← Book details Hayateem Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 18 OF 76

Sashe 18

Hayateem Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Suna barin qasar kai tsaye umarni khams ya bada bazaa sake tsayawa kowace qasar ba sai ta BOYEM dan haka tafiya Sambai aka dauka zuwa BOYEM wadda ta saka aka fara sauyawa bayin abinci zuwa wadatacce me kyau sbd suyi Kyan gani da masarautar zata karba.
#MAMUH

HAYATEEM
by
Mamuhgee
700
0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi
09033181070

Yan Nijar kuma
89825722
Depot my nita
Nissaiba laouali
[09/12, 10:46 am] Asia ahmd: _*HAYATEEM*_
Mamuhgee

17

*JEWELRY JUNCTION*
08039440312
Ina macen datasan Yar kwalisa ce ko kuma wadda ke son zama cikakkiyar Yar kwalisa da zata kece Reni a cikin yan uwanta mata harma da maza ma,
Ina macen dakeson ta shiga mutane a kalli wuyanta da hannuwanta a sake kalla batareda an tantance asalin gwal da diamond ne a jikinta ba ko kuwa me Kama dashi ne??
To tazo ga inda dukkanin wani burinta zai cika gameda son hakan,
Mata Da Ado da Kwalliya Akasanku JEWELRY JUNCTION shago ne Na kayan Kawa Na Mata Manya DA Qanana,
✅duk wani nau'in design Na Sarka, 'Yankunne, Awarwaro, Zobe, Agoggo DA sauransu akwai su kala daban, daban. Sayen daya Ko sari👌
✅Munda ready to wear Na Adire dana materials daga kan boubou gowns zuwa palazzo DA tops dinki Na zamani👌
✅Idan ke ma'abociya son Kamshi ce munada turaruka kala daban daban masu Kamshi da rike jiki👌
✅Gefen inner wears din Yara ma ba'a barmu a bayaba, bra tops, half vest,vest, boxers DA pants Duk akwai masu kyau da inganci😍
🛒Shagonmu na nan a kan tanki road, guiwa low-cost a cikin garin Sokoto. Muna tura kaya ko wace jiha cikin Aminci DA Amana In Sha Allah.
WhatsApp 08039440312
Tiktok :@sokoto jewelry seller
Instagram: jewelryjunction23

***********
Koda su Ayanah suka farfado sun Riga sun bar qasar da ruhinsu yake acan babu sauran abinda ya rage a tattare dasu Bayan gangar jikinda babu ruhi babu zuciya sbd Nurat da Abaas sune ruhi da zuciyar Ayanah Zuhrah kuma rayuwarta,

Ita kanta Zuhrah yan uwanta sune rayuwarta da ita kanta dan haka tana farfadowa babu Abaas da gaske an rabasu rabuwar da har abada sun rabu bazasu sake haduwaba,bazasu sake sanin yana raye kokuma shi yasan sun raye ba hakama bazasu San halinda zai shiga ba ya rayu har zuwa mutuwar sa ba shima bazai San halinda zasu shiga ba na rayuwa ko mutuwa sai kawai ta sake sumewa batareda ta motsa daga inda take ba.

Ayanah kuwa tana farfadowa ta tabbatarda an rabasu da Abaas saita rarrafa ta isa kofa tana bugawa Da dan karfin da baifi na yaron goye ba sbd batada Sauran karfi ko kuzari kokuma wani amfani dan baqin ciki da qunci tareda rabata wainda sune kuzari da rayuwarta yariga yayi mata illar da bazata taba moruwa ba ko dawowa daidai abada

A karo na babu adadi take jin ta sake zabar mutuwa Akan rayuwa,
Inama ace mutuwa Abaas yayi a gabanta tasan ya komawa ubangiji baya duniyar yafi mata samun sassauci da nutsuwa Akan rabasu da akai batareda sunsan Ina rayuwa zata kaisaba shima,wace duniya ko sabuwar kaddarar zai fada duk basu saniba.

