← Book details Hayateem Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 36 OF 76

Sashe 36

Hayateem Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Sauti sosai kukan Ayanaah ya fara fitarwa sbd azaba da zafaffen baqin ciki da quncin dayake yunquro mata tana rintse idanuwanta tareda qanqamesa tareda tsanar rayuwarta da duka abinda zai biyo bayanta jikinta har wata irin jijjiga da kakkarwa yakeyi sbd ba qaramin girmansa da karfinsa yake sauke mata cikin Jin yana samun dukkanin gamsuwa da dumin jiki.

Tsawon lokaci ya dauka kafin ya samu cikakkiyar nutsuwa ya barta kaman babu rai a jikinta idanuwanta a rufe hawaye na bin gefen fuskarta tana fatar inama ranta ya fita a lokacin tabar duniya ta huta da fatar Allah kada ya bata rabon samun ciki.

Wanka yayi da ruwa masu Zafin gaske jikinsa na samun duk wata nutsuwan dayake buqata ya fito ya shirya a wasu kayan ya kwanta.

A cikin daren Ayanah ta fito bata iya ko Miqewa tsaye daidai bare tafiya yanda ya kamata idanuwanta jajir ko gani sosai batayi zuciyarta rufe da quncin duniya hannuwanta biyu dauke da danyar zinariyar daya doro a hannunta wadda tinda ta fito su tenya suka miqe tsaye idanuwan tenya a kanta bata ko kyaftawa zuciyarta na harbawa Sauran kuwa gabaki daya da securities qasa sukai da kansu.

Tenya dake Jin zuciyarta kaman zata fado hannuwan Ayanah din ta zubawa ido kafafunta har rawa sukeyi a natse Ayanah ta qarasa fitowa idanuwan tenya suka sauka Akan hannunta da zinariyar ke haskawa tana daukan ido taje tenya ta sake wata irin ajiyan zuciya me karfin gaske a boye tana Lumshe ido da Jin Wani irin sanyi fada farin ciki na cikata sbd zinariya alama ce ta gamsuwa sosai da zamantowanta cikakkiyar imebetin da a yanzu kawai yake buqatan zuwanta shimfidarsa har zuwa lokacin da zai qoshi da ita tukuna ya sauya Wanda kullum ta kwana a gurinsa zata fito da tukuicin danyen zinari a hannnu duk ranar data fito babu tukuicin komai a hannunta kuwa daga ranar ya gama da ita sauyi yake buqata duk ranar data fito da sarkar daham din dayake dauke da sunansa kuwa daga ranar kuwa ta zama wishimarsa ta har abada da mutuwa ce kadai Zata rabasu Wanda wannan ranar itace babban burin da tenya take dashi mai karfin gaske a zata iya komai Akan hakan sbd Ayanah GHAZ ta zamo wishmah ta uku a tarihin masarautar BOYEM ta duniya.

Ayanah na isowa gaban tenya zubewa tayi qasa tana dakin zinariya dake hannunta da saurin gaske tenya ta tareta jikinta tana kuma tare zinarin ta hanasa isa qasa tana Jin Wani irin kuka mai karfin gaske mara sauti daya tahowa Ayanaah din tana rintse ido sosai.

Bayin tenya dake gefe da sauri suka gyara wa Ayanah rufarta data zame daga kanta suna kara mata kujeran zaman da zaa turata da ita dan komawa da ita.

Tenya ce ta sakata ciki kujeran tareda shafa kanta ta bude Baki ta jero mata wata tsaftacciyar adduar tsari da fatan samun zuriar da duniya zatai alfahari da ita.

Turata sukai zuwa bangarenta sabo da wannan ranar kawai ake jira dan kuwa itama complete bangare aka bata me dauke da manyan palo guda biyu da suka jiqa da luxuries tako ina da bedroom guda uku Wanda daya yake nata daya na abinda zata Haifa saina ukun dake hanyar kitchen dinta ta baya Wanda yake na bayinta da aka ware mata ne guda uku,

Dukiya da daula ce irin wadda idan imaninka baida karfi zaka shagala sosai da duniya a cikinta aka zuba mata a bangarenta da gari na wayewa aka saka masa sunan GHAZ chamber.

