← Book details Min Qalb Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 44 OF 70

Sashe 44

Min Qalb Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

No bana buqatan na blood bank din afara Shirin diban ledan jinin kawai.

Kallon cikin idanuwansa zarah keyi tanason ya kalleta ta karanci yanayinsa da yanda ya karbi zancen itace tabawa Amatun maganin Amma yaqi kallontan saima qoqarin juyawa dayakeyi yaga Andi da kansa tareda Modibbo a bayansu suna kallonsa cikin nustuwa,
Cikin alfahari dashi Modibbo ya jinjina Masa Kai yace"
Abinda kace shine daidai bama buqatan jinin wani gurin dabam munada wainda zasu bada jini da dama...

Andi na kallon fuskarsa dake sunkuye Yana karantar yanayinsa na kulawa da damuwa da yayi akan iyalin Dan uwansa Khalil alokacinda baya rayen ya jinjinawa qoqarinsa cikin yabawa yace"
Bama buqatan jinin kowa acikin dangi ma tunda uban Dan gashinan a tsaye bazai rasa jinin bayarwaba.

Office din Dr ashir suka nufa acan yasake musu bayani tareda Basu tabbacin Inshallah komai zai daidaita kafin suka tafi.

Iyami da kawu ma tuni suka iso asibitin
Hankalin kowa nasake hargitsa musamman yanxu da kowa yaji zancen da akwai ciki kowa yaji batareda dogon nazari ba saiyace meyasa zaa Bata magani ba tambaya
Hakan yasa anty zarah komawa gefe ta zauna cikin yanayi na tsananin damuwa da danasanin Bata maganin duk tasan cikin rashin sani tayi Amma yanda firgici kesa kowa tambayar Yana sata muzantuwa duk da Suma ta musu uxuri sbd tasan firgici ne da tsoron Abinda zai biyo baya.

Iyami ce tadawo gefenta ta zauna tana qoqarin danne damuwarta ta kalleta tace"
Karki damu zarah ko zubewa cikin yayi qaddararsa ce,
Koni da agabana take kowane irin magani Zan iya Bata na ciwon Kai tunda bamu sani ba.

Daga Mata Kai kawai zarah din tayi batareda ta iya ko magana ba
Duk Wanda zaiga gangancin Abinda tayi bazata damuba mutum biyu kawai takeson su fahimci niyyarta da rashin saninta,
Daga MAHMOUD sai Amatun
Amma sai zuciyarta na ganar mata zaiyi wuya MAHMOUD yayi Mata kuskuren fahimta sbd yafi kowa sanin Abinda zata iya aikatawa musamman akan Amatu da kowa ya shaida da zuciya daya take qaunarta.

Cikin ikon Allah ansamu anshawo Kan matsalar jinin ya tsayu cikinma ya tsayu saidai Kam Babu dogon aiki ko motsin dazai iya taba lafiyar cikin Dan haka hutu ne kawai akeso tayita yi jinin ma ansaka Mata roba daya Kuma alhmdlh jikin bai wani Yi baiyiba tafarko har so biyu anty salamatu da iyami na Bata tea sbd sune suka kwana anan.

Hankalin kowa ya kwanta musamman umme da tunda safe Takoma asibitin kusan tareda zarah suka iso Dan motarsu atare tashigo harabar asibitin Kuma kowanne da kayan breakfast ya iso.

Gaisawa sukayi suka Isa dakin tare alokacin anfito da ita wanka kenan iyami nasaka Mata doguwar riga mara nauyi.

Gaisawa sukayi umme na zama kusada Amatun tana qarasa gyara Mata Sanya rigar sai kaffa kaffa takeyi Wanda yasa Amatun kallonta tasaki guntun murmushi tareda riqe hannunta tace"
Umme bafa fashewa zanyiba kiketa Yi kaman kwai.

Babu Wanda be bayyanarda murnarsaba a fili da Abinda tafada sbd tun bayan rasuwar Khalil yau ne farko datai Abinda yake asalin dabiarta wato yanko Magana ba taunawa.

Dariyar farin ciki umme tayi bayan tagama gyara Mata zaman rigar ta zaunar da ita an jingina Mata pillow tace"
Ni ummen Kuma ake fadawa haka Amatu.

Murmushi tayi tace"
Umme ji nayi kamar kina min susa ne Yana sani waiwayi.

