← Book details Hayateem Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 64 OF 76

Sashe 64

Hayateem Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Cikin girmamawa bayin suka sake zubewa qasa Banda jakadiyar sakon data sauke kanta qasa cikin tsananin girmamawa ta sake maimaita sakon Wanda ya qarasa wargaza kuzarin HAILE ta Nemi zubewa jikin fetto kowace jijiyar jikinta jinin cikinta na katsewa kanta yayi nauyi sbd wata irin sarawa da yayi.

Cikin sauri da kokarin sirrinta yanayin Hailen fetto tace masu kawo sakon su wuce ita kuka Kama Hailen tayi suka juya tareda Sauran bayin dake bayansu kowa kafafunsa a nauyaye sbd jinin uwargidansu dake tafarfasa duniyar bangaren tana daukan zafi gabaki dayanta.

Suna isa Kai tsaye har bedroom dinta fetto ta kaita ta kwantar tareda fitowa take ta aika bangaren Aslam Akan a kira likita a turo sa queen haile na buqatarsa.

Aslam na samun sakon ta fito ta nufo bangaren mahaifiyar tata sbd ganin meya sameta kokuma idan Wani abin ne ya faru dan kuwa tasan tabarta da shirin tafiya gurin sultan.

Tana isowa ta tarar da ko magana Mamee din bata iya yi kirjinta ke tsananin ciwo da zafi sosai idanuwanta sunyi jajir ajiyan zuciya kawai takeyi me Zafi da karfi akai akai bakinta baya iya furta komai.

Kallan fetto Aslam din tayi ta tambayeta meya samu mameen
Bayanin komai fetto tayi mata Wanda ya saka Aslam din juyowa ta kalli mahaifiyarta itama idanuwanta na sauyawa zuciyarta tayi dum tama rasa abin fada sbd alamu na sake tabbatarda masifu da ranakun baqin cikinsu zasu bude su fara ne matiqar NUAB na nan dan kuwa dasu da bokayen su sun tabbatarda shine matsalar datake tsakaninsu da dukkanin Buri,nutsuwa,kwanciyan hankali da farin cikinsu da suke buqatar kawar wa matiqar suna son rayuwa da wainnan abubuwan.

Shekara sama da ashirin rabon sultan da Wishmarsa,
Ya rufe ya shafe babinta a rayuwarsa da shimfidarsa kaman yanda kowa da Masarautar suka rufe shafinta a cikin matan sultan,
Wace masifar ce take Neman kunno Kai da a cikin Daren nan wannan mummunan sakon zai bayyana?
Me sultan yake shirin yi na maida wishmah matsayinta a dare guda batareda tsammanin kowaba,
Tayaya macen da suke son ‘dan tawayen ‘danta ya tattarata ya tafi da ita ko su aika masa ita sama zaa ce an maida mata matsayinta dayake tabbatarwa duniya ita din cikakkiyar ikon da mallakar sultan ce.

Wani nauyi kirjinta ya ta jefar da wayarta a kujeran dake dakin tana fasa kiran likita ta bude Baki kaman zuciyarta zatai aman wuta tace

‘Yanayin Mamee baa buqatan likita baqin ciki ne da dacin zuciya zata dawo daidai zuwa anjima idan ta samu sassauci’

Tana gama fadar hakan a koma kan kujeran ta zauna tana dafe goshinta dayake mata nauyi sbd ciwon Kai da bacin ran dayake cinta,

Shiru sukai dukkaninsu kowa da yanda baqin cikinsa yake cin zuciya da kirjinsa,

Meryam da aka aikawa mameen ba lafiya Kai tsaye tana zuwa taji abinda ya faru shiru tayi batareda tace komaiba ta jiya ta koma sbd batada abin fada hakama karfinta da lafiyarta Neman qarewa sukeyi a gurin dawainiya sa dakon baqin ciki da ritirin zuciya kullum Wanda a yanzu kam ta fara gajiya gangar jikinta ta fara gazawa ga daukan wannan baqin cikin da baida ranar qarewa bata fatar ta mutu a cikinsa batareda ta dandana farin ciki da kwanciyan hankalin gidan aure da tara zuria ba.

