Sashe 29
Hayateem Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ratsasu ruwan dumin lallen keyi tako Ina suna jin dumin me zafi har cikin zuciyarsu sbd tsoron d suke ciki yafi komai yawa a cikin zama imebēti sbd kowane lokaci zasu iya rasa rayuwarsu dan haka kowa shiru yayi jiki a sanyaye ba kowane irin dogon motsi.
Ayanaah ce ta bude idanuwanta da sukai jajir ahankali batareda ta juyo gefenta ba ta kalli Zuhrah da suke shaqan Numfashin guri daya ta miqa hannunta dake wata irin rawa sbd shauqin samun abinda zuciya ke so ta cikin ruwan ta Dora tafin hannunta ahankali kan na Zuhrah wadda tana jin saukan hannun Ayanah a kan fatar hannunta rintse idanuwanta tayi wasu hawaye masu tsananin zafi na gangarowa daga idanuwanta kanta na yin qasa ta damqa hannun Ayanah din tana qanqamewa cikin nata hawayenta na tsananta gudu cikeda shauqi da tsananin farin cikin data manta yaya dandanonsa yake a zuciya,
Itama Ayanah hawayen ne ke ciko idanuwanta da sukai jajir tana hana nata hawayen sauka sbd kada a gano halinda suke ciki sedai tata zuciyar harma tafi ta Zuhrah karaya da samun wata irin nutsuwar ruhi da bata taba samu ba tinda rayuwarsu ta wargaje,
Qanqame hannun juna sukai batareda sun juyo sun kalli juna ba ko motsin da zaa gane kowa da abinda yakeji a zuciya da gangar jiki,
Zuhrah kuka takeyi sosai tana sake sunkuyar da kanta qasa sosai tana rokon Allah kada ya raba hannunta dana Ayanah har sai ranta yabar jikinta.
Ayanah ma da kukanta ke komawa zuciyarta kukan zucin takeyi sosai jikinta na wata irin rawa tana sake qanqame hannun da shine hasken rayuwarta.
A wannan yanayin suka share duka awannin da aka dibar musu a cikin ruwan har saida ruwan ya wuce salap suna cikinsa tukuna aka bude kofar tareda shigowa da wasu irin tsaftaccin towels masu dan girma farare qal a basket me kyau kowannensu da baiwar da zata basa nasa.
A cikin wata irin saa me girman gaske saiga sakinah a cikin masu kawowan wadda kai tsaye gurin Ayanah ta nufa a natse kanta a qasa tana isa ta durqusa gaban a hankali tareda dago mata kyakkyawan kwandon da towel din yake ciki yana fidda qamshi me dadi.
Cikin karfin Hali zuciyarsu na yanka suka raba hannuwansu kowacensu na Juyawa ta fice batareda kowa yaji muryan kowa ba sbd basuda daman magana baa basu damar ba.
Towel din Ayanah ta dauka ahankali ta daura a jikinta Bayan sakinah ta miqe a natse ta tayata zare halfvst din jikinta,
Juyawa sakinah tayi zata bar gurin kanta a qasa idanuwanta suka sauka akan Zuhrah wadda ke fitowa daga ruwan itama take jiri me karfin gaske ya dibeta saura kiris ta kife Allah ya bata ikon tsayawa dakyau tana hana firgicinta bayyana sbd zata iya rasa rayuwarta.
Tsurawa Zuhrah idanuwanta tayi tana tafiya kanta na tsananin sarawa da abinda take gani,
‘Zuhrah da Ayanah a matsayin imebēti na Mutum daya?’
Wace irin mummunan qazamiya kuma haramtacciyar kaddara ce wannan?
Tayaya Mutum daya zai kusance su kuma su samu cikinsa su haihu?
Tayaya ma wannan tashin hankalin kaddarar zata fara?
Shin Ayanah da Zuhrahn sunga junansu kuwa?
Idan sun gani sun kuwa San menene yake shirin faruwa dasu?
