Sashe 3
Min Qalb Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Atare suka girgiza Kai itada Usman din suna kallon juna idanuwansu na cikowa da hawaye.
Nasan zaa rina yafada cikin ransa Yana kallonsu zuciya a karye.
Kamo hanun Usman yayi yajasa gefe ya fahimtar dashi sosai ta yanda zai gane Abinda yake nufi
Harya gane Yakuma amince sbd har abada bazaiso Abinda zai samu amatu ba.
Daga haka suka hakura sunaji suna gani suka rabu da juna kawu yatafi da su kafin daga baya Usman yadawo makarantar malam.
Tunda amatu tadawo gidan kawu Bata taba haduwa da tsangwama ba saidai Kuma babuwa wani janta ajiki da iyami tayi.
Basuda qarfi sai rufin asiri da haka malam yasakata primary school dinda yake gadi wadda tuni aka maidata 'yar maigadi.
Usman shekara daya yayi batareda itaba ya tattara karatun yadawo gidan kawu Yana kwana a soro komai tsananin sanyi da zafi kuwa.
A haka kawu yasamar Masa aikin tsaron gidan wanka da bahaya a Tasha har Shima yashiga primary 2
Yana shiga primary 5 ya tattara karatun ya ajiye sbd gwagwarmayar rayuwa.
Kawu da iyami sune gatansu na farko,
Kawu da iyami sune wainda suka cirosu daga bola suka basu sunanda ake kallonsu da daraja ayanzu.
Shekakarda tashiga js 2 a shekarar suka shiga wata sabuwar masifar da akayiwa kawu sharrin satar cire winduna da qofofin makaranta ya siyar.
Duk inda ake zuwa roqo da Kai kuka sunkai akan alamarin Amma Abu ya agagara qarshe dpo nunawa yayi sai idan ita amatu kokuma matar kawun zasu kwana dashi tukuna zai taimakesu.
Akaro na farko da amatu ta tsani maza da taimakonsu.
Ranar dukkaninsu kwana sukayi kukan baqin ciki sunaji suna gani akayi gidan yari da kawu hukuncin shekara biyu dama Kuma abin hadda gayya sbd Shima alqali yaso amatun tabasa hadin Kai sbd irin wankewa da jikinta yayi gashi fatarta Ashe me irin hasken Nan ce ga jikinta daya gama fitowa ana mace tsaf yanzu iyakaci qarasa balagewa ne dabatayiba a cikakkiyar mace.
Tunda akayi gidan yari da kawu alamarin duniya yasakosu gaba ko abincinda zasuci ya gagaresu dole Usman ne yanaji Yana gani yake fita gwagwarmaya Amma sai ahankali.
Wata bakwai da zuwan kawu gidan yari aka koresu daga gidan dasuke suka rasa gurin zuwa ga iyami Dan cikinsa take dauke dashi wahala tasaka ya bare ko kudin asibiti basuda.
Akaro na farko da Usman yakoma sata kenan arayuwarsa ya kama musu daki buyi a wani gidan haya me dakuna goma reras a jere kamar shaguna,
Gidanda ya hada mutane dabam dabam masu halaye dabam dabam.
#mamuh#
MIN QALB
Mamuhgee
ZAFAFA BIAYAR
SIRADIN RAYUWA
safiyya huguma
MIN QALB
mamuhgee
YANKAN BAYA
billyn Abdul
KIBIYAR AJALI
Miss xoxo
ABINDAKE CIKIN ZUCIYATA
hafsat rano
Pay @09033181070
Or 09032345899
[3/4, 12:14 AM] Zafafa: *_MIN QALB 3_*
_mamuhgee_
_Min qalb Na kudine_
Daki 'daya ya dauka iyami da amatu suka dauka daya
Sabuwar rayuwa suka Fara a gidan inda ake zaman rashin nasiha da ragawa juna,
Sam gidan kowa ta kansa yakeyi Babu Mai ta6uwa kowa ka taba Babu sauki sai masifa.,
Hakan yasa suma ahankali rayuwa ta koya musu yanda take,
Sunaji suna gani itama amatu ta ajiye karatu suka fada gwagwarmayar neman abin rufawa Kai asiri,
Amatu da iyami suka bazama neman ayuka
Ita iyami tasamu aikin abincin wata makaranta amatu Kuma tasamu aiki bookshop din wata iyamura.
