Sashe 41
Min Qalb Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Zamewa tayi ta zube qasa tareda sakin wani irin gigitaccen kuka me qarfi dayasa asibitin suka qara daukar shiru kowa na sake rafka tagumin rashin Khalil din dakuma kuka da tashin hankali dazata shiga idan ta farka Wanda suka shirywa Sha dama.
Tsayawa sukayi kowannensu na nasa kukan me tsananin cikin tausayinta da Kuma zafin rashinsa Suma daya bugesu Babu Wanda yayi yunqurin hanata sbd kuka Kam yariga ya sameta abarta tayisa ko zataji sassucin radadin ZUCIYA.
Irin kukan datakeyi ne yasaka hankalin duk Wanda ke asibitin tashi sbd kukan nata taba zuciyoyinsu yakeyi Yana sake tuno musu da Dr khalil sbd rashinsa ne kawai yasa take wannan kukan Dan kuwa da Yana Raye Amatunsa bazatayi irin wannan kukan ba matuqar ba al'amari yafi qarfinsa bane.
MAHMOUD ne da kansa Modibbo yasashi yadawo asibiti yadaukosu Amatun tunda yashigo asibitin yaji tsit Yana Kama hanyar dakin datake yafara jiyo kukanta dayasashi tsayawa cak qafafunsa da zuciyarsa na qara daukar nauyin rashin Dan uwa mafi soyuwa garesa.
Jin kukan na kakkaryasa yasa yayi jarumtar qarasawa dakin ya tura ahankali yaci karo da ita zube bakin qofar tana kukan idanuwanta kamar zasu zazzago qasa.
Saurin juyawa yayi yacewa su iyami su kamota sutafi gida.
Daqyar suka tattarota suka saka mota suka nufi zabeera inda take cike tundaga farkon layin anguwar talakawane tako Ina bulbulowa sukeyi dukkaninsu yawanci mutanensa ne da taimako ya hadasu.
Ko a anguwarsu kawu jama'ar dasuka halarto dan jana'izarsa basa qirguwa
Hakama ko anguwar gidan Ibrahim daya zauna Saida yayi mutane sbd ko acikin rashin Saida ya taimaki mutane da dama.
Sashen Modibbo akayi da ita inda gawarsa take shimfide an lullubeta su Modibbo da Andi taredasu alhaji qarami da kawu dake gefe zaune Yana tsiayayar hawayen dasuka kasa tsaya masa,wallahi ayau ki yakeyi tamkar 'dan daya fito daga tsotsonsa ne ya rasa sbd Khalil yarone daya shiga ransa Wanda yakejin inama ace haddashi ya tsinta lokacinda ya tsinto su Amatu da Usman.
Kukan umme ne dake zaune gaban gawar ta daga qafafunsa tana addua tana kukan da bayama fita sbd disashewa da muryarta tayi hakama ko gani batayi sosai ayanzu sbd kumburin da idanuwanta da fuskarta sukayi.
Tun kafin ta iso gaban gawar tasa qafafunta suka kasa daukarta ta zube tana sake sabon kukan dake taba dukkanin mutanen dake palon tafara rarrafowa tanajan jikinta ta matso gaban gawar tana kallon fuskarsa dake bude tayi fari fes Yana sheqi kamar zaiyi murmushi.
Qoqarin daukewa numfashinta yafarayi Salman da USI sukayi kanta suna Kiran sunanta anty juwairiyya dake palon itama tayi saurin tarota tana shafa Mata fuskarta zuwa bayanta numfashin na Dan daidaituwa.
Cewa akayi su fita za'a yiwa Khalil din wanka sbd lokacin jana'izar yayi sabon kuka Amatu tafashe dashi tana kallonsa tana Kiran sunansa ganin zata karya musu zuciya yasa Andi yace juwairiyya tayi cikin gida dasu itada umme wadda sai anriqeta sbd sosai Bata gani komai sai dishi dishi.
