← Book details Min Qalb Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 42 OF 70

Sashe 42

Min Qalb Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Sosai anty zarah da anty salamatu ke kula da ita hakama kullum umme saitazo da kanta ta dubata musamman saka mutuwar arai datayi arai sosai sai lafiya take neman gagararta sbd kullum cikin zafin jiki da zazzabin dare take,
Modibbo da kansa kullum yake Kira yaji lafiyarta da kansa ba saqo ba shikuwa Andi kullum saiyayi musu aikin idan da Abinda Amatun ke buqata saidai Kuma MD ZABEERA baibar ko wace irin qofa dazasu buqaci wani abinba koyaushe buqatarsu cikakkiyace daga garesa duk da baitaba zuwa inda takeba rabon daya kalli ko inda sashen yake tun ranarda ta dawo.

Rasuwar 'dan uwansa ta dakesa sosai harsaida hakan ya taba himmarsa da jajircewarsa a aiki shiyasa take dukkanin iya qoqarinsa gurin cire tunanin wanzuwarta a zabeera yariga ya damqawa zarah komai na buqatar Amatun harta fita takaba Dan haka yagama komai baida sauran tunani akanta saima busy daya qara saka kansa zama Dan yanzu tafiye tafiyensa sundawo dama sbd Khalil ne dake takura Masa yasa yarage tafiye tafiyensa Amma yanzu Kam sai ya qarawa kansa yawan tafiye tafiyen.
##Mamuh#
*_'yan uwa inaga anan zamu tsaya sbd duba da azumi daya riga yazo inshallah saimu Bari idan Allah yabamu yawancin ran kaiwa bayan sallah saimu qarasa Inshallah._*
_NAGODE_*_MQ 32_*
Gyara zama anty zarah tayi tana sake qurawa fuskar Amatun datayi haske sosai Ido tana maida kallonta zuwa hannuwanta dasukai haske sosai har wani yellow yellow sukayi taji hankalinta nason tashi gabanta na faduwa ta maida kallonta Kan fuskarta tanabinta da kallo ko Ina har zuwa qasanta ta ajiye cup din furar da Amatun tasa aka kawo Mata tana cewa''
Amatu yanayinki na bani tsoro da rashin nutsuwa sbd yanayinki na nuna kamar bakida jini,
Ruwa idanuwanta ke qoqarin kawowa tana kallon fuskarta Amatun dake zaune ka kwantarda kanta jikin sofa idanuwanta a lumshe Wanda yanzu hakan yazama tamkar dabia gareta sbd aduk lokacinda ta zauna tayi shiru idanuwanta take lumshewa sbd tunanin rayuwarta data juya Mata kamar upside down Dan kuwa sai yanzu take sake tabbatarda rashin Dr khalil zabeera arayuwarta babbar gibi ce ga rayuwarta sbd shine farin cikinta, walwalarta,gatanta,burinta,alfaharinta, nutsuwarta gatanta dama asalinta gaba daya...

Hawayen datake riqewane suka gangaro daga cikin rufaffun idanuwanta Wanda yasa hankalin Anty zarah sake tashi tunanin qilan eh da gasken Amatun batada jinin tunaninta ya zama gaskia ta dafe goshi tana rintse ido cikin tsananin damuwa da firgici tace"
Amatu Dan Allah ki bude Ido kiyi magana wannan kukan naki na zuci Yana wahalardamu masu qaunarki,
A zabeera kaf gaba daya yanzu Babu Wanda akeji dashi ake tsananin qaunarsa fiyeda kowa kamarki sbd kece Abinda duniya gaba daya ta shaida Dr khalil zabeera naso fiyeda komai har rayuwarsa,
Damuwarki damuwar kowa ce,
Kukanki baqin cikin mune,
Amatu Dan Allah kiyi hkr ki dauki dangana tareda daukar qaddarar rashin Dr Khalil sbd ganinki ahaka na karya dukkanin qwarin gwiwar ummen khalil,
Yanzu Amatu bansan yazanyiba gaki da rashin lafiya ajikinki ta zazzabin dare kullum Amma kinki ko karban magani gashi yanzu Ina sakaran ko jini na neman gagararki Amatu meyasa,meyasa......hawaye ne suka katse Mata takasa qarasa maganar ta miqe da sauri zata bar gurin Amatu ta riqo hannunta ahankali tana bude idanuwanta dasukai jajir ta zubawa fuskar anty zarah din dake hawaye tanajin qaunarta tako Ina tana shigarta tareda tausayinsu su duka.

