Sashe 3
Hayateem Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sun yada zango a duhun dajin kauyen ba shakka ba tsoro ba fargaba sbd babu abinda yake basu tsoro kuma daman su daji da cikin ruwa ne gurin rayuwansu,
Idan suka saka Buri Akan gari to tabbas sai sun cika wannan burin ta hakanne sukai suna sukai karfi suka zama abin tsoro da shakka ga garuruwan daba manya ba,
Abu na farko da suka fara fuskanta shine dajin na dauke da tarin macizai da babu Wanda zai iya tsallakewa ya wuce dajin gaba ya isa cikin hanyar garin dan sun fara rasa mutanensu sosai da dafi dan haka suka sauya mataki ta hanyar fara farautarsu amma kaman dai dajin babu abinda yake cikinsa sai tarinsu dan haka suka fara Neman hanyar shiga.
Khams shugaba kuma me sarautar kusra shi kadai ne yake iya keta dajin ya shiga harya fita babu abinda ya samesa sbd tsananin abubuwan dake jikinsa na tsari da kariya daga kakanninsa,
Dan haka shi kadai da Kansa ya shiga yayi tafiya me Nisan data daukesa kusan wani daya sai gashi a farkon garin ANJOM Wanda ya sakasa tsayawa cikin tsananin farin ciki yana Jin wani irin Mazarin ganin hasken samun cikar burinsa Wanda samun wannan garin zai cika masa,
Jajayen idanuwansa ya rintse da karfi ya bude su ahankali yana shakar iskar garin me tsananin dadi da nutsuwa tareda kwanciyan hankalin da zai juya musu zuwa tabbataccen baqin cikin da baza su taba mantawa ba a tsawon tarihi,
Juya wa yayi ya fara kallan koina dake nuna arziki a garin,
Mutane daddaiku dake hidimar gabansu a farkon garin ya ringa bi da kallo wainda kowannensu yake harkar gabansa cikin farin ciki da annashuwa batareda sun Lura dashi ba sbd sanin baqon da baida shedan shigowa baqunta daga GHAZ baya taba shigowa garin.
Wani iskan farin ciki da tsananin Jin dadi khams ya sake yana daga kafafunsa yaci gaba da takowa zuwa cikin garin yana Jin kaman ya kamasu a lokacin ya bude ido yagansa a bakin ruwan shiga qasar BOYEM.
Tafiya yake yi yana sake Jin zalamarsa da tsananin rashin imaninsa yana fadada sbd yana qara shiga yana ganin tsananin mutanen da garin zai yi Wanda zasu cike dukkanin abinda yake nema.
Ahankali daidaikun mutane suka fara kallansa suna shiga tsananin mama ki da fargaba sbd yanayin baqinsa da yayi yawa da muninsa tareda kalar kayan jikinsa da komai yake baqi babu abu ko daya dayake jikinsa dayake da wata kalar Bayan baqi.
Lura da hakan ya zame ya dawo wajen gari ya fara dakun damar shiga garin har dare yayi sosai tukuna ya sulalo cikin garin yana zagaye wa ya gama Karance yanda rayuwan darensu take sedai abinda ya fahimta babu yanda zaa yi ya isa ko kusa da hanyar gidan shugaban garin Wanda a cikin Daren ya sake tabbatarda kafi ne a garin ta yanda yana buqatan karyasa kafin su samu daman shigowa su samu abinda suke so dan haka ya dawo farkon gari.
Bakin wani qaramin gidan dake farkon garin ya tsaya yana zubawa gidan idanuwansa da babu komai a cikinsu sai rufe wan ido na rashin tausayi ko kadan.
Kallan gidan yayi sosai kafin ya saka hannunsa jikinsa ya zaro wata wuqa baqa qirin me tsananin kaifi da dafi ya tinkari kofar shiga gidan yana isa kofar shiga wadda take ta itace kafarsa ya saka ya turata da karfin gaske Wanda take ta fadi sedai batai wani qara ba sbd kasancewanta ice ba karfe ko katako ba.