Idan har sun sani tasani zasu gwammaci su mutu su dukan dasu yadda da wannan mugun tashin hankalin’
Koda sakinah ta fito daga gurin bata ganin gabanta sosai sbd tama kasa yadda da Zuhrah ce idanuwanta suka gano mata dan bama zai taba yiyuwaba wannan kaddarar a yanzu kam tayi nauyin da kila dole zaa iya rasa dayansu biyun.
Su kuwa suna gama daura towels din daya bayan aka nuna musu wata kofa suka shiga toilet ne masu kyau da tsari a jere dan suyi wanka da ruwan dumi sosai kafin su fito kowacensu akaita sabon gurin da zata zauna,
Suna shiga gurin a kebe yake dan haka rufe su akai sbd su ayanzu ba kowa akeso yaga jikinsu ba dan kuwa sun zama tamkar Al’aurar da haramun ne ganin jikinsu,
Ana rufe su kowacensu ta nufi toilet daya ta shige aka bar Ayanah a tsaye tareda Zuhrah wadda itama take tsaye cak babu Wanda ya motsa a cikinsu tsawon mintina uku,
Tsit gurin yayi sai motsin ruwan daya fara tashi ahankali na fara wankan da Sauran sukai,
Sai a lokacin Ayanah ta dago ahankali cikin wani irin slow na tsananin mutuwan jiki ta Dora fararen idanuwanta masu kyau da kashe jiki akan fuskan Zuhrah wadda itama dagowan tayi ahankali.
#MAMUH
HAYATEEM
by
Mamuhgee
700
0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi
09033181070
Yan Nijar kuma
89825722
Depot my nita
Nissaiba laouali
[09/12, 10:47 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_*
Mamuhgee
27
*_UMMU ASLAM COLLECTION_*
08035014107
-Ina mata yan kwalisa masu son burgewa?
-Shin Kayan kitchen na zamani masu sauki da rahusa na kitchen din yan gayu dama na gargajiya kike so?
-shin abayas na yayi da daukan ido da burgewa kike nema?
-kokuwa original misk dahara kuke buqata dan asali?
-kokuwa Kayan GHT na Neman lafiya da gyara kike so?
-ke harma laces da atampopi na alfarma masu sauki kikeso?
To duka kinzo gidansu indai sune abinda kike buqata ba bata lokaci kinzo kin gama samu kawai tintibi UMMU ASLAM COLLECTION 08035014107 duk inda kike zata aika miki batareda bata lokaci ba.
*********
Idanuwansu na haduwa sarewa Ayanah taji kafafunta na Neman yi ta dafa bango ahankali wannan Karan hawayenta gangarowa sukeyi suna sauka fuskanta har zuwa kirjinta ta rintse ido wani yanayi na cikata ta sake bude idanuwanta akan Zuhrah dake kuka sosai itama tana jin kafafun nata sun gaza,
Ahankali suka tako zuwa juna babu kowa dake ganinsu dan haka suna qarasowa wata irin runguma sukaiwa juna Ayanah na zubewa qasa Zuhrah ta bita qasan suna rungume da juna qamqam kaman zasu shige jikin juna,
Kuka sukeyi sosai kaman ransu zai fita mara sauti sbd kada a jiyo su,
Hannuwan Ayanah suna wata irin rawa ta kamo fuskan Zuhrah ta tsira mata ido hawaye na gudu sosai akan fuskanta tsawon mintina kafin takai bakinta ta sumbaci goshinta ta sumbaci gefen fuskanta ta sumbaci tsakiyar kanta ta kamo hannuwanta suka ta sumbata koina jikinta rawa yakeyi sbd jin kaman zata Hadiye Zuhrah,
Zuhrah kuwa batada Sauran kowane irin kuzari qanqame Ayanah din kawai takeyi tana kuka kaman ranta zai bar jikinta jikinta na rawa itama sosai,
Magana sukeyi wa juna amma ba daman hakan sbd zaa iya jinsu dan haka babu Wanda ya iya bude baki a cikinsu sedai ido da hannuwansu ke aiki,
Zuhrah duk yanda taso kasa riqe kanta tayi ta gama ficewa hayyacinta kamo fuskan Ayanah tayi da tafin hannuwanta biyu takai bakinta kan kunnenta ta bude baki da wani irin sauti daya saka gabaki daya dan Sauran karfin halin Ayanah rushewa tace
‘Yēne Ayanah(my Ayanah),hiyiwēteni(my life),Yene widi(my precious)’
Rintse idanuwa Ayanaah tayi tana sake qanqame Zuhrah kafin ta bude bakinta cikin tsananin sanyi da mutuwan jiki tace
‘Ina rokon Allah ya zama gatanki Zuhrahna ya baki kariya da juriya tareda ingancin rayuwa,
Bazan taba barin a gurbata rayuwanmu da alaqar mu ba,
Duk halinda zamu shiga bazamu taba zama a cikin qazantacciyar alaqar da akeson mu zauna ba,zan baki kariya da rayuwata koda bama tare,
Zan zabi mutuwa akan a hada mu a qazamiyar shimfidar mu yada mummunan zuriar datake ta Allah wadai a garemu matiqar muka hada shimfida da Mutum daya…..’