MAHMOUD ne yabiyo bayansu bayan sun fito Yana rintse idon damuwar tambayar dasu Andi suka turosa yayiwa Amatun ya tsaya bayansu kadan yayi Dan gyaran murya kadan yakira juwairiyya ta tsaya tareda juyowa tana kallonsa da jajayen idanuwanta
Ya Dan kalli Amatu da umme dake hawaye Babu me lakkar qwaqqwaran motsi acikinsu a taqaicema baya tunanin zasu fahimci Abinda zai fada ya Dan dauke Kai cikin qaqalo nutsuwa yace"
Zaki tambayetane ko da akwai janaba atare dashi.
Dummm taji itama juwairiyyar tareda sauke Kai ta gyada Kai tareda matsawa gurin Amatun dake tafiya tanajan qafa jiki a sake ta riqota tana kallon fuskarta datai ja ahankali tace"
Amatu wanka za'a yi Masa anason sanin idan da akwai janaba ataredashi
Cak Amatu ta tsaya tareda juyowa ta kalli anty juwairiyya da jajayen idanuwanta dasuka Fara bushewa taji sabon kuka na zuwar Mata sbd tun yanzu taqara tabbatarda mutuwa tonon asiri ce, Amma tunda tariga ta rasashi meya rage Mata tun yanzu tafara ganin tonon asiri ahankali ta juyar dakai tana qoqarin wucewa ta 'dagawa anty juwairiyya din Kai Wanda yasa MAHMOUD ZABEERA dayaga amsar data bayar juyawa ya koma Yana qoqarin Hana mutuwar jikinsa bayyana, cikin sanyin jiki ya sanardasu Andi Nan aka Fara yimasa wanka,
Suna gamawa aka shiryasa cikin farin likafaninsa aka shimfidesa tsaf aka sake aikawa matarsa da mahaifiyarsa sukazo sukai masa adduar data Kuma Kai Amatu ga Suma akai ciki da ita aka dauki gawarsa aka fito da ita inda dubban mutane ke jira Wanda yasa iyayensa da Yan uwansa mamakin lokacinda yayi wainnan jama'ar a waje wanda yawancinsu talakawane da marasa lafiyarsa Wanda yasa Andi Jin kunyar kansa alokacin dasuke zaune suna zuba mulki da oda alokacin 'yayansu nacan suna taimakawa talakawa da marasa qarfi,
Ya tabbata koshi ya mutu yanzu bazaiyi jama'ar Khalil ba Wanda sukewa fatan ya dace tun anan.
Anyi jana'izar Dr khalil zabeera ankaisa kwancinsa na qarshe andawo anci gaba da karban gaisuwar da aketa ganin mutane kala kala a zabeera Wanda yaketa saka iyayensa da Yan uwansa alfahari da Jin sasssaucin zafin rashinsa sbd ganin Inshallah ya dace tunda kowa yazo da alkhairin dayake fada akansa.
Acan cikin gida kuwa a sashen umme ake karban gaisuwar
Umme ko Magana Bata iyawa idan anmata gaisuwa saidai daga Kai kawai Dan ko mutanen Bata ganewa sosai,
Amatu kuwa zazzabine me qarfi ya rufeta bayan anty juwairiyya da anty zarah sun taimaka Mata tayi wanka ta gyara jikinta tareda sallar asuba aka kwantar da ita a quryar bedroom din umme anty zarah ta zauna tareda ita tana shafa kanta sbd irin ajiyar zuciyar datakeyi Babu qaqqautawa kuka tuni idanuwanta suka bushe ko zuwa bayayi sai ajiyar zuciya da idanuwan datake zarewa.
Nuratu kuwa hajiya Maryam tafi kowa shiga tashin hankali bayan iyayen Khalil din da matarsa sbd Nuratu da abin ya buga sosai sai zabura takeyi tana somewa qarshe dai ankira likita yace saisun tafi da ita asibiti fatarsu alamarin bai taba qwaqwalwartaba.
Da daddare Amatu sashenta aka maidata tareda iyami da da anty salamatun gidansu da zasu zauna da ita kafin agama zaman gaisuwar asan abin yi.