Shigowa yayi Kai tsaye ya nufi dakin farko dayake gidan yana shiga dakin ya fizge labulen dake dake take hasken farin wata ya ratso cikin dakin,
Yara ne su hudu a kwance jere suna bacci cikin nutsuwa
Wuqar hannunsa ya daga bai tsaya komaiba ya qaddamar musu ya fito dakin hannuwansa da fuskansa duka jini ya fada Dayan dakin acan iyayen suke take ya take kan Baban da kafarsa ya soka masa wuqar hannunsa da karfi a gefen hannunsa yana fizgo maman itama ya doke wuyanta da karfi take ta yanke jiki ta some a gurin.
Fizgo Baban yayi cikin tsananin karfi ya sake soka masa wuqa a gurin daya soka masa farko ya miqar dashi cikin rashin tausayi ko kadan ya dauresa ya durkusa ya dauki Matar yajasa da igaya ya fice dasu.
A cikin duhun Daren ya biyo daji dasu ya Baro garin
Tafiya me tsanani sukai har gari yayi haske tukuna suka samu tsallake rabin dajin zuwa me hadarin ga mamakinsa suma babu abinda ya samesu harya tsallake dasu suka sake nusawa
Matar na farfadowa ya sauke ya daureta tareda mijin yaci gaba da jansu cikin Axaba da rashin tausayi ko kadan.
Sai dare ya sosai ya iso wajen dajin dasu inda mutanensa suka taso suka tarbesa tareda karban masa.
Azaba suke tsananin cikin musamman Baban da jininsa ke fita a hankali daga yankar da yayi masa,
Maman kuma bakinta da dukkanin yawun jikinta sun gama bushewa daqyar dukkaninsu suke numfashin azaba da kafafunsu da duka sun fashe daga tafiyan.
Kusrawa basu tsaya komaiba suka hau gana musu sabuwan azabar data saka kowannensu some wa amma a hakan suka cigaba da basu azabar data saka mijin mutuwa sbd jininsa daya qare qaf daga jikinsa.
Duk wani sirrin ANJOM sun samesa a bakin Matar wadda azaba take daf da dauke ranta,
Sun samu sanin komai da sanin asalin mene ze karya musu garin su samu shiga a bakinta batareda tasan mijinta ya mutu ba sbd ta tsiratar dasu ta fada musu abinda suke son ji.
Azabarta bata qare ba sun saida suka tirsasata ta samo musu jinin GHAZ,
Sbd Neman kubutar dasu mijinta ta dawo ANJOM inda ta fadi duk abinda ya faru Banda cewa mijinta na raye zata samo musu jinin GHAZ dan tseratar dashi,
Da farko jinyarta akai a cikin iyalinsa sbd yanayinta da tausayin mummunan halin data shiga na rashin ‘yayanta duka da mijinta datace ya rasu batareda tasan da hasken ya rasu ba,
Adalci da tsananin tausayin GHAZ Ali ya saka ya dawo da ita cikin iyalansa da qarin shakkar zasu iya dawowa su dauketa ko kasheta tinda taga inda suke.
Raunika na fili da boye ne a jikinta da suke kokarin zama baraza ga rayuwarta duk da hakan tayi alkawarin tseratar da mijinta dan haka zamanta a cikin asalin GHAZ shine isharar datake ganin kaman Allah yayi mata Akan ta kubutar da mijinta sbd a farko tasan bazata taba iyawaba dan babu ta inda zata samu kusanci da ahalin GHAZ bare samun jininsu koda diqo daya ne sai gashi batareda tsammani ba Allah Kai tsaye ya shigar ita cikinsu.
GHAZ Ali ya shigo da itane cikinsu shi kuma sbd ya sakata tsaro sosai ta yanda ko akwai wani abin bazata samu damar yi ba ko fita gari.