Jawota tayi ta maidata zaune tana kallon fuskarta ta tashi zaune ahankali tareda sake hannun anty zarah din tana dauke idanuwanta daga kallonta ahankali ta bude baki cikin yanayi na karyewar zuciya tace"
Anty zarah meyasa kike qaunata har haka?

Meyasa keda Dr kuke min irin wannan son haka?

Anty zarah kinsan arayuwata bantaba samun soyayya irinta Dr khalil zabeera ba,
Shine ya koyamin sonsa alokacinda zuciyata batasan wata soyayya ba saita kudi,
Shine yabani sunan mutunci da martabar mace,
Dr khalil zabeera yazabi soyayyata fiyeda komai da kowa,
Yasa zuciyata takamu da zazzafar soyayyarsa me wuyar Bari bare mantawa Amma yatafi ya barni a daidai lokacin da zuciyata batasan komai da kowaba bayanshi,
Meyasa yatafi yabarni anty zarah Ina tsananin buqatarsa.......

Rufe Mata baki anty zarah tayi tana girgiza Mata Kai hawayenta itama suna gudu tace"
Amatu kada kiyi sa6o ki dauki dangana shima da ana bada zabin mutuwa da bazai taba zabin barinki ba sbd bazaiso ganinki cikin irin wannan halin dakike cikiba yanzu..

Kiyi hkr ki rungumi hukuncin ubangiji akanku hakan da yayi shine daidai kizama me godewa ubangiji aduk halinda Kika tsintsi kanki.

Sauke Kai Amatun tayi hawayenta suka Gama gangarowa ta dago tana sharewa ta kalli anty zarah datake kallonta cikin tsananin damuwa ta sauke ajiyar zuciya ahankali tareda lumshe ido ta bude ta miqawa anty zarah din hannu tana kallon cup din furar data kawo Mata.

Da sauri anty zarah din ta dauki cup din ta Bata tana bayyanarda Jin Dadinta na sassautowa da Amatun tayi cikin guntun zumudi tace"
Thank you AMATULLAH.

Da sauri Amatun ta kalleta tana fasa Kai cup din bakinta sbd duk duniya Dr khalil dinta ne kawai ke Kiranta da cikakken sunanta AMATULLAH.

Fuskewa anty zarah tayi tana qaqalo murmushi ganin tana neman dawo da gaba baya tace"
Banma iya fadar sunan yayi Dadi ba kaman yanda ake fada.

Ganin tashiga kame kamen fadar sunan datayi yasa Amatu sake sauke ajiyar zuciya tana Kai cup din bakinta
tana kurba ahankali ta lumshe ido tana gyara jinginawarta
sbd dadi dakuma karbuwa dataji bakinta da cikinta sunayi da furar saita saki jiki tanasha ahankali furan na sake sanyata lumshe ido.

Anty zarah ganin yanda furan tasamu karbuwa sosai agun Amatun yasata miqewa da sauri ta nufi fridge ta dauko gaba daya jug din furan ta dawo dashi ta ajiye gaban Amatun tana cewa''
Kawo cup din aqara zubawa Kisha
Dama nasan zakiji Dadinta sbd har sabuwar Madara na zuba Miki aciki.

Qara Mata tayi takuma shanyewa Saida ta shanye kusan cup uku kafin tace ta Isa abarta haka.

Cikin Jin Dadi anty zarah tagyara zama tana Mata fira ahankali tana matsa Mata qafafunta dasuka Dan kumbura sbd zama guri daya
Ahaka har bacci ya dauketa cikin nutsuwa Wanda rabonta da irinsa tun kafin rasuwar mijinta sai yau.

Gyara Mata kwanciya zarah tayi kafin ta zame ta fice daga part din gaba daya takoma nasu Nan ma wani aikin tahau sbd MAHMOUD datake saka ran
dawowarsa ayau din duk da gaba daya yinin ranar basuyi wayaba dama itace tafi Kira to itakuma yau ganin yanayin sauyin jikin Amatu yasa hankalinta yadan dauku ko yanzu tana ganin kamar hasashenta gaskia ne Amatu na buqatar ganin likita jikinta bai nuna tana lafiyaba
Dole zata fadawa umme kokuma MD idan yadawo yau asan nayi kada wani ciwo ya kamata basuda masaniya.