Kallon anty zarah tayi zatayi Magana saiga MD ZABEERA yashigo atake imperial majesty yacika gurin da sanyin qamshi Wanda yasakata lumshe ido sbd qamshin daya samu karbuwa daga yanayinta na ciki
Anty zarah ma lumshe ido tayi cikin yanayi na damuwa sbd jiya baikoma gidan ba sai dare sosai yanzu da safe Kuma tana tashi tahowarta asibiti tayi kawai sbd tayi tunanin Yana Nan din Ashe sai yanzu yake isowa gashi haryanxu basuyi Magana ba tana buqatan Magana dashi taji nasa tunanin akanta.

Ahankali ya qaraso ciki Yana gaidasu umme da iyami kafin ya maida kallonsa kadan akan gadon Amatun wadda ta bude idanuwanta adaidai lokacin sukai Ido cikin Ido
Da sauri kowannensu ya dauke idanuwansa shi Yana basarwa itakuma tana Dan tsuke fuska.

Kasa hkr zarah tayi sbd tanason Jin bakinsu su biyun akan alamarin ta juyo ta fuskancesa cikin tausasa harshe tace"
Ina kwana?

Kallonta yayi a natse ya amsa Yana qoqarin juyawa ya fice tace"
Ba laifina bane Abinda yafaru jiyan inatason inyi bayani Amma kamar kowa yakasa fahimtata.

Tsit dakin sukayi sbd Jin zancen nata musamman Amatu datakejin zancen yanzu.

Umme ce tayi saurin kallon Amatu kafin ta maida kallonta Kan zarah din tace"
Ba kasa fahimtarki akaiba zarah Amma ta Yaya Zaki yanke bata Magani without any consulting?

Da idonki Kinga Abinda yafaru da ita akan hakan,
Bai kamata ki kasa fadawa kowa Abinda yake damuntaba tun farko you should have told me ko Kuma MAHMOUD.

Cikowa idanuwanta sukai da hawaye bayan sunyi jajir ta dago ta kalli MAHMOUD din daya juya baya din bai fita ba yanajin saukar maganganun ummen har cikin ransa sbd idan har zarah tayi Dan kulawa ga Amatun bai kamata suga laifinta ba saidai ba halinsa bane tsayawa hayaniya.

Kallonsa zarah tayi ahankali tace"
Kana tunanin hakan kaima?

Rintse idanuwansa yayi tareda juyowa ahankali ya kalli Amatun da itama idanuwanta sukai jajir kafin ya kalli zarah din cikin radadin Abinda zai fada yace"
U could have asked kafin kibata maganin tunda Salman na Nan kokuma kifadawa ummen tun farko
This is irresponsible of you zarah...

Cikin bayyanarda tsananin damuwarta Amatu tace"
Me kukeyi wa anty zarah haka?

Kallonsa tayi Ido cikin Ido tace"
Kuna tunanin anty zarah zata iya cutatar Dani ne ko me?

Ni banganeba,
Nice nace anty zarah tabani magani idan tanada bayan haka idan anty zarah tasan Ina tareda wani Abu atare Dani wlh bazata taba bani Abinda zai cutatar daniba bama haka wlh na tabbata a duniya idan akwai meson Abinda yake taredani bayan ni da mahaifinsa da Yana Raye to anty zarah ce idan da ace tasani,
Meyasa zaku dasa ayar tambaya akanta Bayan dukkanin shedarta yakamata ku bayar,
Umme kadaki zargi anty zarah akaina ko Abinda yake taredani Dan Allah ko anan gabane hakan Yana karya zuciyar me hakuri wlh,
Zaku iya dasa Mata wani tunani na dabam Bayan ba haka takeba kunfi kowa sani musamman Kai zatafi Jin zafi idan kayi Mata wannan tunani""taqarasa fada tana dauke idanuwanta daga cikin nasa daya zuba mata Yana kallonta da idanuwa a bude sbd akaro na farko ta tayasa fadar Abinda yake cikin zuciyarsa sbd shine yafi kowa sanin zarah bazatayi ko kusan hakanba Akan wani bare akan wannan silly yarinyar.

Numfashi ya sauke ahankali tareda kallon cikin idanuwan Amatun kafin ya juyo ya kalli zarah da idanuwanta sukai jajir cikin kulawa da taushin harshe yace"
Lets go.

