ma kafin tafada musu komai dangane da cikin saita fada Masa tuntuni haka suke Dan haka Bata sakaran akwai Abinda zai taba sanyashi shigowa....
MAHMOUD Kaine da kanka yau?""maganar umme data sanyata bude rufaffun idanuwanta cikin rashin sa'a sai acikin nasa daya zuba Mata akaro na farko daya kafeta idanuwansa Yana kallon cikinta daya Gama girma.
Cire idanuwanta cikin nasa tayi akaro na farko wata irin tsananin kunyarsa ya kamata sbd ganin irin kallon dayakewa cikinta
Ta 'dan muskuta ahankali tareda Dan Jan wuyar rigarta sama sbd budadden wuyane Dan doguwar rigace Mara nauyi Sam hannunta ma qarami ne irin na shimi.
Ahankali ya dauke kansa Yana zaunawa a kujerar dake fuskantar Tata ya kalli umme ya bude baki cikin yanayinsa na nutsuwa cikin sauti me taushi yace'
Barka da yau umme,
Na sameku lfy?
Lafiya kalau,
Yaushe kadawo ne Dan last time Dana tambaya zarah tacemin kana Turkish.
I came back this evening.
Allah sarki to sannu da hanya.
Thank you umme""ya furta cikin qaramin sauti sbd Sam kwata kwata rayuwarsa bai Saba da a nuna Masa kulawaba musamman daga gareta shiyasa yaji abin wani irin har baisan Yaya zai amsa Mata dinba Bayan da qananan kalmomi.
Kallon anty salamatu data kawo Masa drinks yayi tareda Dan girgiza Kai Yana cewa''
No thank you bana buqatan komai am ok.
Maida kallonsa yayi Kan umme cikin nutsuwa batareda ya kalli Amatu ba yace"
Umme Dr Fatima tayi bayanin komai dangane da yanayin da ita take ciki wanda yakamata asan asalin menene yasa takasa kwantar da hankalinta kodan sbd lafiyan Abinda yake tareda ita,
Meyasa bazaku fada Mata ta kwantar da hankalinta ba sbd high BP dinnan is a very serious issue and I can't.....sai yayi shiru yakasa qarasa fada ya 'dan kalli gefenta kadan tareda maida kallonsa Kan Dr Fatima yace"
Please make her understand illolin BP game ciki please.
Kallonsa Dr Fatima tayi kafin tajuyo ta kalli Amatun datake mamakin yanda Ashe dama Yana Magana haka sosai saidai maganar tasa tafi Kama da kamar ransa A 'dan bace yake.
Cikin damuwa ma umme itama tace"
Hakane kam Amatu Dan Allah ki cire damuwar idanma damuwar tsoron haihuwar kika saka aranki ki cire Zaki haihu lfy munanan munata Miki addua.
Idanuwanta be suka ciko da hawaye har suka Fara gangarowa Wanda yasa kowa zuba Mata idanuwansa cikin mamaki da damuwa,
Dr Fatima ce ta Kama hannunta tajata
daki tareda ce musu karsu damu zata Magana da Amatun zataji matsalarta.
Daki suka Shiga tareda rufo qofa suka bar su ummen zaune tsit cikin tsumayi.
Kiran wayarsa akayi ya miqe ya fice a natse tareda daukar wayar Yana Magana kamar bayason Yi ya nufi hanyar sashensu.
Kallon Amatu Dr Fatima tayi cikin nutsuwa da kulawa tace"
Amatu karki damu ni likitarki ce duk Abinda na tambaya kada kiji komai karki boye ki fadamin sbd lafiyanki da abindake cikinki mukeso Kuma kema nasan bazaki so komai yasameku ba, kinada matsalar da kikeji ne dangane da cikin?
Kokuma a jikinki?
Numfashi ta sauke tareda sauke kallonta daga Dr Fatima din ta bude bakinta dayayi nauyi tace"
Dr Fatima kaina ne ke tsananin ciwo sai Kuma kamar na daina Jin motsin cikin tun jiya.....
Kallonta Dr Fatima tayi da sauri cikin 'yar razana amm zamtowarta likita saita saki murmushi cikin kulawa da kwantarwa da Amatun hankali tace"
Jiya tun yaushe ne bakiji motsin ba?
Tun da yamma danaji bansake ji ba.
Sake wani murmushin me sauti tayi tareda dafa hannun Amatun tace"
Kinga wannan ba wani matsalane babba ba zamu duba mugani inshallah baby lafiyansa kalau
Bayan wannan menene Kuma matsalar?