Kiran sunan Abaas takeyi duk lokacinda ta bugu kofar batareda akwai lakar komaiba a jikinta tamkar yar maye ko fita muryanta baya yi amma a hakan bata hakura ta Dena ba Abaas tsakanin buqata a kusa da ita kokuma a zubar dasu ko a ruwan qasar ne kafin a gama barin qasar.

Tsananin wahala,qunci,nannauyan baqin ciki,tarin gajiya da ruhi gangar jiki da zuciya sukai harma da idanuwa ya sakata silalewa qasa kwance a gurin tana fidda Numfashi gajiyayye tareda rufe idanuwanta ahankali jikinta na saki batareda ta some ba kawai dai ba lallai ta sake moruwa ba ko taba dawowa daidai ba.

Sakinah dake rungume da Zuhrah itama ta gama fita hayyacinta matsowa tayi gefen Ayanah din tareda dagota jikinta ta kwantar sukai shiru sbd yanzu kam babu wani qarshen qunci da baqin ciki dayayi saura Wanda basu gani ba dan haka koma me zasu tarar a gaba bazasu Ji komaiba.

Haka suka kwana suka wuni tamkar gangar jikinsu babu rai a jikinta,
Babu me iya kowane irin motsi idanuwansu ma a rufe suke ko abinci sun dena iya ci sedai sakina ce take karbowa ta rarrafo ta zauna tsakiyar su ta ringa basu a baki Akan dole sbd karfinsu dayake sake yin qasa sosai Wanda Sai a yanzu sakina ke sake tabbatarda kasancensu su duka hudun a tare da gaske shine rayuwa,ruhi,kuzari da karfin zuciyarsu sbd a yanzu Ayanah da zuhran gasunan sun zama tamkar marasa cikakken hankali.

Idan dare yayi haka zata zauna tsakiyar su ta kwantar da kansu a jikinta tana Shafa bayansu da fuskar su sbd samar da nutsuwa ko yar qanqanuwa ce a zuciya da gangar jikinsu.

Idan gari ya waye haka zata jawosu inda ake fiddosu Ana zuba musu ruwa sbd su wanke kullum kafin isarsu inda zaa kaisu,

Haka zata janyo su kaman qananun yara Ana dukansu duk da yanzu an rage dukansu sosai sbd duk anason suyi dan yi Kyan kallo dan haka kullum Ana fiddosu a hade guri daya a ringa zuba musu ruwa masu tsananin yawa suna goge jikinsu Wanda baya goga jikinsa lokacin da ake zuba ruwan duka yake sha da Bulala dan haka sakinah ganin kullum sai an dake su amma tamkar jiran duka sukeyi sbd ya wahala ta kashesu subar daniya ya saka koyaushe idan Ana zuba ruwan itace me wanke jikinta ta wanke nasu su dukan.

Ana gama wankesu haka zaa sake shanyasu a rana sai sun bushe a gargadasu a maidasu inda suke a rufe,

***********sake nutsawa tafiyarsu tayi Wanda a yanzu suna samun abinci sosai hakama wankan kullum ake musu dan haka yunwarsu ta ragu sosai sedai shi wanka kam ya saka duk fatar su ta bushe qayau sun koma wata sabuwar halittar daban kowannensu cikin bayin ka kalla tamkar an birkidasa cikin farin gari an ciro sbd kullum ruwan kawai ake zuba musu sannan a shanyasu a rana.

Har lokacin babu abinda ya sauya a sabuwar kaddararriyar rayuwar data samu su Ayanah,

A yanzu basa iya ko magana daga ido se ido sai kallo dan haka ne ita kuma sakinah nauyinsu ya dawo kanta gabaki daya fatarta dai suna isa qasar da zasu din a siyesu koda kashesu zaayi gwara a siyesu acan din da azo baa siyesu ba kusrawa su dawo dasu.

**********Tafiyar sati bakwai sukai tukuna jirginsu ya fara shigowa qasar da kowane tarihin zamanin ke fadar iko,girma,mulki,arziki da tsananin da masarautar qasar take dashi sakamakon sarakunanta da suke aje tarihi me girman gaske kafin rasuwa subar karagarsu.