Kuka sosai Zuhrah ke qarawa sbd maganganun Ayanaah din dake sake kashe rayuwarta sbd sunzo gabar da kaddarar tayi musu muni me girma bama girma ba,
Duk shauqin ganin junansu Ayau Bayan shekara guda bai taho musu da alkhairi ba dan kuwa wannan shine mafi girman quluwar kaddararsu da basusan tayaya zasu fuskancetaba kuma tinda aka zabesu din to tabbas Ana nufin sai sun sauke buqatar sultan din BOYEM Wanda mutuwar dayansu ce kadai zata Hana hakan idan kuma sun fito sun bayyana alaqarsu sbd Kaucewa hakan to dukansu ne zasu rasa ransu sbd sun aika laifi me girma ita kuma a yanzu tanason ko yayane dayansu ya rayu sbd Abaas dayake raye a duk inda yake.
Sun jima a hakan kafin daqyar suka iya rabuwa da jikin juna sbd motsin fitowan wasu wanka dan haka kai tsaye a sanyaye suka fada toilet daddaya suma take suka sakar wa kansu ruwa sbd kukan ruwan ya hana aji sautin kukan dasuke fasa a tare.
Sun jima a toilet din kafin suka fito kusan a tare suka fito kan kowannensu a qasa batareda sun sake kallan ko inda inuwan juna take ba.
Haka aka fice dasu zuwa inda zasu zauna kowannensu da Wanda zai taimaka masa zama a dakinsa dan sai wadda sultan ya kwana da ita zaa warewa bangarenta me girma da bayi idan ta samu ciki zata cigaba da zama idan bata samu ba sultan ya gama yayinta tafiya ake da ita.
Kwata kwata ba guri daya aka aje su ba kowa da dakinta daban dan haka suna dawowa ba jimaw aka kawo wa kowacensu lafiyayyun Kayan itatuwa da zallan madarar nonon raqumi me dumi da zuma tareda duk wani abu dazai Kama jikin mace na qarin Ni’iman nace me karfin gaske.
Sakinah aka kawowa Ayanah wadda taje taji jikinta ya sake mutuwa Ana rufe musu daki ta zube gaban sakinah tana kuka me karfi da Neman yaya zatai da rayuwarta da wannan sabuwar kaddarar.
Sakinah ma kukan takeyi cikin tashin hankali da rashin sanin tinanin yi dan kuwa wannan Karan ko ita batada shawarar bayarwa sbd abu dayane a bayyane tabbatacce kuma shine Allah ne kadai zai Hana dayansu barin duniya kokuma su dukan ma.
Kuka sukeyi tare tsawon lokaci kafin aka taba kofar dakin wadda ta sakasu shire hawayensu suna Miqewa tsaye kansu a qasa sakinah ta bude dakin.