********Da wannan dalilin Asamah ta zama cikin iyalin GHAZ tareda jinya me kyau ta warke sosai ta zama tamkar amintacciyar ahalin sbd lokaci daya ja sosai hakama kusrawa suna bangaren sun kafa garin kansu sbd burinsu Wanda suke jiran ranar cikarsa.
Lokaci ya tafi sosai kauna da shaquwa me tsafta ce a tsakanin dukkanin GHAZ da Asamah wadda kulawa da gabaki daya yaran gidan ta dawo hannunta duk da sun zama yan mata amma itace ke kulawa da komai nasu musamman Abaas Wanda yayi wata irin shaquwa da ita,
Duk tsawon shekarun datai a cikinsu burinta Akan kubuto da mijinta bai taba fita a ranta ba duk da lokuta da dama tana Jin kaman ta hakura da hakan sbd tsoron illar da kusra zasu iya shigowa gari suyi Wanda a yanzu cikin garin ANJOM iyalan GHAZ ne kadai take dasu sbd tausayinta daya zamo kauna me karfi a gareta.
A yanzu da shekaru suka ja kusra hakurinsu ya fara qare wa dan haka ahankali suka fara farautar duk Wanda zai fito daga garin dama hanyar makusanta hanyar dajin garin ta yanda gabaki daya nahiyar ta zama ta gagari kowane dan Adam bi a tahiri sbd duk Wanda ko hanya ta biyo dashi ta nahiyar ko gawarsa baa samu dan haka duniya da dukkanin nahiyar tarihi bin nahiyar ya zama tamkar tarihi sbd gabaki daya zagaye suke da dajin ANJOM Wanda ya koma babu shiga dajin babu fita dan haka rayuwar ANJOM ta fara shiga wani irin halin tsanani da rashin kwanciyan hankali da fargaban ko Yaushe komai ze iya faruwa garesu.
Tin masifar na waje dajin nasu harta fara shigowa sbd kisan yayi yawan da a bakin gari suke samun gawarwakin mutanensu.
Wannan tashin hankalin ne ya saka GHAZ fara tinanin iyalinsa da bazai iya barin wannan masifar dake kokarin afkowa ANJOM ta shafesu dan haka yasa aka fara Ramin fita garin ANJOM ta baya ta inda yake saka ran babu kusrawan zuwa ruwan dazai iya kaika nahiyoyi da dama dan tsira.
************
Zaune suke a wata irin lafiyayyan rumfar hutawarsu kowannensu na Zaune gurin cike da yayan marmari masu kyau sai qatuwar kwaryar dabino da shima yake da daukan ido.
Ayanah ce kadai bata gurin sbd shirinta dayake daukan lokaci dan haka tana fito wa tareda baiwarta daya Sakeena dake biye da ita.
Rumfar ta tinkaro a natse cikin takun dayake bayyanarda tsananin nutsuwarta da mulki yake ciki,
Qarar sarkar hannunta data kafarta me fidda dan sautin daukan hankali ce ta saka Asamah dake sake jere Kayan marmari fara dagowa ahankali ta sauke idanwanta Akan hanyar tana zubawa halittar Ayanah dake daukan idanuwa duk Wanda zai kalleta ido Tana ambatar Masha Allah Masha Allah cikin zuciyar.
Abaas ne ya juya ahankali shima yana kallan Ayanah din yana zubawa kyakkyawan fuskanta ido yana Godiyan Allah ako Yaushe da Ayanah ta kasance jininsa wadda yakejin kaman jinin da suka hada bai ishesa ba yana tsananin son ace ya sake hada wani abu da ita Wanda zaisa ace yafi duka Sauran yan uwansu kusanci da hada jini ita.
Ganin idanuwansa akanta kaman koyaushe yana kallanta cike da kauna me tsanani ta jini bude bakinta tayi wani kyakkawan murmushi ya mamaye fuskanta har saida hakoranta suka dan bayyana ta qaraso gurin tana miqa masa hannunta dayake sanye da fararen azurfa masu kyau da rashin sirki.
