← Book details Hatsabibin Boka Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
CHAPTER 38 OF 41

PART 2⃣

Hatsabibin Boka Part 2 Complete Hausa Novel · about 6 min read

47
By gentle
Lady💃🏽


Bayan wata daya saiga dalhatu Wanda Usman yaba nemansu yaganosu awani kauyen giwa dayake zariya .

Malam garba Yakoma sana ar siyarda rariya akasuwa ranarda yasanar dashi yakirah kaleed yafada masa washe gari suka dunguma dashi da Usman da dalhatu

Kasuwa suka wuce kaitsaye yana cikin Yar runfarsa yaga mota yatsaya yabi motar dakallo yaga wadanda zasu fito Usman ne yasoma fitowa aituni malam garba yazama natsaye

Bakinsa harrawa yake wajen kiran sunansa Usman da murmushi suka karasa wajen runfar

Usman yaduka harkasa yagaidashi kaleed ma haka"" malam yafashe da kuka yace Usman ina yata ina kabarota???

Usman yace baba wannan maganar tanada tsayi baikamata muyita ananba idan gidan baida nisa mukarasa cen mana

Malam garba yace to to shikenan yacewa wani makocinsa yadibamasa zaije gida yadawo nan Usman yasallami dalhatu yace zaka iyah tafiya muhade gobe ya maganar wadanda nasaka kabincikomun

Yace wlh haryanxu bansamu komai gamedasuba Amman munakan bincike dazaran nasamu zankiraka sukai sallama yawuce sukuma suka shiga mota dama kaleed ne yakejan motar malam"" yayita masu kwatance harsuka kaigidan

Inna huwaile tana kofar gida dadan kanonta nabara""

Fa Iza tana zaune dawani yaro gabadaya an gundule mata kafa fuwa fa Iza tabi motar dakallo aranta tana ayyanawa idan wannan mai motar yabasu sadaka boyewa zatayi bazata barwa inna huwaile ba

Usman yana fitowa tasoma sadaka sabida Allah abamu saboda Allah"" kabamu nan Allah yabaka acen sadaka fisabilillahi

Abamu na shiru tayi sakamakon ganin malam yafito cikin motar huwaile tace yakika daina fa Iza koyatafi

Tace ah ah nagansu tareda malam ne gasunan suna tunkaromu tuni cikin huwaile yaduri ruwa tace Allah yasa bamagana yadauko manaba


Muna zaman zaman mu abunda zamuci kawai muke nema nezaikaishi yajawo mana fitina"" sallama sukayi fa Iza ce tasamu Damar amsawa malam yace kukaraso ciki yace huwaile kishigo mijin Ameena ne

Tace wacce ameena badai yataba??? Yace itah wayyo ni huwaile ina kabarota Dan nan Dan Allah kakiramun itah kalli yanda nakoma duk sanadin muzgunawar danayiwa rayuwarta tafashe dakuka nacuceta nacutarda rayuwarta

Ninasan alhakinta bazai barniba" Dan Allah kakiramun itah innemi yafiyarta tunkafin inmutu inhadu da Allah bansan mezance masaba naci amanar marainiyar Allah ta sake fashewa dakuka

Usman yace inna mushiga daga ciki saimuyi maganar haka tamike dayar sandarta tana lalabe kaleed ne yarike mata sandar zuwa cikin gida

Fa iza kuma tasoma Jan jiki zuwa cikin gidan yaronta yana bayanta" malam yashinfida masu tabarma suka zauna

Malam ameena kawai yaketa tambaya Usman yace sai hakuri baba Ameena tarigamu gidan gaskiya

Huwaile tadora hannu aka takwalma ihu wayyo nabanie na lalace inaxankai tarin alhakinta yake kaina kaico meyasa nadinga cutarda yarinyar nan alhalin batayimun laifin komai

Usman yace innah kiyi hakuri wannan yaron tane shine Wanda Allah ya azurtamu dasamunsa kafin takoma ga mahaliccinta

Shine yadameni akan nakawoshi yanason ganin dangin mahaifiyarsa dama nasan kulba Dade zainemi sanin tushensa shiyasa nasa anemomun inda kuke tosaijiya nasamu cikakken bayanin indakuke

Malam garba Wanda shima hawayen yake shara yace Allah sarki ameena kiyafemun banyimaki abunda yadace nayimaki amatsayina na uba ba nacutarda rayuwarki ganina dake nakarshe tunsanda tazo tareda yaron nan yana shekara biyu

Ace yata daya da Allah yabani aduniya tuntana karama bataji dadina ba gashi hartarasu Amman banida labari nibansan meyasa nabar kaduna ba

Hauwaile tana sharbar majina tace malam kagafartamun wlh aikinane nice nakarbo maganie aka daureka agarin nan duk abunda yafaru wlh aikinane Nice nashiga tsakaninka da yarka nantabasu labarin makircinda taitahadamata
.