A cikin daren suna isowa Kai tsaye ruwan zafi da wasu tsaftattun maganin gargajiya na al’adarsu aka sakata a ciki tana Jin wata irin azaba na ratsa jini da gangar jikinta harma da zuciyarta.
#MAMUH

HAYATEEM
by
Mamuhgee
700
0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi
09033181070

Yan Nijar kuma
89825722
Depot my nita
Nissaiba laouali
[09/12, 10:47 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_*
Mamuhgee

33
*_ZUZEAM VENTURES_*
08144015291
Bononza bononza
Assalamu alaikum yan uwa mata masu albarka
Zuzeam ventures zatayi promo karshen wannan watan har zuwa cikin watan nan me kamawa insha allah
-Da 5k kachal zaa baki kaza da ciccibi da gari da tsumi da gumba masu kyau da ingancin dazai sakaki dawowa ki qara harma ki kawo wani,
-Da 10k zaa baki kaza full da ciccibi da gari da tsumi da gumba,
wannan promo ne akan murnar cika shekara 10 cif da fara sanaa a online
Dan haka duk wadda take bukatar shiga cikin wannan promo Dan samun wannan garabasa to tayi sauri kafin ta kare
Kuma ku sani tsakani da Allah zaayi wannan promo komi me inganci ne Kyau sosai zaa baku tsakani da Allah
Idan kinada 3k ma zaa baki ciccibi kawai sai gari da tsumi masu kyau da ingancin suma,
Dan haka duk wadda take da bukata kofa a bude take
Idan kinada Yan uwa da abokan arziki zaki iya tallata masu idan kin kawo mutun goma suka shiga na 10k kinada package din 5k
Idan kin kawo mutun goma suka shiga na 5k kinada package din 3k.
Zuzeam ventures
08144015291

*******
Kakkarwa jikinta keyi yana daukan zafi sosai idanuwanta har lokacin a rufe hawayen dake fitowa ma sun qafe koina na jikinta ya sake sai yanda sukai da ita tana Jin komai amma bata motsaba ko kadan,

Tenya ce da kanta da sakinah suka gasata a cikin ruwa Kala uku da suka saka jikinta Dena kakkarwa hakama karfi na dan dawo mata,

Ba qaramar shiga yayi mata ba wadda ta sakata samun yan qananun raunikan da azabar tayi mata sosai amma dan karfin Hali da taurin zuciyar data gama mutuwa,

Yanda jikinta ke fizga yana jijjiga ne a cikin ruwan yake tabbatar musu da azabar datake ciki na gurzuwan datai a inda ba damar fada bare magana,

Wani jiqon da gyara na musamman da tattali ta samu daga tenya da bayinta kafin aka hada mata wasu ruwan masu tsafta da Zafin gaske tayi wankan tsarki ta fito daure da towel bata iya tafiya me hayaniya a natse kanta a qasa idanuwanta jajir gashinta na tsiyayan ruwa suna bin fatarta dake da santsi,

Ko data fito babu kowa dakin bayan sakinah data fidda mata kayan sakawa doguwar rigar bacci me kauri datakai mata qasa sosai tareda saka mata qamshi me sanyi,

Isowa tayi gaban mirror ta zauna har lokacin idanuwan basa kallan koina bata iya cewa komai kaman bebiya,

Sakinah da jikinta yake a tsananin sanyaye itama idanunwata Jan sukai tanason yiwa Ayanaah din kuka amma kuma zuciyarta na hanata hakan sbd insha Allah kaddararsu zata sauya ne daga yanzu,

Towel sabo dake hannunta ta saka ahankali ta fara gogewa Ayanah din gashinta cikeda kulawa kafin ta dauko hand dryer tafara busar mata da Kai cikin nutsuwa da kulawa tana kasa kallan fuskar Ayanah din har ta gama ta dauko mata undies sabbin tareda kayan baccin ta kawo mata har gabanta ta juya ahankali zata fice kaman daga sama taji anriqo hannunta.