Idan suka saka Buri Akan gari to tabbas sai sun cika wannan burin ta hakanne sukai suna sukai karfi suka zama abin tsoro da shakka ga garuruwan daba manya ba,
Abu na farko da suka fara fuskanta shine dajin na dauke da tarin macizai da babu Wanda zai iya tsallakewa ya wuce dajin gaba ya isa cikin hanyar garin dan sun fara rasa mutanensu sosai da dafi dan haka suka sauya mataki ta hanyar fara farautarsu amma kaman dai dajin babu abinda yake cikinsa sai tarinsu dan haka suka fara Neman hanyar shiga.
Khams shugaba kuma me sarautar kusra shi kadai ne yake iya keta dajin ya shiga harya fita babu abinda ya samesa sbd tsananin abubuwan dake jikinsa na tsari da kariya daga kakanninsa,
Dan haka shi kadai da Kansa ya shiga yayi tafiya me Nisan data daukesa kusan wani daya sai gashi a farkon garin ANJOM Wanda ya sakasa tsayawa cikin tsananin farin ciki yana Jin wani irin Mazarin ganin hasken samun cikar burinsa Wanda samun wannan garin zai cika masa,
Jajayen idanuwansa ya rintse da karfi ya bude su ahankali yana shakar iskar garin me tsananin dadi da nutsuwa tareda kwanciyan hankalin da zai juya musu zuwa tabbataccen baqin cikin da baza su taba mantawa ba a tsawon tarihi,
Juya wa yayi ya fara kallan koina dake nuna arziki a garin,
Mutane daddaiku dake hidimar gabansu a farkon garin ya ringa bi da kallo wainda kowannensu yake harkar gabansa cikin farin ciki da annashuwa batareda sun Lura dashi ba sbd sanin baqon da baida shedan shigowa baqunta daga GHAZ baya taba shigowa garin.
Wani iskan farin ciki da tsananin Jin dadi khams ya sake yana daga kafafunsa yaci gaba da takowa zuwa cikin garin yana Jin kaman ya kamasu a lokacin ya bude ido yagansa a bakin ruwan shiga qasar BOYEM.
Tafiya yake yi yana sake Jin zalamarsa da tsananin rashin imaninsa yana fadada sbd yana qara shiga yana ganin tsananin mutanen da garin zai yi Wanda zasu cike dukkanin abinda yake nema.
Ahankali daidaikun mutane suka fara kallansa suna shiga tsananin mama ki da fargaba sbd yanayin baqinsa da yayi yawa da muninsa tareda kalar kayan jikinsa da komai yake baqi babu abu ko daya dayake jikinsa dayake da wata kalar Bayan baqi.
Lura da hakan ya zame ya dawo wajen gari ya fara dakun damar shiga garin har dare yayi sosai tukuna ya sulalo cikin garin yana zagaye wa ya gama Karance yanda rayuwan darensu take sedai abinda ya fahimta babu yanda zaa yi ya isa ko kusa da hanyar gidan shugaban garin Wanda a cikin Daren ya sake tabbatarda kafi ne a garin ta yanda yana buqatan karyasa kafin su samu daman shigowa su samu abinda suke so dan haka ya dawo farkon gari.
Bakin wani qaramin gidan dake farkon garin ya tsaya yana zubawa gidan idanuwansa da babu komai a cikinsu sai rufe wan ido na rashin tausayi ko kadan.
Kallan gidan yayi sosai kafin ya saka hannunsa jikinsa ya zaro wata wuqa baqa qirin me tsananin kaifi da dafi ya tinkari kofar shiga gidan yana isa kofar shiga wadda take ta itace kafarsa ya saka ya turata da karfin gaske Wanda take ta fadi sedai batai wani qara ba sbd kasancewanta ice ba karfe ko katako ba.