Bata wani jima tana aiki gurinba saigashi Shima Usman aka kamasa aka rufe kusan wata biyu ga iyami ma tana fama da ciwon diabetes sai kawai tace Mata ta ajiye aikin abincin makarantar kada taji ciwo al'amarin yaqara lalace musu.
Hakan yasa nauyi yahau kanta na kulada iyami damuma nauyin ci da shansu.
Rayuwa da lokaci sune suka koyar da ita darussa da dama wanda ayanxu take musu kallon fahimta,
Tunda lalurar nauyin ahalinsu tadawo kanta Bata taba samun Wanda yadubeta da fuskar taimakawaba kowa da wata mummunar manufa yakeson taimaka mata,
Ansha niyar lalatar Mata da rayuwa tana tserata,
Ansha wulaqantata akan ana Mata kallon fandararriya Mara asali,
A ranarda wani yayi niyar lalatar Mata da rayuwa ta dole da niyar zai taimaka musu aranar ne zuciyarta ta gama qanqansewa da duk wani alamarin mutanen duniya
Shiyasa take Kiran kanta da furen kan juji.
Iyami ma hakan yasake busar Mata da zuciyar zata nemi kudi kota yayane Banda haram,
Babban Abinda ke qara kawo tabarbarewar zaman lafiyarmu shine hukunci akan Wanda hukuncin laifinsa bai Kai ba shike kawo sauyawar tunani da zuciya,
To kusan hakance tafaru da ahalin kawu,
Bayan fitowar Usman tuni zuciyarsa ta gama kangarewa sbd rufesan da akayi suncire Masa tsoron gidan yari Kuma,
Rayuwarsu tadawo sabuwa,
Burinsu shine kudi,
Farin cikinsu shine kudi,
Mafarkinsu shine kudi,
Mafarkinsu shine kudi
Idan har kudi suke Hana Dan Adam wulaqanta da tozarta tareda azabta Irin wadda suka taso suka rayu acikinta to tabbas sun shirya samun kudi Koda na wani ne.
Basu sake jinjinawa alamarin kudi ba Saida sukayi belin kawu da kudi naira dubu dari bayan yayi shekara daya da wata Tara gidan yari.
Babban al'amarinda ya shallake tunanin abokan zamansu na gidan hayan shine qarmashewar da zuciyar kawu tayi fiyeda ta kowa acikinsu game da kudi,
Yana fitowa gidan yari Abinda yafara fada afili shine'"
Idan har kudi sune maganin wulaqanci da toxarci tareda maganin wani baqin ciki to tabbas burina yanxu shine kudi,
Kudinma ba qananun ba manya nake buri.
Shekaru sunja sosai alamura sunyi haske sosai a rayuwarsu sbd kowa yanada hanyoyin samun kudinsa,
Acikin gidansu dake cike tab da 'yan haya to tabbas Babu me masifa da fitinar kawu,
Bayada sauki ko kadan Dan babu ubanda yake ragarwa a gidan ciki kuwa harda alhaji mande me gidan,
Duk masifaffun gidan suna shafawa kawu lafiya sbd fitinarsa Amma shikuma iyami ce kawai daidai dashi sbd ko atsakaninsu basawa juna nasiha ko sauqi.
Damuwa,kuka,kunci,baqin ciki,takaici,tuna baya
Wainnan duk wasu abubuwane dasuka binne a bayan rayuwarsu,
Sun koya su ciyar da kansu tun basusan kan nasuba,
Sun koya tsayawa da qafafunsu da junansu tun basusan meye duniyar ta qunsaba,
Sunyi yaqi da wahala da yunwa tareda azabta su kadai batareda wani ya tallafesuba,
Sun yakice tsoro tun basusan meye tsoronba
Dan haka su aduk yanda rayuwa tazo musu yanzu basuda damuwa da ita sbd sunsan babu wata gwagwarmayar data fi wannan din.
Wannan shine rayuwarsu,
Rayuwar 'yancin Kai rayuwarda baduda burin komai cikinta saina suji Dadi su dawwama da juna acikinsa.
AMATULLAH yanxu rayuwarta takeyi cikin jin Dadi da walwala,
Babu Abinda ya dameta face taji dadin rayuwa tareda ahalinta data keda burin su samu duniya suji dadinsu,
Duk inda tasamu aiki Bata jimawa ake watsewa sbd halayenta na Babu Abinda ya dameta bayan shiririta da yin duk Abinda taga dama
Duk Wanda yayi gigin shiga huruminta kuwa Yara take sawa qanana su koyawa mutum hankali kokuma usi Wanda beda aikin yi yanxu sai yawon banza sai idan ansamu na sanfewa a sanfe.