Aikin gyare gyare da girki suka hau Yi itada hafsatu sbd tuntuni ta zauna tayi nazari zata dauki shawarar Amatu ta kawo gyara arayuwar aurenta da tsakaninta da mijinta,
Zata cire shakku da tsoron mijinta ta fuskanci reality rayuwar aure sukeyi ba zaman darasiba Dan haka zata sauya kanta ta sauya zamantakewarta da MAHMOUD ZABEERA kada tayi sake lokaci ya qure Mata.

Sai yamma suka Gama komai tayi wanka ta sanya doguwar riga ta atampa tareda yafa qaramin qyale akanta ta hada abincin data dibarwa amatu ta jera a tray hafsatu ta dauka suka nufi can.

Koda suka shiga futowarta wanka kenan itama ta sanyo riga da skirt na atampa ta sanya.,
Abin mamaki maimakon taji kayan sun Mata yawa sbd Rama saitaji kamar skirt din ya kamata hakama rigar.

Kallon anty zarah dake kallonta cikin yanayi na tunanin dabasanma na menene ba haka kawai idan tana kallon Amatu wani lokacin saita Shiga tunanin yanzu saime Kuma zaizo gaba a rayuwar Amatun.

Anty zarah kina ganin na qara jiki ne kokuwa nece naji hakan?

Numfashi anty zarah din ta sauke tana matsowa gaban Amatun ta Dan ja rigarta daga gefe gefe taji ba wani space tasaki murmushi tana cewa''
Gskia baki wani qara ba inaga sbd dai kin Dade baki sakasu bane shiyasa gashi bakida wasu tsofin kayan bare kisaka Amma kiyi hkr kiyi manage tunda ba abin ado bane Kuma ba fita zakiyi ba bare kice Zaki takura.

Gyada kanta tayi tana sanyawa kanta hula Mara nauyi ta Dan saki fuska ta qaqalo murmushin yaqe sbd faranta ran Anty ZARAn tace"
Anty zarah wannan qamshin na Rabin ranki ne?

Sbd nasan shi kadaine akewa wannan Shirin na musamman.

Kasa boyuwa farin cikin anty zarah yayi ta saki annushuwa sosai tana cewa''
Amatun kin bawa MAHMOUD sunan Dole Wanda harya zauna cikin kaina Nima RABIN RAN ANTY ZARAH.

Falo suka fito suna cigaba da Dan fira sama sama sbd karta zaqe da yawa ganin Amatun tafara sakewa.

Suna zama tace"
Anty zarah kokinsan meyasa idon mutum ke nauyi wani lokacin kamar zasu juye ga ciwon Kai me tsanani???

Kallonta da kyau zarah tayi kafin tace"
Kinajin hakan ne?

Gyada Kai tayi ahankali tana cewa"
Qila sbd kukan danakeyi ne koyaushe.

Aa Amatu ba lallai hakan bane ni nafi zargin rashin ishashen jini atare dake kibari Akira likiti ya dubaki.

Ba buqatan hakan anty kawai daima yanzu Kwan biyun Nan nadainajin nauyin idon ciwon Kai me tsanani yafi damuna idan akwai maganin ciwon Kai kawai kiban danasha shikenan zanji sauqinsa Inshallah.

Akwai ibuprofen agurina Yana maganin ciwon Kai sosai yanxu idan na koma xan aiko hafsatu takawo Miki kisha kafin ki kwant kafin safe zakiji wasai.

Nagode anty zarah Allah yabarki da Rabin ranki yabaki zuciyarsa.

Wata Yar dariyar farin ciki tasaki tana qoqarin dasawa zuciyarta zancen ta hanyar cewa amin saidai Kuma wani sashen na zuciyar na ganin kamar da wuya samun zuciyar MD ZABEERA koba agurinta ba ko agurin kowama.

Salman ne yashigo palon daukeda babbar ledar fresh fruits da ledar gasassun kifin dasuka gasu cikin source din veg chips sai qamshi sukeyi.

Da kallo dukkaninsu suke binsa har su hafsatu suka karbi kayan hannunsa sukai kicin dasu Dan zubowa a tray ya qaraso ya zauna gefen anty zarah Yana kujerar dake kallon ta Amatu Yana kallonta cikin yanayi na tsananin kulawa Yana tambayarta Yaya take
Ta amsa Masa cikin yanayin sake bawa kanta qwarin gwiwa sbd su masoyanta dasuka damu kansu akan damuwarta.
Chapter 42 · 0% Book details