Bedroom dinsa tashiga ahankali ta kunna wutar dakin tana juyowa ahankali da jikinta da Babu qarfi ko kadan idanuwanta suka tsaya akan shimfidar dasuka kwana a Daren jiyan ta qurawa jinin dayake Kan shimfidar ido tafara takawa ahankali ta Isa bakin gadon ta zube qasa tareda jawo zanin gadon ta qanqame tana sake kuka ahankali tana tuno Daren na jiya wanda yayisa a cikin yanayi na ciwo da rashin qarfin jiki sosai kamar Wanda rabo ke cizo Kuma kaman yasan rabuwa zasuyi, gwara da Bata hanasa kantaba Ashe datafi kukan datakeyi ayanzun.
Cukuikuye zanin gadon tayi cikin jikinta tana shaqar qamshin jikinsa dake jikin zanin cikin kuka tace"
Jiya kana taredani Dr meyasa zaka tafi??????
Kuka take fitarwa me qaramin sauti a bakin gadon har wahalallen bacci ya dauketa zaune a qasan.
Sai asuba ta bude idanuwanta dasukai nauyi sbd kumburi ta tashi tana gyara zamanta kafin ta miqe ahankali tana kallon zanin gadon dake jikinta ta sake kallonsa kafin ta nannadesa ta nufi cikin wardrobe din dakin tayi Masa kyakkyawan boyo ta fito dakin takoma dakinta inda su iyami suke sanyin AC yasa wani irin dogon bacci ya daukesu,
ta shiga toilet tayo alwala tana fitowa iyami na farkawa ganin alamar alwala atareda ita dakuma Jin ana sallah a masallacin cikin zabeera yasa tasan asuba ce ta tashi zaune tana qoqarin saukowa gadon ta nufi bayin itama.
Sallah Amatun ta tayar kanta na tsananin ciwo kamar zai tsage qarshe dai a zaune tayi sallar.
Guraren qarfe Tara na safiya aka kawo abincin safe aka jere musu a dining tareda sabuwar me aikin da aka iko ma Amatun.
Anty zarah ma tunda safe ta iso sashen ta gaidasu iyami dake zaune Palo jigum sbd Amatun ta rufe kanta a dakin Khalil din tanata kuka ita kadai taqi fitowa.
Duk yanda anty zarah tayi qin fitowa Amatun tayi salman da USI ma sunxo sunyi sunyi taqi bude dakin Saida akaje aka sanarwa umme.
Ummen na zuwa qofar bedroom din nasa kasa Magana tayi itama sai kawai ta fashe da sabon kukan daya daga musu hankali
Amatu dataji kukan ummen hankalinta yaqara tashi ta rarrafo ta bude qofar tareda fadawa jikin ummen tanajin kukan ummen har cikin ranta kamar yanda idan Dr na Nan tasan zaiji kukan ummensa.
Daqyar juwairiyya dasu anty zarah suka sallashesu aka fadowa su Modibbo saiga Andi dakansa ya zauna yayi musu nasihu masu karya zuciya da saka tawakkali Nan suka dauki qaddara suka dangana.
Anty zarah ce da iyami suka Bata abinci Dan Dole Tasha tea kawai sai guntun slicebread anty zarah takaita ta watsa ruwa ta sanya doguwar riga da hijab suka dawo Palo ta zauna cikin mutane.
Dukkanin kulawa da cinta da yanayinta anty zarah ce takeyi sai su iyami dasuke kwana yimata addua suna tofa Mata sbd yanda take firgita cikin bacci idan ya dauketa.
Anyi adduar uku anyi ta bakwai an watse kowa yakoma inda yafito sai anty salamatu da sabuwar me aikinta da aka bar Mata tayi zaman takaba Wanda taso takoma gidansu tayi umme ta ringa roqonta kada ta tafi tabarta Dole akace ta zauna anan tayi takaba tukuna.
****
Rayuwa me sauyawa kamar yanda mutuwa take Dole hakama dangana daci gaba da rayuwa yake Dole.,
Kusan sati hudu kenan yanzu da rasuwar Dr khalil zabeera Wanda tuni wasu suka manta suka koma harkokinsu Banda Amatu da mahaifiyarsa da har abada mutuwarsa bazata taba sakinsuba,
USI yakoma makaranta daqyar sbd kasa tafiya yayi yabar Yar uwarsa alokacin datafi buqatarsa Amma itace da kanta ta tuna Masa cewa burin Dr khalil ne yayi karatu me zurfi Dan ya tsayu da kansa ya tsaya musu wataran kamar irin yanzu da basuda Khalil din tabbas sunyi Rashi Dan yanzu zasu koma Matsin rayuwarsu ne na dah.