Shigowa yayi Kai tsaye ya nufi dakin farko dayake gidan yana shiga dakin ya fizge labulen dake dake take hasken farin wata ya ratso cikin dakin,
Yara ne su hudu a kwance jere suna bacci cikin nutsuwa
Wuqar hannunsa ya daga bai tsaya komaiba ya qaddamar musu ya fito dakin hannuwansa da fuskansa duka jini ya fada Dayan dakin acan iyayen suke take ya take kan Baban da kafarsa ya soka masa wuqar hannunsa da karfi a gefen hannunsa yana fizgo maman itama ya doke wuyanta da karfi take ta yanke jiki ta some a gurin.
Fizgo Baban yayi cikin tsananin karfi ya sake soka masa wuqa a gurin daya soka masa farko ya miqar dashi cikin rashin tausayi ko kadan ya dauresa ya durkusa ya dauki Matar yajasa da igaya ya fice dasu.
A cikin duhun Daren ya biyo daji dasu ya Baro garin
Tafiya me tsanani sukai har gari yayi haske tukuna suka samu tsallake rabin dajin zuwa me hadarin ga mamakinsa suma babu abinda ya samesu harya tsallake dasu suka sake nusawa
Matar na farfadowa ya sauke ya daureta tareda mijin yaci gaba da jansu cikin Axaba da rashin tausayi ko kadan.
Sai dare ya sosai ya iso wajen dajin dasu inda mutanensa suka taso suka tarbesa tareda karban masa.
Azaba suke tsananin cikin musamman Baban da jininsa ke fita a hankali daga yankar da yayi masa,
Maman kuma bakinta da dukkanin yawun jikinta sun gama bushewa daqyar dukkaninsu suke numfashin azaba da kafafunsu da duka sun fashe daga tafiyan.
Kusrawa basu tsaya komaiba suka hau gana musu sabuwan azabar data saka kowannensu some wa amma a hakan suka cigaba da basu azabar data saka mijin mutuwa sbd jininsa daya qare qaf daga jikinsa.
Duk wani sirrin ANJOM sun samesa a bakin Matar wadda azaba take daf da dauke ranta,
Sun samu sanin komai da sanin asalin mene ze karya musu garin su samu shiga a bakinta batareda tasan mijinta ya mutu ba sbd ta tsiratar dasu ta fada musu abinda suke son ji.
Azabarta bata qare ba sun saida suka tirsasata ta samo musu jinin GHAZ,
Sbd Neman kubutar dasu mijinta ta dawo ANJOM inda ta fadi duk abinda ya faru Banda cewa mijinta na raye zata samo musu jinin GHAZ dan tseratar dashi,
Da farko jinyarta akai a cikin iyalinsa sbd yanayinta da tausayin mummunan halin data shiga na rashin ‘yayanta duka da mijinta datace ya rasu batareda tasan da hasken ya rasu ba,
Adalci da tsananin tausayin GHAZ Ali ya saka ya dawo da ita cikin iyalansa da qarin shakkar zasu iya dawowa su dauketa ko kasheta tinda taga inda suke.
Raunika na fili da boye ne a jikinta da suke kokarin zama baraza ga rayuwarta duk da hakan tayi alkawarin tseratar da mijinta dan haka zamanta a cikin asalin GHAZ shine isharar datake ganin kaman Allah yayi mata Akan ta kubutar da mijinta sbd a farko tasan bazata taba iyawaba dan babu ta inda zata samu kusanci da ahalin GHAZ bare samun jininsu koda diqo daya ne sai gashi batareda tsammani ba Allah Kai tsaye ya shigar ita cikinsu.
GHAZ Ali ya shigo da itane cikinsu shi kuma sbd ya sakata tsaro sosai ta yanda ko akwai wani abin bazata samu damar yi ba ko fita gari.