Amatu kyakkyawar cikakkiyar budurwace yanxu wadda tagama hada komai musamman kyawun jiki da fuska.
Maza ko gigin zuwa nemanta basayi sbd a duniya idan akwai Abinda ta tsana fiyeda komai to mazane idan aka cire usi dinta da kawunta.
Kana cewa kana sonta zata saka ahada maka jini da majina Wanda usi ne me aikin shida wasu abokanansa.
Ayanxu Kam sunsan duniya sunkuma darassantu da iliminda tabasu shiyasa akoda yaushe ashirye suke da duk sabon darasinda zata kawo.
AMATULLAH K SALEH shine cikakken sunanta Wanda kawu yabata aranar da yafara kaita makaranta,
Usman K saleh 'dan uwantane da aduniya babu Abinda takeso da qauna sama dashi,
Zata iya sadaukarda rayuwarta data Bari wani abu ya samesa,
Hakama zata iya sadaukarda komai sbd shi sbd sunawa juna kallon uwa daya uba daya suke ko kawu baitaba sanin ba uwa daya uba dayane ya haifesuba duk da Shima bakowane yasan cewa bashine mahaifinsu ba musamman da kusan halayen amatu duk nasa ne na rashin hakuri ko kadan,
Acikin su hudu kuwa baasan waye yafi wani son kudi da abun duniyaba shiyasa ake musu laqabi da dangin tsamiya.
Arayuwarta tayi aiki kala dabam dabam zai Kai goma koma fiye Wanda takeyi yanxu a restaurant shine kusan na sha daya
Hakama kawu yayi sanaoin harya gaji Amma yaqi kudi shiyasa ya tattara ya watsar yakoma zaman saka ido da jiran Wanda tsautsayi zaisa ya tabasa yaga masifa tareda siyan radio yakoma Shan waqe waqen gargajiya wanda kowa naji ba halin mgn sbd Shima ubanda zai tanka dinyake nema Amma haka kowa ke dannewa sbd azauna lfy duk da gidan kullum cikin fada da hayaniya ake.
****
Qarar waqar sani sabulu ce ta _duniya wandon roba_ ta cika gidan ta karade
wane daki da saqo na gidan sbd qarar muryar radio din da aka Kai qarshe gaba daya.
Hankalinsa kwance yake yana Shan waqarsa Yana sakace haqoransa da tsinke
Daka gansa zakasan babu Abinda ya damesa.
Dukkanin mutanen gidan 'dai 'dai suka ringa fitowa rayukansu a 'bace da takaicinsa na kullum Wanda inda sabo sun Saba da dabi'arsa ta tayardasu kullum da sautin radionsa da muryarsa Bata qasa
Gashi bamai ikon mgn 'yar gaban goshinsa da shaqiyin dansa suce ba Wanda ya isa
Amma rshin arzikinsu babu kalar Wanda basa fafatawa dashi wanda kallo daya zakayi musu kasan su din abin mamaki ne,
Rayuwarsu abin kallo ce sbd sudin abin mamakine.
Yana ganin mutanen gidan sunfara fitowa ya sake dauke Kai sama Yana jiran yaji wani Mai shafaffun Mai akai ne zaiyi mgn ya sauke Masa masifar dake cinsa ta takaicin iyami daya kwana dashi na biya Masa bashin dabaiyi niyar biyaba yanzu da kudinda yaci burin canza radio dashi na AMATULLAH da USI.
Cikin bacci qarar radio din ke shigarta Yana damunta,
Juya kwanciyarta tayi tana toshe kunnuwanta da pillow Amma
Sam qarar Bata daina shiga kunnuwanta ba.
Tsoki tasaki ahankali tana cewa'
Kawuuuu.
Saidata sake rintsawa ta juya kwanciyarta tsawon minti goma Amma Sam baccin ya gagara sbd qarar radio din dole ta yaye lullubinta ta miqe zaune tana miqa tana cewa'
Allah yasa yanda natashi yau cikin qoshin lfy
yasa yau ranar sa'atace,
Allah yasa yauma na hadu da irin hajiyar Dana hadu da ita jiya nayi mata kukan tausayi tabani kudinda zanyo......