Tsayawa sukayi kowannensu na nasa kukan me tsananin cikin tausayinta da Kuma zafin rashinsa Suma daya bugesu Babu Wanda yayi yunqurin hanata sbd kuka Kam yariga ya sameta abarta tayisa ko zataji sassucin radadin ZUCIYA.
Irin kukan datakeyi ne yasaka hankalin duk Wanda ke asibitin tashi sbd kukan nata taba zuciyoyinsu yakeyi Yana sake tuno musu da Dr khalil sbd rashinsa ne kawai yasa take wannan kukan Dan kuwa da Yana Raye Amatunsa bazatayi irin wannan kukan ba matuqar ba al'amari yafi qarfinsa bane.
MAHMOUD ne da kansa Modibbo yasashi yadawo asibiti yadaukosu Amatun tunda yashigo asibitin yaji tsit Yana Kama hanyar dakin datake yafara jiyo kukanta dayasashi tsayawa cak qafafunsa da zuciyarsa na qara daukar nauyin rashin Dan uwa mafi soyuwa garesa.
Jin kukan na kakkaryasa yasa yayi jarumtar qarasawa dakin ya tura ahankali yaci karo da ita zube bakin qofar tana kukan idanuwanta kamar zasu zazzago qasa.
Saurin juyawa yayi yacewa su iyami su kamota sutafi gida.
Daqyar suka tattarota suka saka mota suka nufi zabeera inda take cike tundaga farkon layin anguwar talakawane tako Ina bulbulowa sukeyi dukkaninsu yawanci mutanensa ne da taimako ya hadasu.
Ko a anguwarsu kawu jama'ar dasuka halarto dan jana'izarsa basa qirguwa
Hakama ko anguwar gidan Ibrahim daya zauna Saida yayi mutane sbd ko acikin rashin Saida ya taimaki mutane da dama.
Sashen Modibbo akayi da ita inda gawarsa take shimfide an lullubeta su Modibbo da Andi taredasu alhaji qarami da kawu dake gefe zaune Yana tsiayayar hawayen dasuka kasa tsaya masa,wallahi ayau ki yakeyi tamkar 'dan daya fito daga tsotsonsa ne ya rasa sbd Khalil yarone daya shiga ransa Wanda yakejin inama ace haddashi ya tsinta lokacinda ya tsinto su Amatu da Usman.
Kukan umme ne dake zaune gaban gawar ta daga qafafunsa tana addua tana kukan da bayama fita sbd disashewa da muryarta tayi hakama ko gani batayi sosai ayanzu sbd kumburin da idanuwanta da fuskarta sukayi.
Tun kafin ta iso gaban gawar tasa qafafunta suka kasa daukarta ta zube tana sake sabon kukan dake taba dukkanin mutanen dake palon tafara rarrafowa tanajan jikinta ta matso gaban gawar tana kallon fuskarsa dake bude tayi fari fes Yana sheqi kamar zaiyi murmushi.
Qoqarin daukewa numfashinta yafarayi Salman da USI sukayi kanta suna Kiran sunanta anty juwairiyya dake palon itama tayi saurin tarota tana shafa Mata fuskarta zuwa bayanta numfashin na Dan daidaituwa.
Cewa akayi su fita za'a yiwa Khalil din wanka sbd lokacin jana'izar yayi sabon kuka Amatu tafashe dashi tana kallonsa tana Kiran sunansa ganin zata karya musu zuciya yasa Andi yace juwairiyya tayi cikin gida dasu itada umme wadda sai anriqeta sbd sosai Bata gani komai sai dishi dishi.
MAHMOUD ne yabiyo bayansu bayan sun fito Yana rintse idon damuwar tambayar dasu Andi suka turosa yayiwa Amatun ya tsaya bayansu kadan yayi Dan gyaran murya kadan yakira juwairiyya ta tsaya tareda juyowa tana kallonsa da jajayen idanuwanta
Ya Dan kalli Amatu da umme dake hawaye Babu me lakkar qwaqqwaran motsi acikinsu a taqaicema baya tunanin zasu fahimci Abinda zai fada ya Dan dauke Kai cikin qaqalo nutsuwa yace"
Zaki tambayetane ko da akwai janaba atare dashi.