******Tenya kuwa a tsaye take qyam kan kafafunta tinda wannan sakon ya iso mata Wanda kwakwalwan kanta itama ta kasa dauka sbd babu ta yanda zaayi ace Bayan shekaru masu yawa da yafe wishmah daga zuciya da shimfidarsa rana tsaka dare daya yace ya dawo da ita a Daren da suke kallan Daren karshe na rayuwarsu a masarautar,
A Daren da suke jiran gari ya waye masa su bar komai anan suje su shimfida sabuwar rayuwa,

Shin sultan ya San da shirin tafiyarsu ne a goben daya yanke wannan hukuncin daya girgiza zukatansu dama duk Wanda zaiji cikakkiyar sanarwar zuwa da safe,

A wane Hali NUAB zai tsinci wannan mummunan labarin ga kunnuwa da zuciyarsa sbd hakan da sultan yayi Baro Baro yana nuni da Hana cikar burin NUAB ne yayi ta hanya me sauki se karfi dan kuwa koda NUAB yake ‘danta Wanda yafi kusanci da ikonta Akan kowa zamtowanta wishmah din ubansa kuma maidata cikakken matsayinta ya kere kowace irin dama da ikon da ‘danta yake dashi akanta.

Zufa ne a tsiyayo mata ahankali yana gangarowa daga gefen goshinta ta zame ahankali ta zauna gefen sakinah datai mutuwar Zaune itama idanuwanta jajir dan kuwa matiqar wannan mummunan sakon ya isa kunnan NUAB wutar tsanar mahaifinsa datake ransa ce zata sake hauhawa sbd tafiya da mahaifiyarsa bazai taba yiyuwaba gashi a yanzu datake cikin tsananin shauqin danta matiqar ya tafi yabarta batareda ya cika mata alkawarin tafiya da itaba komai zai iya faruwa da ita dan haka akwai tashin hankali a cikin wannan lamarin daya sauka a dare daya tamkar saukar aradu.

Kasa isarwa da Ayanah sakon sukai dukkaninsu sbd basusan tayaya kwakwalwanta zata karbi sakon ba hakama basu saniba ko sakon ya isa kunnuwan NUAB shima basusan yaya zai amsa sakonba dan haka tamkar sakon mutuwa sakon ya zamewa kowane ba gangaren harda na maraki wadda itama daga sama taji sakon ya saukar mata kamar tsawa sbd ta Riga ta dauka ta sakawa zuciyarta sultan ya gama da wishmah kenan har karshen rayuwarta,
Ko HAILE da zuriarta sun dauka ya gama da ita ya rufe babinta har qarshen rayuwarsa Shiyasa komai Yazo musu a mummunan bazata da gigita.

Kowane bangare a cikin bangaren uku na matan nasa tsit ya dauka babu bangaren da ba a cikin dacin zuciya da mutuwar jiki me tsanani suke ba tareda fargaba dan kuwa abu ne dayazo babu shirinda zasu San yaya zasu tarbesa ba.

Dare sake nutsuwa yakeyi Wanda ya saka tenya da suke Zaune zasuyi kwanan Zaune miqewa tayi shirin kaiwa sultan ziyara dan isar da rokon alfarmar da zasu buqata.

Tareda bayi hudu ta isa bangaren sultan din ta isarwa da kadir roko da sassaucin da wishmah take nema daga sultan Akan zuwanta Ayau Yazo ba shiri sultan yayi mata Afuwan karbanta a gobe ba yau din ba sbd yanzu haka ta jima da bacci sbd yanayin jikinta.

Kadir bai jima sosai a ciki ba gurin isar da sakon ya fito da sakon rokonsu ya karbu Ayau sultan ya mata Afuwa zuwa goben ta dawo cikakkiyar macensa wishmah dinsa.

Da sanyin jiki tenya tayi godia da girmamawa ta juya ta bar gurin tana komawa bangarensu kowa yayi dakinsa cikin jimamin yanda zasu iya sanar da Ayanah a gobe ta Koma wishmah dinta bazata taba iya bin ‘danta ba sedai shi idan zai zauna Masarautar tareda ita.