Nasan zaa rina yafada cikin ransa Yana kallonsu zuciya a karye.
Kamo hanun Usman yayi yajasa gefe ya fahimtar dashi sosai ta yanda zai gane Abinda yake nufi
Harya gane Yakuma amince sbd har abada bazaiso Abinda zai samu amatu ba.
Daga haka suka hakura sunaji suna gani suka rabu da juna kawu yatafi da su kafin daga baya Usman yadawo makarantar malam.
Tunda amatu tadawo gidan kawu Bata taba haduwa da tsangwama ba saidai Kuma babuwa wani janta ajiki da iyami tayi.
Basuda qarfi sai rufin asiri da haka malam yasakata primary school dinda yake gadi wadda tuni aka maidata 'yar maigadi.
Usman shekara daya yayi batareda itaba ya tattara karatun yadawo gidan kawu Yana kwana a soro komai tsananin sanyi da zafi kuwa.
A haka kawu yasamar Masa aikin tsaron gidan wanka da bahaya a Tasha har Shima yashiga primary 2
Yana shiga primary 5 ya tattara karatun ya ajiye sbd gwagwarmayar rayuwa.
Kawu da iyami sune gatansu na farko,
Kawu da iyami sune wainda suka cirosu daga bola suka basu sunanda ake kallonsu da daraja ayanzu.
Shekakarda tashiga js 2 a shekarar suka shiga wata sabuwar masifar da akayiwa kawu sharrin satar cire winduna da qofofin makaranta ya siyar.
Duk inda ake zuwa roqo da Kai kuka sunkai akan alamarin Amma Abu ya agagara qarshe dpo nunawa yayi sai idan ita amatu kokuma matar kawun zasu kwana dashi tukuna zai taimakesu.
Akaro na farko da amatu ta tsani maza da taimakonsu.
Ranar dukkaninsu kwana sukayi kukan baqin ciki sunaji suna gani akayi gidan yari da kawu hukuncin shekara biyu dama Kuma abin hadda gayya sbd Shima alqali yaso amatun tabasa hadin Kai sbd irin wankewa da jikinta yayi gashi fatarta Ashe me irin hasken Nan ce ga jikinta daya gama fitowa ana mace tsaf yanzu iyakaci qarasa balagewa ne dabatayiba a cikakkiyar mace.
Tunda akayi gidan yari da kawu alamarin duniya yasakosu gaba ko abincinda zasuci ya gagaresu dole Usman ne yanaji Yana gani yake fita gwagwarmaya Amma sai ahankali.
Wata bakwai da zuwan kawu gidan yari aka koresu daga gidan dasuke suka rasa gurin zuwa ga iyami Dan cikinsa take dauke dashi wahala tasaka ya bare ko kudin asibiti basuda.
Akaro na farko da Usman yakoma sata kenan arayuwarsa ya kama musu daki buyi a wani gidan haya me dakuna goma reras a jere kamar shaguna,
Gidanda ya hada mutane dabam dabam masu halaye dabam dabam.
#mamuh#
MIN QALB
Mamuhgee
ZAFAFA BIAYAR
SIRADIN RAYUWA
safiyya huguma
MIN QALB
mamuhgee
YANKAN BAYA
billyn Abdul
KIBIYAR AJALI
Miss xoxo
ABINDAKE CIKIN ZUCIYATA
hafsat rano
Pay @09033181070
Or 09032345899
[3/4, 12:14 AM] Zafafa: *_MIN QALB 3_*
_mamuhgee_
_Min qalb Na kudine_
Daki 'daya ya dauka iyami da amatu suka dauka daya
Sabuwar rayuwa suka Fara a gidan inda ake zaman rashin nasiha da ragawa juna,
Sam gidan kowa ta kansa yakeyi Babu Mai ta6uwa kowa ka taba Babu sauki sai masifa.,
Hakan yasa suma ahankali rayuwa ta koya musu yanda take,
Sunaji suna gani itama amatu ta ajiye karatu suka fada gwagwarmayar neman abin rufawa Kai asiri,
Amatu da iyami suka bazama neman ayuka
Ita iyami tasamu aikin abincin wata makaranta amatu Kuma tasamu aiki bookshop din wata iyamura.