Dummm taji itama juwairiyyar tareda sauke Kai ta gyada Kai tareda matsawa gurin Amatun dake tafiya tanajan qafa jiki a sake ta riqota tana kallon fuskarta datai ja ahankali tace"
Amatu wanka za'a yi Masa anason sanin idan da akwai janaba ataredashi
Cak Amatu ta tsaya tareda juyowa ta kalli anty juwairiyya da jajayen idanuwanta dasuka Fara bushewa taji sabon kuka na zuwar Mata sbd tun yanzu taqara tabbatarda mutuwa tonon asiri ce, Amma tunda tariga ta rasashi meya rage Mata tun yanzu tafara ganin tonon asiri ahankali ta juyar dakai tana qoqarin wucewa ta 'dagawa anty juwairiyya din Kai Wanda yasa MAHMOUD ZABEERA dayaga amsar data bayar juyawa ya koma Yana qoqarin Hana mutuwar jikinsa bayyana, cikin sanyin jiki ya sanardasu Andi Nan aka Fara yimasa wanka,
Suna gamawa aka shiryasa cikin farin likafaninsa aka shimfidesa tsaf aka sake aikawa matarsa da mahaifiyarsa sukazo sukai masa adduar data Kuma Kai Amatu ga Suma akai ciki da ita aka dauki gawarsa aka fito da ita inda dubban mutane ke jira Wanda yasa iyayensa da Yan uwansa mamakin lokacinda yayi wainnan jama'ar a waje wanda yawancinsu talakawane da marasa lafiyarsa Wanda yasa Andi Jin kunyar kansa alokacin dasuke zaune suna zuba mulki da oda alokacin 'yayansu nacan suna taimakawa talakawa da marasa qarfi,
Ya tabbata koshi ya mutu yanzu bazaiyi jama'ar Khalil ba Wanda sukewa fatan ya dace tun anan.
Anyi jana'izar Dr khalil zabeera ankaisa kwancinsa na qarshe andawo anci gaba da karban gaisuwar da aketa ganin mutane kala kala a zabeera Wanda yaketa saka iyayensa da Yan uwansa alfahari da Jin sasssaucin zafin rashinsa sbd ganin Inshallah ya dace tunda kowa yazo da alkhairin dayake fada akansa.
Acan cikin gida kuwa a sashen umme ake karban gaisuwar
Umme ko Magana Bata iyawa idan anmata gaisuwa saidai daga Kai kawai Dan ko mutanen Bata ganewa sosai,
Amatu kuwa zazzabine me qarfi ya rufeta bayan anty juwairiyya da anty zarah sun taimaka Mata tayi wanka ta gyara jikinta tareda sallar asuba aka kwantar da ita a quryar bedroom din umme anty zarah ta zauna tareda ita tana shafa kanta sbd irin ajiyar zuciyar datakeyi Babu qaqqautawa kuka tuni idanuwanta suka bushe ko zuwa bayayi sai ajiyar zuciya da idanuwan datake zarewa.
Nuratu kuwa hajiya Maryam tafi kowa shiga tashin hankali bayan iyayen Khalil din da matarsa sbd Nuratu da abin ya buga sosai sai zabura takeyi tana somewa qarshe dai ankira likita yace saisun tafi da ita asibiti fatarsu alamarin bai taba qwaqwalwartaba.
Da daddare Amatu sashenta aka maidata tareda iyami da da anty salamatun gidansu da zasu zauna da ita kafin agama zaman gaisuwar asan abin yi.
Bedroom dinsa tashiga ahankali ta kunna wutar dakin tana juyowa ahankali da jikinta da Babu qarfi ko kadan idanuwanta suka tsaya akan shimfidar dasuka kwana a Daren jiyan ta qurawa jinin dayake Kan shimfidar ido tafara takawa ahankali ta Isa bakin gadon ta zube qasa tareda jawo zanin gadon ta qanqame tana sake kuka ahankali tana tuno Daren na jiya wanda yayisa a cikin yanayi na ciwo da rashin qarfin jiki sosai kamar Wanda rabo ke cizo Kuma kaman yasan rabuwa zasuyi, gwara da Bata hanasa kantaba Ashe datafi kukan datakeyi ayanzun.