Tsananin tsaro da tsari tareda dokokin dake zagaye da qasar daban yake da duka Sauran qasashen duniyar Wanda ya saka zuwa qasar yake tamkar samun babban rabone da saa a duniyar da suke rayuwar,

Suna gap da isowa kusan iyakar bodar da zata shigo dasu farkon ruwan qasar saida aka sake tsafta ce kowane bawa kafin suma suka wanke kansu da dan gyara komai na tsarinsu dasu kansu din.

Boda biyar ce tin daga farkon shigowa nahiyar qasar kafin isa cikin bodar ruwa ta cikin qasar wadda ita kanta bakin bodar cikin kasar daga nan bakin zuwa cikin qasar tafiya ce tsananin tafiya.

A bodar farko saida suka share kwana daya a bakin wajen qasar batareda sun samu damar shiga ba saida aka gama binciken tabbacin kasuwan bayin sukeyi kafin aka barsu suka wuce.

Wuni guda suka sake share wa Bayan barinsu Checking point na bodar farko kafin suka iso ta biyu.

Anan ta biyu ba saida suka share kwana daya harda wuni kafin aka gama tareda basu damar wucewa.

Shima tsakanin boda ta biyun zuwa ta uku tafiyar wuni guda ce sukutum sai tsakar dare suka isa dan haka baa duba kowane jirgin ba duka jiragen da suka taho a wajen bodar suka kwana sai washe gari aka fara aiki akansu.

Tashin farko abinda suka fuskanta anan shine bazasu shiga da jirginsu can bodar karshe ta cikin asalin qasar ba dan haka duka yawansu anan bodar zasu tsaya da jirginsu sedai shugabansu da wasu daga cikin manyansu da bazasu wuce Mutum Ashirinba dan a qaida baa wuce hakan dan hakan komai yawan bayinsu koda bayinsu sunfi dubu daruruwa to su dai da zasuci kasuwarsu bazasu wuce Mutum ashirin ba kuma da jirgin bakin bodar zasu biya su dauka su isa can sai sun dawo su koma jirginsu su koma inda suka fito.

Wannan dalilin ya saka kowace boda dake qasar girman bodar kawai yana fin girman qasashe da dama sbd irin tarin manyan mahaukatan jiragen ruwan dake tsayawa ko zama a gurin ba qaramar qasa ke iya daukansu ba,

Kowace boda dake qasar tamkar wata qasar ce me zaman kanta sbd gari ne da mutane sosai sbd duk wani maaikacin bakin boda na qasar anan yake rayuwa da iyalansa da yan kasuwarsu harma da sauran manyan huldodon kasuwancin qasar da akeyi kuma anan ma Ana cin kasuwar bayi sedai acan babbar bodar ake cin asalin babbar kasuwar bayin datafi kowace a duniyarsu,

Hakanne ya saka kowace bodar qasar gari ce guda mai zaman Kansa hidima sosai da cin kasuwanni akeyi tareda dubban Jamaa.

A nan jirgin kusrawa ya tsaya suka gama karba da biyan komai na tsantsar dukiya me yawan gaske kafin suka fiddo bayinsu kaf aka Kirgasu tareda biyawa kowane bawa daya Lasisin shiga qasar.

Saida suka kwana biyu a wannan bodar Ana harkar lasisin shiga qasar kafin aka kammala komai suka zuba bayinsu a sabon jirgi da zai kaisu suka wuce tareda barin dukannin Sauran kusrawa a garin bodar su samu shaqatawa da hutawa suma kafin su dawo Wanda a kalla basu San kwanakin da zasu shafe ba kafin dawowan tasu.

Bodar gaba baa tsaya komaiba lasisin bayinsu aka bi daya bayan daya Ana duba wa tareda tabbacin sa tukuna aka barsu suka wuce.

Suna wucewa khams ya sauke wata sanyayar ajiyar zuciyar samun nutsuwa da jin qamshin cikar Buri,

Qamshi da iskar da kake shaqa a kasar kusan daban yake sbd nutsuwa da tarin arziki kawai kake Ji da gani tako ina,
Chapter 18 · 0% Book details