Bata wani jima tana aiki gurinba saigashi Shima Usman aka kamasa aka rufe kusan wata biyu ga iyami ma tana fama da ciwon diabetes sai kawai tace Mata ta ajiye aikin abincin makarantar kada taji ciwo al'amarin yaqara lalace musu.
Hakan yasa nauyi yahau kanta na kulada iyami damuma nauyin ci da shansu.
Rayuwa da lokaci sune suka koyar da ita darussa da dama wanda ayanxu take musu kallon fahimta,
Tunda lalurar nauyin ahalinsu tadawo kanta Bata taba samun Wanda yadubeta da fuskar taimakawaba kowa da wata mummunar manufa yakeson taimaka mata,
Ansha niyar lalatar Mata da rayuwa tana tserata,
Ansha wulaqantata akan ana Mata kallon fandararriya Mara asali,
A ranarda wani yayi niyar lalatar Mata da rayuwa ta dole da niyar zai taimaka musu aranar ne zuciyarta ta gama qanqansewa da duk wani alamarin mutanen duniya
Shiyasa take Kiran kanta da furen kan juji.
Iyami ma hakan yasake busar Mata da zuciyar zata nemi kudi kota yayane Banda haram,
Babban Abinda ke qara kawo tabarbarewar zaman lafiyarmu shine hukunci akan Wanda hukuncin laifinsa bai Kai ba shike kawo sauyawar tunani da zuciya,
To kusan hakance tafaru da ahalin kawu,
Bayan fitowar Usman tuni zuciyarsa ta gama kangarewa sbd rufesan da akayi suncire Masa tsoron gidan yari Kuma,
Rayuwarsu tadawo sabuwa,
Burinsu shine kudi,
Farin cikinsu shine kudi,
Mafarkinsu shine kudi,
Mafarkinsu shine kudi
Idan har kudi suke Hana Dan Adam wulaqanta da tozarta tareda azabta Irin wadda suka taso suka rayu acikinta to tabbas sun shirya samun kudi Koda na wani ne.
Basu sake jinjinawa alamarin kudi ba Saida sukayi belin kawu da kudi naira dubu dari bayan yayi shekara daya da wata Tara gidan yari.
Babban al'amarinda ya shallake tunanin abokan zamansu na gidan hayan shine qarmashewar da zuciyar kawu tayi fiyeda ta kowa acikinsu game da kudi,
Yana fitowa gidan yari Abinda yafara fada afili shine'"
Idan har kudi sune maganin wulaqanci da toxarci tareda maganin wani baqin ciki to tabbas burina yanxu shine kudi,
Kudinma ba qananun ba manya nake buri.
Shekaru sunja sosai alamura sunyi haske sosai a rayuwarsu sbd kowa yanada hanyoyin samun kudinsa,
Acikin gidansu dake cike tab da 'yan haya to tabbas Babu me masifa da fitinar kawu,
Bayada sauki ko kadan Dan babu ubanda yake ragarwa a gidan ciki kuwa harda alhaji mande me gidan,
Duk masifaffun gidan suna shafawa kawu lafiya sbd fitinarsa Amma shikuma iyami ce kawai daidai dashi sbd ko atsakaninsu basawa juna nasiha ko sauqi.
Damuwa,kuka,kunci,baqin ciki,takaici,tuna baya
Wainnan duk wasu abubuwane dasuka binne a bayan rayuwarsu,
Sun koya su ciyar da kansu tun basusan kan nasuba,
Sun koya tsayawa da qafafunsu da junansu tun basusan meye duniyar ta qunsaba,
Sunyi yaqi da wahala da yunwa tareda azabta su kadai batareda wani ya tallafesuba,
Sun yakice tsoro tun basusan meye tsoronba
Dan haka su aduk yanda rayuwa tazo musu yanzu basuda damuwa da ita sbd sunsan babu wata gwagwarmayar data fi wannan din.
Wannan shine rayuwarsu,
Rayuwar 'yancin Kai rayuwarda baduda burin komai cikinta saina suji Dadi su dawwama da juna acikinsa.
AMATULLAH yanxu rayuwarta takeyi cikin jin Dadi da walwala,
Babu Abinda ya dameta face taji dadin rayuwa tareda ahalinta data keda burin su samu duniya suji dadinsu,
Duk inda tasamu aiki Bata jimawa ake watsewa sbd halayenta na Babu Abinda ya dameta bayan shiririta da yin duk Abinda taga dama
Duk Wanda yayi gigin shiga huruminta kuwa Yara take sawa qanana su koyawa mutum hankali kokuma usi Wanda beda aikin yi yanxu sai yawon banza sai idan ansamu na sanfewa a sanfe.