Dagowa tayi ta kalleta kafin tayi qasa da Ido cikin damuwa tace"
Ciwon Mara saikuma gashi dazu Naga jini kadan kadan kaman Yana zuwa.
Kama ne kokuma kingani din?
Nagani""tafada Kai tsaye tana bayyanarda damuwarta.
Ok Amatu kinaji karki damu sosai Dan akan wannan insha Allah yanzu zanje dake asibiti zandubaki acan sbd Kinga gskia lokacin haihuwarki bai Isa yiba ana haihuwane at 36weeks zuwa 40weeks harma fiye amma ke Kinga yanzu kina cikin 33weeks atleast Koda za'ayi haihuwar gaggawa ne Kikai ko 35weeks haka so yanxu zanje dake asibiti zamu duba matsalar mugani Amma kema saikin taimaka kin rage damuwar komai aranki sbd Kinga damuwace tasaka BP dinki rising and hawan BP Kuma na iya leading to komai so please Amatu kicire damuwa inshallah komai zaizo yanda ake so ake Kuma fata kinji ko??
Ajiyar zuciya ta sauke ahankali kafin ta daga Kai tana cewa Inshallah Dr.
Dr Fatima ce kawai ta fito tabaro Amatun cikin daki dan tashirya tafito su tafi.
Zama Dr Fatima tayi ta fuskanci umme data zuba Mata Ido tana tsumayin jiran Abinda zata fada musu
ta Dan sauke numfashi cikin yanayi na damuwa kadan tace"
Gskia akwai matsala dangane da yanda tace batajin motsin cikin gakuma zuban jini datace Dan haka inaga asibiti zamu Bata gado ta kwanta mufara monitoring BP dinta da lafiyar babyn har musamu takai lokacin haihuwar saidaima bazance ga komaiba yanzu sainaje asibiti munyi scanning munkuma dubata mungani musan meye abinyi.
Ajiyar zuciya umme ta sauke jiki a mace yace"
To Allah yasa miji alkhairi
Min barwa Allah komai
Allah yayi Mana jagora.
Amin anty salamatu da Dr Fatima sukace Suma jiki amace.
Dr Fatima ce ta miqe tafara ficewa tana latsa Kiran MD Dan sanar Masa halinda ake ciki.
Cikin doguwar rigar jikinta ta fito sai dogon hijabin data sanyo.
Fitowa sukayi umme na riqeda hannunta sbd qafafuwanta dasuka kumbura sosai daqyar take takasu ga mararta datai nauyi tana Mata ciwo.
Baqar JUGUAR RANGE ROVER suka tarar pake a bakin qofar palon akunne sai qyalli take tana aiki duk da Basa ganin Wanda ke ciki kowannensu Saida ya ayyana MAHMOUD ZABEERA ne sbd shikadaine ke dukan irin wainnan motacin a zabeera duk da kowa na dukan kalar nasa arzikin.
Shine da kansa yake tuqa motar
Umme ta bude baya Amatun tashiga ahankali Yana kallonsu ta mirror kafin anty salamatu tashiga
Umme tace suje zataje ta shirya zatazo daga baya.
Jan motar yayi suka wuce Yana tuqin ahankali kamar Wanda ya dauko me naquda.
Koda suka Isa Dr Fatima ta shirya komai Nan take aka karbeta akai nufi labour room da ita Dan acan zasu dubata suyi Mata scanning.
Anty salamatu ana Shiga da Amatun ta daga waya takira kawu tafada Masa tana kashewa saiga Kiran iyami cewa gatanan zuwa.
Tashin farko suna Gama dube dubensu suka gano ruwan dake riqeda babyn saura kadan su Gama tsiyayewa gashi lokaci baiyiba Dan ko kadan Bata Fara budewar haihuwa ba suna saka ran saidai CS gashi Kuma lokaci baiyiba da saura Dan haka mun yanke zamu riqeta anan muna kulawa da lafiyarsu har zuwa Nanda sati biyu tashiga 35to 36weeks sai ayi aikin saidai gskia babyn zaizo ba qwari muna fatan yazamto rashin qwarin kawai sbd irin hakan babies din yawanci na zuwa da matsaloli"""Dr Fatima ce take fadawa MAHMOUD ZABEERA hakan acikin office dinta bayan tabaro Amatun gurin nurses suna shifting dinta zuwa dakinda zasu ajiyeta.