Tenya ce da kanta tareda masu Binta a baya kaman zasu mata sujjada,
Shigowa tayi tana kallan fuskan Ayanaah din wadda fuskanta ta kumbura sosai tayi jajir alaman kuka me karfin gaske tayi,
Ayanaah ce ta bude idanuwanta da sukai jajir ahankali batareda ta juyo gefenta ba ta kalli Zuhrah da suke shaqan Numfashin guri daya ta miqa hannunta dake wata irin rawa sbd shauqin samun abinda zuciya ke so ta cikin ruwan ta Dora tafin hannunta ahankali kan na Zuhrah wadda tana jin saukan hannun Ayanah a kan fatar hannunta rintse idanuwanta tayi wasu hawaye masu tsananin zafi na gangarowa daga idanuwanta kanta na yin qasa ta damqa hannun Ayanah din tana qanqamewa cikin nata hawayenta na tsananta gudu cikeda shauqi da tsananin farin cikin data manta yaya dandanonsa yake a zuciya,
Itama Ayanah hawayen ne ke ciko idanuwanta da sukai jajir tana hana nata hawayen sauka sbd kada a gano halinda suke ciki sedai tata zuciyar harma tafi ta Zuhrah karaya da samun wata irin nutsuwar ruhi da bata taba samu ba tinda rayuwarsu ta wargaje,
Qanqame hannun juna sukai batareda sun juyo sun kalli juna ba ko motsin da zaa gane kowa da abinda yakeji a zuciya da gangar jiki,
Zuhrah kuka takeyi sosai tana sake sunkuyar da kanta qasa sosai tana rokon Allah kada ya raba hannunta dana Ayanah har sai ranta yabar jikinta.
Ayanah ma da kukanta ke komawa zuciyarta kukan zucin takeyi sosai jikinta na wata irin rawa tana sake qanqame hannun da shine hasken rayuwarta.
A wannan yanayin suka share duka awannin da aka dibar musu a cikin ruwan har saida ruwan ya wuce salap suna cikinsa tukuna aka bude kofar tareda shigowa da wasu irin tsaftaccin towels masu dan girma farare qal a basket me kyau kowannensu da baiwar da zata basa nasa.
A cikin wata irin saa me girman gaske saiga sakinah a cikin masu kawowan wadda kai tsaye gurin Ayanah ta nufa a natse kanta a qasa tana isa ta durqusa gaban a hankali tareda dago mata kyakkyawan kwandon da towel din yake ciki yana fidda qamshi me dadi.
Cikin karfin Hali zuciyarsu na yanka suka raba hannuwansu kowacensu na Juyawa ta fice batareda kowa yaji muryan kowa ba sbd basuda daman magana baa basu damar ba.
Towel din Ayanah ta dauka ahankali ta daura a jikinta Bayan sakinah ta miqe a natse ta tayata zare halfvst din jikinta,
Juyawa sakinah tayi zata bar gurin kanta a qasa idanuwanta suka sauka akan Zuhrah wadda ke fitowa daga ruwan itama take jiri me karfin gaske ya dibeta saura kiris ta kife Allah ya bata ikon tsayawa dakyau tana hana firgicinta bayyana sbd zata iya rasa rayuwarta.
Tsurawa Zuhrah idanuwanta tayi tana tafiya kanta na tsananin sarawa da abinda take gani,
‘Zuhrah da Ayanah a matsayin imebēti na Mutum daya?’
Wace irin mummunan qazamiya kuma haramtacciyar kaddara ce wannan?
Tayaya Mutum daya zai kusance su kuma su samu cikinsa su haihu?
Tayaya ma wannan tashin hankalin kaddarar zata fara?
Shin Ayanah da Zuhrahn sunga junansu kuwa?
Idan sun gani sun kuwa San menene yake shirin faruwa dasu?
Idan har sun sani tasani zasu gwammaci su mutu su dukan dasu yadda da wannan mugun tashin hankalin’
Koda sakinah ta fito daga gurin bata ganin gabanta sosai sbd tama kasa yadda da Zuhrah ce idanuwanta suka gano mata dan bama zai taba yiyuwaba wannan kaddarar a yanzu kam tayi nauyin da kila dole zaa iya rasa dayansu biyun.