Kallonsa tayi zuciyarta na narkewa,fushinta na wankewa sbd yanda yayi ya nuna kulawarsa gareta tareda nuna damuwarsa akanta
Cikin sanyi tace meyasa nakesonka sosai hakane MAHMOUD DAHEER ZABEERA?

Ahankali ta sauke idanuwanta daga kansa tana cewa''
Nakawo Mata breakfast inason zanbata da kaina.

Wani irin kallon are you kidding me?yayi Mata Yana mamakin halinta na rashin Jin zafi.

Murmushi tasake cikin sanyi tareda daga Masa Kai
Ahankali yace ok tareda juyowa ya fice zuwa office din Dr Fatima.

Qoqarin zuba Mata abinci umme tayi Amatun tayi saurin hanawa tana kallon anty zarah cikin murmushi tace"
Umme antyna ce zata bani abinci da kanta Dan Allah.

Kallon zarah din umme tayi cikin Jin nauyi kadan duk da ita Bata dauki maganarsu cin fuska ga zarah din ba sbd tun farko yakama kafin kabawa wani magani kabari likita ya rubuta Masa Mana.

Iyami ce taqara dorawa da bawa zarah haquri tareda matsa Mata ta matso Dan bawa Amatun Abinda takawo Mata.

Cikin farin ciki da cire damuwar Abinda ya wuce din ta zubawa Amatun kunun gyada da plantain ta miqa Mata tana cewa''
Kici sosai sbd kisamu qarfin haihuwa idan lokaci yayi Dan karki manta da alqawarin da kukaimin keda Dr khalil na cewa zaku bani Abinda zaku Haifa tun a wancan cikin na iska.

Dariya kowa yayi a dakin Banda Amatu da kewar Dr da tunaninsa ya dawo mata.

Yamma sosai aka sallameta Salman ya kalli su kawu da iyami Bayan dukkaninsu sun fito harabar asibitin za'a tafi gida yace"
Kawu muje saina saukeku a gida su Kuma su tafi a motar umme ga Kuma motar zarah MD ma Yana cikin asibitin Naga shigowarsa kafin ayi sallamar inaga Yana tareda likitocin.

Kallon salman din kawu yayi kafin ya maida kallon gun umme da Amatu yace"
Ai Amatu tafiya zanyi da ita tayi takabarta tareda renon cikinta a gida sbd hankalin iyami rabuwa zaiyi da ni kaina....

Zaro idanuwa waje umme tayi hakama zarah dashi kansa Salman din.

Cikin rawar murya umme tace"
Kawu kayi hakuri Amma bangane ainihin Abinda kake nufi ba.

Ina nufin tunda dai dama gida zata dawo ko Bayan takaba gwara Takoma can din tayi zaman idan yaso bayan haihuwar sai asan nayi......

Bayansa dukkaninsu sukabi da kallo Babu me iya Magana sbd girgizar zancensa
Ganin suna kallon bayansa yasashi juyawa sai sukai Ido biyu da MAHMOUD dake tunkarosu cikin tafiyarsa me nutsuwa.
##Mamuh#
*Littafin Nan na kudine kabiya ka karanta cikin nutsuwa da aminci.**_MQ 34_*
Fuska kawu ya sake bayan isowar MD yace"
MAHMOUD sannu da qoqari mungode sosai Allah yasaka yayi muku albarka duk ku duka Allah yaji qan Khalilu yayi Masa rahama tareda albarkar Abinda yabari a baya.

Amin kowannensu yace jiki a sanyaye kafin umme ta Dora da fadin"
MAHMOUD kayi Magana da kawu Dan Allah yabar Amatu harta haihu tukuna ayi maganar tafiyarta.

Miqawa zarah takardar dake hannunsa Wanda Fatima tabayar kafin ya kallesu cikin rashin son Jan dogon zance yace"
Kutafi zamuyi mgn da kawun Zan wuto da ita idan angama.

Kallonsa umme tayi tana miqa dukkanin yardarta akan cika maganarsa na zai dawo da Amatun zabeera idan sun barta.

Ahankali ya gyada Kai Yana Dan rufe Ido.

Kallon Amatun umme tayi jiki a matuqar mace tace"
Ina jiran dawowarki Amatu.

Gyada Mata Kai tayi tana murmushin Bata qwarin gwiwa kafin ta kalli anty zarah da ita tayi wani iri tace"
Anty ZARAH saki fuskan Mana saikace Rabin ranki ne akace za'a tafi dashi.
Chapter 44 · 0% Book details