Amatu kyakkyawar cikakkiyar budurwace yanxu wadda tagama hada komai musamman kyawun jiki da fuska.
Maza ko gigin zuwa nemanta basayi sbd a duniya idan akwai Abinda ta tsana fiyeda komai to mazane idan aka cire usi dinta da kawunta.
Kana cewa kana sonta zata saka ahada maka jini da majina Wanda usi ne me aikin shida wasu abokanansa.
Ayanxu Kam sunsan duniya sunkuma darassantu da iliminda tabasu shiyasa akoda yaushe ashirye suke da duk sabon darasinda zata kawo.
AMATULLAH K SALEH shine cikakken sunanta Wanda kawu yabata aranar da yafara kaita makaranta,
Usman K saleh 'dan uwantane da aduniya babu Abinda takeso da qauna sama dashi,
Zata iya sadaukarda rayuwarta data Bari wani abu ya samesa,
Hakama zata iya sadaukarda komai sbd shi sbd sunawa juna kallon uwa daya uba daya suke ko kawu baitaba sanin ba uwa daya uba dayane ya haifesuba duk da Shima bakowane yasan cewa bashine mahaifinsu ba musamman da kusan halayen amatu duk nasa ne na rashin hakuri ko kadan,
Acikin su hudu kuwa baasan waye yafi wani son kudi da abun duniyaba shiyasa ake musu laqabi da dangin tsamiya.
Arayuwarta tayi aiki kala dabam dabam zai Kai goma koma fiye Wanda takeyi yanxu a restaurant shine kusan na sha daya
Hakama kawu yayi sanaoin harya gaji Amma yaqi kudi shiyasa ya tattara ya watsar yakoma zaman saka ido da jiran Wanda tsautsayi zaisa ya tabasa yaga masifa tareda siyan radio yakoma Shan waqe waqen gargajiya wanda kowa naji ba halin mgn sbd Shima ubanda zai tanka dinyake nema Amma haka kowa ke dannewa sbd azauna lfy duk da gidan kullum cikin fada da hayaniya ake.
****
Qarar waqar sani sabulu ce ta _duniya wandon roba_ ta cika gidan ta karade
wane daki da saqo na gidan sbd qarar muryar radio din da aka Kai qarshe gaba daya.
Hankalinsa kwance yake yana Shan waqarsa Yana sakace haqoransa da tsinke
Daka gansa zakasan babu Abinda ya damesa.
Dukkanin mutanen gidan 'dai 'dai suka ringa fitowa rayukansu a 'bace da takaicinsa na kullum Wanda inda sabo sun Saba da dabi'arsa ta tayardasu kullum da sautin radionsa da muryarsa Bata qasa
Gashi bamai ikon mgn 'yar gaban goshinsa da shaqiyin dansa suce ba Wanda ya isa
Amma rshin arzikinsu babu kalar Wanda basa fafatawa dashi wanda kallo daya zakayi musu kasan su din abin mamaki ne,
Rayuwarsu abin kallo ce sbd sudin abin mamakine.
Yana ganin mutanen gidan sunfara fitowa ya sake dauke Kai sama Yana jiran yaji wani Mai shafaffun Mai akai ne zaiyi mgn ya sauke Masa masifar dake cinsa ta takaicin iyami daya kwana dashi na biya Masa bashin dabaiyi niyar biyaba yanzu da kudinda yaci burin canza radio dashi na AMATULLAH da USI.
Cikin bacci qarar radio din ke shigarta Yana damunta,
Juya kwanciyarta tayi tana toshe kunnuwanta da pillow Amma
Sam qarar Bata daina shiga kunnuwanta ba.
Tsoki tasaki ahankali tana cewa'
Kawuuuu.
Saidata sake rintsawa ta juya kwanciyarta tsawon minti goma Amma Sam baccin ya gagara sbd qarar radio din dole ta yaye lullubinta ta miqe zaune tana miqa tana cewa'
Allah yasa yanda natashi yau cikin qoshin lfy
yasa yau ranar sa'atace,
Allah yasa yauma na hadu da irin hajiyar Dana hadu da ita jiya nayi mata kukan tausayi tabani kudinda zanyo......