Su kuwa suna gama daura towels din daya bayan aka nuna musu wata kofa suka shiga toilet ne masu kyau da tsari a jere dan suyi wanka da ruwan dumi sosai kafin su fito kowacensu akaita sabon gurin da zata zauna,
Suna shiga gurin a kebe yake dan haka rufe su akai sbd su ayanzu ba kowa akeso yaga jikinsu ba dan kuwa sun zama tamkar Al’aurar da haramun ne ganin jikinsu,
Ana rufe su kowacensu ta nufi toilet daya ta shige aka bar Ayanah a tsaye tareda Zuhrah wadda itama take tsaye cak babu Wanda ya motsa a cikinsu tsawon mintina uku,
Tsit gurin yayi sai motsin ruwan daya fara tashi ahankali na fara wankan da Sauran sukai,
Sai a lokacin Ayanah ta dago ahankali cikin wani irin slow na tsananin mutuwan jiki ta Dora fararen idanuwanta masu kyau da kashe jiki akan fuskan Zuhrah wadda itama dagowan tayi ahankali.
#MAMUH
HAYATEEM
by
Mamuhgee
700
0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi
09033181070
Yan Nijar kuma
89825722
Depot my nita
Nissaiba laouali
[09/12, 10:47 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_*
Mamuhgee
27
*_UMMU ASLAM COLLECTION_*
08035014107
-Ina mata yan kwalisa masu son burgewa?
-Shin Kayan kitchen na zamani masu sauki da rahusa na kitchen din yan gayu dama na gargajiya kike so?
-shin abayas na yayi da daukan ido da burgewa kike nema?
-kokuwa original misk dahara kuke buqata dan asali?
-kokuwa Kayan GHT na Neman lafiya da gyara kike so?
-ke harma laces da atampopi na alfarma masu sauki kikeso?
To duka kinzo gidansu indai sune abinda kike buqata ba bata lokaci kinzo kin gama samu kawai tintibi UMMU ASLAM COLLECTION 08035014107 duk inda kike zata aika miki batareda bata lokaci ba.
*********
Idanuwansu na haduwa sarewa Ayanah taji kafafunta na Neman yi ta dafa bango ahankali wannan Karan hawayenta gangarowa sukeyi suna sauka fuskanta har zuwa kirjinta ta rintse ido wani yanayi na cikata ta sake bude idanuwanta akan Zuhrah dake kuka sosai itama tana jin kafafun nata sun gaza,
Ahankali suka tako zuwa juna babu kowa dake ganinsu dan haka suna qarasowa wata irin runguma sukaiwa juna Ayanah na zubewa qasa Zuhrah ta bita qasan suna rungume da juna qamqam kaman zasu shige jikin juna,
Kuka sukeyi sosai kaman ransu zai fita mara sauti sbd kada a jiyo su,
Hannuwan Ayanah suna wata irin rawa ta kamo fuskan Zuhrah ta tsira mata ido hawaye na gudu sosai akan fuskanta tsawon mintina kafin takai bakinta ta sumbaci goshinta ta sumbaci gefen fuskanta ta sumbaci tsakiyar kanta ta kamo hannuwanta suka ta sumbata koina jikinta rawa yakeyi sbd jin kaman zata Hadiye Zuhrah,
Zuhrah kuwa batada Sauran kowane irin kuzari qanqame Ayanah din kawai takeyi tana kuka kaman ranta zai bar jikinta jikinta na rawa itama sosai,
Magana sukeyi wa juna amma ba daman hakan sbd zaa iya jinsu dan haka babu Wanda ya iya bude baki a cikinsu sedai ido da hannuwansu ke aiki,
Zuhrah duk yanda taso kasa riqe kanta tayi ta gama ficewa hayyacinta kamo fuskan Ayanah tayi da tafin hannuwanta biyu takai bakinta kan kunnenta ta bude baki da wani irin sauti daya saka gabaki daya dan Sauran karfin halin Ayanah rushewa tace
‘Yēne Ayanah(my Ayanah),hiyiwēteni(my life),Yene widi(my precious)’
Rintse idanuwa Ayanaah tayi tana sake qanqame Zuhrah kafin ta bude bakinta cikin tsananin sanyi da mutuwan jiki tace
‘Ina rokon Allah ya zama gatanki Zuhrahna ya baki kariya da juriya tareda ingancin rayuwa,
Bazan taba barin a gurbata rayuwanmu da alaqar mu ba,
Duk halinda zamu shiga bazamu taba zama a cikin qazantacciyar alaqar da akeson mu zauna ba,zan baki kariya da rayuwata koda bama tare,
Zan zabi mutuwa akan a hada mu a qazamiyar shimfidar mu yada mummunan zuriar datake ta Allah wadai a garemu matiqar muka hada shimfida da Mutum daya…..’