Cak ta tsaya tareda rufe ido tana Hadiye hawayenta da suka ciko idonta kafin ta juyo ahankali ta kalli Ayanah din wadda bata dagoba bata kuma bude Baki ba,

Shiru sukai dukansu babu Wanda ya motsa hakama sakinah hawayenta Neman kasa riqewa sukeyi dan haka ta daga hannunta daya zata rufe bakinta Ayanah ta fada jikinta ahankali daga Zaunen tareda zagayeta da hannuwanta biyu ta rungumeta cikin wani tsananin sanyi tareda rufe idanuwanta ta fasa wani irin kuka mai tsananin sanyi da ratsa zuciya tana qanqame sakinar cikin mutuwar jiki.

Sakinah dake tsaye Jin tayi kafafunta na Neman gazawa sbd mutuwan jiki da kasa riqe kanta datai itama ta fasa kuka Mara sauti tana rungume kan Ayanaah tsananin tausayinta na rufe zuciya da idonta.

Kuka mai yawan gaske Ayanah ta yi sosai a jinin sakinah har saida zazzabin jikinta yayi tsananta kafin sakinar ta taimaka mata ta saka kayan takaita inda zatai sallah tayi sallar ta kwantar da ita a gado daidai lokacin Dayar baiwar me suna Nimah ta shigo dauke da tray din dayake jere da madara me zafi da magani ta iso dasu ta miqawa sakinah.

Karba tayi ta bata a bakinta ta shanye tas sbd batason bata lokaci da tsayawa gardama Akan hakan,
Tana shanyewa ta miqa musu cup din Tasha magani ta zame ta kwanta a hankali sakinah ta rufeta da wani qaton lallausan bargon da taushi sa kadai zai qarawa baccinka karfi.

Kashe wuta da saita sanyin ac tayi kafin ta fice daga dakin aka rufe kofar.

Sai a lokacin sukai gaggawar zuwa tasu sallar tin kafin lokacinta ya wuce,

Bacci sosai da zazzabi Imebēti Ayanah ghaz ta samu na tsawon lokacinda bata sani ba sedai koda ta tashi tasan rana tayi dan haka Kai tsaye toilet ta nufa cikin rashin qwari tayi wanka da alwala ta fito a lokacin ne sakinah ta shigo ta gyara dakin ta sake fito mata kayan d aka kawo dan sakawanta aka cike wardrobe dasu tareda duka wani abin buqatarta masu yawa da tsada.

Breakfast aka kawo mata tana gamawa kyautikan matan sultan suka iso gareta sbd cika al’adar zamowanta imebetin da zata cigaba da zuwa tiraka,

Kyautar MARAKI ce ta fara isowa na wata doguwar sarkar zinari mai hade da yan kunne suma dogaye da sarkar kafa,

Godia tayi cikin sanyi kafin kyautar haile ta iso daga baya ita kuma sarkar Kai ce ta zinari da awarwaro masu kowane hannu babbiyu,
Itama godia tayi kafin su sakinah suka karba sukai ciki dasu tukuna daga nan tenya ta zaunar da ita t fara jero ma tsauraran sharuddan suka biyo matsayin datake dashi yanzu,

Duk abinda ake fada mata baya iya ko motsawa ba idanuwanta da sukai ja ne har lokacin take zubawa komai kawai idan ta gaji kuma ta Lumshe idanuwanta da sauke Numfashi ahankali,

A hakan ta wuni babu kowane irin kyakkyawan kuzari ko magana sedai ido kawai daga qarshe ma daki ta qarasa wuni ita kadai komai na rayuwarta na dawo mata farko da karshe,

Yammar fari nayi masu gyaranta suka iso da tenya haka aka kuma gasata a wasu ruwan magani masu zafi da ratsa jiki har magrib tukuna aka gama suka fice,
Chapter 36 · 0% Book details