********A daidai wannan lokacin NUAB yana tsaye tsakiyar palonsa idanuwansa jajir sunyi Wani irin jan daya saka gabaki daya Yaransa sunkuyar da kansu suna tsaye Jere a kofar palon babu me ikon cewa komai ko tambayar komai sbd fushi da wutar dake ci a idanuwan LEUL dinsu sun tabbatarda mahaifinsa ne kadai a duniyar nan ya isa ya tabasa haka batareda sun shiga ba amma wannan fadan ba gurin shigarsu bane amma dukda mahaifinsa ne yana cewa suyi Wani abin tsaf zasuyi batareda tsayawa komaiba dan haka Ayau da suke ganin fushi da tsananin bacin ran da basu taba ganiba a tattare dashi ba yasa sun tabbatarda akwai Sauran Wani abu koma menene a zuciyar NUAB gameda mahaifinsa dan ba dan hakan ba Ayau sultan YASAR bazai kwana da kansa Akan wuyansa ba batareda sun tabbatarda ya samu ganawa da malaikan daukan rai.

Duk wata jijiyar dake jikinsa sun fiffito fuskarsa da kunnuwansa sunyi jajir Wanda ke bayyanarda ba qaramar wuta ce take ci a jini da zuciyarsa ba dan kuwa zuciyarsa gap take da bindiga Akan abinda yake ji,
Duk yanda ya rayu cikin fushi da mahaifinsa Akan abinda yayi na rabasa da uwarsa bai taba dauka zuciyarsa takai maqurar matakin karshe na qinsa da mahaifiyarsa ba da har zai iya basa zabi biyu na abinda yasan babu Wanda zai taba yi a cikin biyu ?

Bazai taba karban mulkin BOYEM ba sbd qiyayyar BOYEM da duk Wanda yake cikinta dake zuciyarsa,
Hakama zabi na biyun bazai taba saka hannun yabar mahaifiyarsa a BOYEM ba bazai taba dawowa ba har karshen rayuwarsa,
Tayaya wannan mutumin zaiyi tinanin yabar mahaifiyarsa anan qasar yabar qasar har abada sbd kawai yana son ya karbi mulkin masarautar da bai taba shaawan zama magajinta bare sarkintaba,Masarautar data wulaqanta mahaifiyarsa,
Masarautar da bata taba daraja mahaifiyarsa ba.

Rintse jajayen idanuwansa yayi yana sake Jin fushin da bai taba Jin irinsa ba yana danne kirjinsa da numfashinsa ya bude bude ido yana dunqule hannuwansa biyu da suke wata irin rawar tsantsar bacin rai da baqin ciki me tsananin gaske.

Tsit bangaren nasa ya dauka harma da zagayensa dan kuwa niimar bangarorin duk Wanda yake jinin masarautar dumi ya dauka me karfin gaske sbd masifar da babu shiri data fadowa kowannensu a Daren.

A bangaren sultan shima a Zaunen kaman yanda duka iyalansa suke ya kwana zuciyarsa cikeda abubuwa daban daban da suke shirye da karban tsanar kowace iri daga NUAB da kowa ma matiqar zai Kai qure lambar fushi da Zafin kan NUAB ya sakasa karban mulkin Masarautar dayake shirye da sauka ako Yaushe dan kawai ya Dora sa akai Wanda saiyayi hakan zai samu nutsuwa da sukunin dabai samu irinsa ba tinda ya hau mulkin.
#MAMUH

HAYATEEM
by
Mamuhgee
700
0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi
09033181070

Yan Nijar kuma
89825722
Depot my nita
Nissaiba laouali
[09/12, 10:47 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_*
Mamuhgee

59
Koda safiyar garin ta waye kowa dake cikin ahalin da ciwon Kai masu tsanani suka ringa tashi dashi tareda ciwon rai shima me tsananin gaske ga wainda suka samu rintsa wa baccin kenan ga wainda basu rintsa ba kuwa kaman wainda suka kwana gadin gawa haka suka tashi da idanuwa kaman baqin china.

NUAB ALMAZZ da duk Wanda yake bangarensa cikin Yaransa kaf babu Wanda ko gifta masa bacci yayi a ido,
Chapter 64 · 0% Book details