Cukuikuye zanin gadon tayi cikin jikinta tana shaqar qamshin jikinsa dake jikin zanin cikin kuka tace"
Jiya kana taredani Dr meyasa zaka tafi??????
Kuka take fitarwa me qaramin sauti a bakin gadon har wahalallen bacci ya dauketa zaune a qasan.
Sai asuba ta bude idanuwanta dasukai nauyi sbd kumburi ta tashi tana gyara zamanta kafin ta miqe ahankali tana kallon zanin gadon dake jikinta ta sake kallonsa kafin ta nannadesa ta nufi cikin wardrobe din dakin tayi Masa kyakkyawan boyo ta fito dakin takoma dakinta inda su iyami suke sanyin AC yasa wani irin dogon bacci ya daukesu,
ta shiga toilet tayo alwala tana fitowa iyami na farkawa ganin alamar alwala atareda ita dakuma Jin ana sallah a masallacin cikin zabeera yasa tasan asuba ce ta tashi zaune tana qoqarin saukowa gadon ta nufi bayin itama.
Sallah Amatun ta tayar kanta na tsananin ciwo kamar zai tsage qarshe dai a zaune tayi sallar.
Guraren qarfe Tara na safiya aka kawo abincin safe aka jere musu a dining tareda sabuwar me aikin da aka iko ma Amatun.
Anty zarah ma tunda safe ta iso sashen ta gaidasu iyami dake zaune Palo jigum sbd Amatun ta rufe kanta a dakin Khalil din tanata kuka ita kadai taqi fitowa.
Duk yanda anty zarah tayi qin fitowa Amatun tayi salman da USI ma sunxo sunyi sunyi taqi bude dakin Saida akaje aka sanarwa umme.
Ummen na zuwa qofar bedroom din nasa kasa Magana tayi itama sai kawai ta fashe da sabon kukan daya daga musu hankali
Amatu dataji kukan ummen hankalinta yaqara tashi ta rarrafo ta bude qofar tareda fadawa jikin ummen tanajin kukan ummen har cikin ranta kamar yanda idan Dr na Nan tasan zaiji kukan ummensa.
Daqyar juwairiyya dasu anty zarah suka sallashesu aka fadowa su Modibbo saiga Andi dakansa ya zauna yayi musu nasihu masu karya zuciya da saka tawakkali Nan suka dauki qaddara suka dangana.
Anty zarah ce da iyami suka Bata abinci Dan Dole Tasha tea kawai sai guntun slicebread anty zarah takaita ta watsa ruwa ta sanya doguwar riga da hijab suka dawo Palo ta zauna cikin mutane.
Dukkanin kulawa da cinta da yanayinta anty zarah ce takeyi sai su iyami dasuke kwana yimata addua suna tofa Mata sbd yanda take firgita cikin bacci idan ya dauketa.
Anyi adduar uku anyi ta bakwai an watse kowa yakoma inda yafito sai anty salamatu da sabuwar me aikinta da aka bar Mata tayi zaman takaba Wanda taso takoma gidansu tayi umme ta ringa roqonta kada ta tafi tabarta Dole akace ta zauna anan tayi takaba tukuna.
****
Rayuwa me sauyawa kamar yanda mutuwa take Dole hakama dangana daci gaba da rayuwa yake Dole.,
Kusan sati hudu kenan yanzu da rasuwar Dr khalil zabeera Wanda tuni wasu suka manta suka koma harkokinsu Banda Amatu da mahaifiyarsa da har abada mutuwarsa bazata taba sakinsuba,
USI yakoma makaranta daqyar sbd kasa tafiya yayi yabar Yar uwarsa alokacin datafi buqatarsa Amma itace da kanta ta tuna Masa cewa burin Dr khalil ne yayi karatu me zurfi Dan ya tsayu da kansa ya tsaya musu wataran kamar irin yanzu da basuda Khalil din tabbas sunyi Rashi Dan yanzu zasu koma Matsin rayuwarsu ne na dah.