********Da wannan dalilin Asamah ta zama cikin iyalin GHAZ tareda jinya me kyau ta warke sosai ta zama tamkar amintacciyar ahalin sbd lokaci daya ja sosai hakama kusrawa suna bangaren sun kafa garin kansu sbd burinsu Wanda suke jiran ranar cikarsa.
Lokaci ya tafi sosai kauna da shaquwa me tsafta ce a tsakanin dukkanin GHAZ da Asamah wadda kulawa da gabaki daya yaran gidan ta dawo hannunta duk da sun zama yan mata amma itace ke kulawa da komai nasu musamman Abaas Wanda yayi wata irin shaquwa da ita,
Duk tsawon shekarun datai a cikinsu burinta Akan kubuto da mijinta bai taba fita a ranta ba duk da lokuta da dama tana Jin kaman ta hakura da hakan sbd tsoron illar da kusra zasu iya shigowa gari suyi Wanda a yanzu cikin garin ANJOM iyalan GHAZ ne kadai take dasu sbd tausayinta daya zamo kauna me karfi a gareta.
A yanzu da shekaru suka ja kusra hakurinsu ya fara qare wa dan haka ahankali suka fara farautar duk Wanda zai fito daga garin dama hanyar makusanta hanyar dajin garin ta yanda gabaki daya nahiyar ta zama ta gagari kowane dan Adam bi a tahiri sbd duk Wanda ko hanya ta biyo dashi ta nahiyar ko gawarsa baa samu dan haka duniya da dukkanin nahiyar tarihi bin nahiyar ya zama tamkar tarihi sbd gabaki daya zagaye suke da dajin ANJOM Wanda ya koma babu shiga dajin babu fita dan haka rayuwar ANJOM ta fara shiga wani irin halin tsanani da rashin kwanciyan hankali da fargaban ko Yaushe komai ze iya faruwa garesu.
Tin masifar na waje dajin nasu harta fara shigowa sbd kisan yayi yawan da a bakin gari suke samun gawarwakin mutanensu.
Wannan tashin hankalin ne ya saka GHAZ fara tinanin iyalinsa da bazai iya barin wannan masifar dake kokarin afkowa ANJOM ta shafesu dan haka yasa aka fara Ramin fita garin ANJOM ta baya ta inda yake saka ran babu kusrawan zuwa ruwan dazai iya kaika nahiyoyi da dama dan tsira.
************
Zaune suke a wata irin lafiyayyan rumfar hutawarsu kowannensu na Zaune gurin cike da yayan marmari masu kyau sai qatuwar kwaryar dabino da shima yake da daukan ido.
Ayanah ce kadai bata gurin sbd shirinta dayake daukan lokaci dan haka tana fito wa tareda baiwarta daya Sakeena dake biye da ita.
Rumfar ta tinkaro a natse cikin takun dayake bayyanarda tsananin nutsuwarta da mulki yake ciki,
Qarar sarkar hannunta data kafarta me fidda dan sautin daukan hankali ce ta saka Asamah dake sake jere Kayan marmari fara dagowa ahankali ta sauke idanwanta Akan hanyar tana zubawa halittar Ayanah dake daukan idanuwa duk Wanda zai kalleta ido Tana ambatar Masha Allah Masha Allah cikin zuciyar.
Abaas ne ya juya ahankali shima yana kallan Ayanah din yana zubawa kyakkyawan fuskanta ido yana Godiyan Allah ako Yaushe da Ayanah ta kasance jininsa wadda yakejin kaman jinin da suka hada bai ishesa ba yana tsananin son ace ya sake hada wani abu da ita Wanda zaisa ace yafi duka Sauran yan uwansu kusanci da hada jini ita.
Ganin idanuwansa akanta kaman koyaushe yana kallanta cike da kauna me tsanani ta jini bude bakinta tayi wani kyakkawan murmushi ya mamaye fuskanta har saida hakoranta suka dan bayyana ta qaraso gurin tana miqa masa hannunta dayake sanye da fararen azurfa masu kyau da rashin sirki.