Kuka sosai Zuhrah ke qarawa sbd maganganun Ayanaah din dake sake kashe rayuwarta sbd sunzo gabar da kaddarar tayi musu muni me girma bama girma ba,
Duk shauqin ganin junansu Ayau Bayan shekara guda bai taho musu da alkhairi ba dan kuwa wannan shine mafi girman quluwar kaddararsu da basusan tayaya zasu fuskancetaba kuma tinda aka zabesu din to tabbas Ana nufin sai sun sauke buqatar sultan din BOYEM Wanda mutuwar dayansu ce kadai zata Hana hakan idan kuma sun fito sun bayyana alaqarsu sbd Kaucewa hakan to dukansu ne zasu rasa ransu sbd sun aika laifi me girma ita kuma a yanzu tanason ko yayane dayansu ya rayu sbd Abaas dayake raye a duk inda yake.
Sun jima a hakan kafin daqyar suka iya rabuwa da jikin juna sbd motsin fitowan wasu wanka dan haka kai tsaye a sanyaye suka fada toilet daddaya suma take suka sakar wa kansu ruwa sbd kukan ruwan ya hana aji sautin kukan dasuke fasa a tare.
Sun jima a toilet din kafin suka fito kusan a tare suka fito kan kowannensu a qasa batareda sun sake kallan ko inda inuwan juna take ba.
Haka aka fice dasu zuwa inda zasu zauna kowannensu da Wanda zai taimaka masa zama a dakinsa dan sai wadda sultan ya kwana da ita zaa warewa bangarenta me girma da bayi idan ta samu ciki zata cigaba da zama idan bata samu ba sultan ya gama yayinta tafiya ake da ita.
Kwata kwata ba guri daya aka aje su ba kowa da dakinta daban dan haka suna dawowa ba jimaw aka kawo wa kowacensu lafiyayyun Kayan itatuwa da zallan madarar nonon raqumi me dumi da zuma tareda duk wani abu dazai Kama jikin mace na qarin Ni’iman nace me karfin gaske.
Sakinah aka kawowa Ayanah wadda taje taji jikinta ya sake mutuwa Ana rufe musu daki ta zube gaban sakinah tana kuka me karfi da Neman yaya zatai da rayuwarta da wannan sabuwar kaddarar.
Sakinah ma kukan takeyi cikin tashin hankali da rashin sanin tinanin yi dan kuwa wannan Karan ko ita batada shawarar bayarwa sbd abu dayane a bayyane tabbatacce kuma shine Allah ne kadai zai Hana dayansu barin duniya kokuma su dukan ma.
Kuka sukeyi tare tsawon lokaci kafin aka taba kofar dakin wadda ta sakasu shire hawayensu suna Miqewa tsaye kansu a qasa sakinah ta bude dakin.
Tenya ce da kanta tareda masu Binta a baya kaman zasu mata sujjada,
Shigowa tayi tana kallan fuskan Ayanaah din wadda fuskanta ta kumbura sosai tayi jajir alaman kuka me karfin gaske tayi,