Malam baisan sanda yadauketa da mariba yace Allah ya isa tsakanina dake bazan taba yafemakiba kuma kije nasakeki saki uku

Huwaile ta sake fashewa dakuka harda kururuwa tace nashiga uku malam karkayimun haka inazani dani dawan nan yarinyar kadubi yanda Allah yamiyardai nibana gani itakuma tarasa kafafuwanta kobaka koremuba Allah yayimaka sakayya idan kayimana Allah ya isah yazamu sake zama koyanxu aimunga isha ra masu hali irin namu saisu daina domin karshensu bazaiyi kyauba

Malam yace wlh baxan iyah cigaba dazama dakeba huwaile kincuceni kinsa nacutarda marainiyar Allah ahakan kikeson kigama lafiya??/ taya xakisamu farinciki bayan kuma kintauye nawasu aibazaki tabagani dakyauba

Tace nagani wlh nagani duk yanda nake aibata ameena inakiranta Yar iska saitayi cikin shege inacewa tanabiyar maza saigashi yata danake so itah tajawomun abun kunya harda tukuicin da. Dama ance duk abunda kke kirawa diyan wani tabbas nakane zasu kasance..


Yanxu abunda yake faruwa kenan kacewa Dan wani shege ko Dan iska ko barawo alhalin iska baya haihuwa kacewa yarwani karuwa ko yar iska kasani zakasamesu acikin yayanka..

Antambayi manzon Allah daidaga cikin mutanensa yace ya rasulullahi mezanyi domin inkiyaye kaina daga shiga wuta ??? Sai manzon Allah yacemasa Kuffa lisanika ka yi riko da harhenka saisukace ya manzon Allah tayamutun zairike abunda yake magana dashi?? Sai manzon Allah yace ka kiyaye halshenka daga mummunar magana


Mummunar magana takumshi ka aibata Dan uwanka musulmi baijiba baiganiba kayimasa karya koka muzantashi kokaimasa sharri koka aibatashi agunwani kace yayi Abu kaza alhalin baiyiba. Komai zakafada akan Dan uwanka yakasance alkhairine

Hakika harshe yanakai mutum ga mahalaka sautari zakafadi Abu kaga kamar bakomaibane alhalinkuwa babban abune


Tasharbe majina ko haka Allah yabarmu munga ishara banji haushinkaba danbabu wanda zaizauna da shu umar mace irina"" "

Usman yace malam hakuri zakayi "" yace hmm mezanyiwa hakurin kakalli abunda tayimun tarabanie dayata abokaina dukiyata Dan tasanadinta komai nawa ya tabarbare

Dama duk gidanda matargidan tazama masifaffiya yana karyarda arzikin maigida tunsanda na aureta komai nawa yaja baya inata hasarar kayana kudina sai darjewa suke

Saiganie waida tallar rariya ai idanma nazauna da itah natabbata shege Dan watarana wlh tsirara zanyi yawo"

Me akeyi dawadan nan mutanen masu bakar aniya kabarma bani hakuri danyauma zansaka gidan nan kasuwa inkoma inda akasanni incigaba dasabuwar rayuwa

Huwaile sai kuka take Usman yace ba za ayi hakaba kabarmasu gidan muje cen zansiyamaka wani gidan Wanda kakeso zankuma baka jari

Malam yace yanzun wannan annamimiyar zakabawa gida harkamanta abunda taimaka da matarka???


Usman yace bakomai malam aikomai yawuce ko iyah haka aitaga isha ra kuma wacce tayiwa bata duniyar ni aganina komai yawuce hannu yasaka cikin aljihu yaciro kudi masu yawa yabasu yacewa malam yatashi suwuce


Yace tunyanzu kabari nayi bankwana da abokaina nakuma hada kayana"" Usman yace munada sauran lokaci muje tare yanxun kaimasu sallama

Kayanka kuma kabarsu zansiyamaka wasu acen haka malam yataso sukafito innah huwaile saikuka take tanakiran sunan malam

Haka suka fita sukashiga motar zuwa kasuwa bakin runfar malam suka tsaya yafita dasauri yanata fara a wani mai tallar alawa dakayan zakie yazo wajen motar yana asiye alawa ayi tsaraba akaiwa iyali

Usman haka kurum yaji gabansa yafadi kofar motar yabude yafita shikuma mai alawa yadauka siye zaiyi yajuyo dasauri ido hudu sukai Usman yanunashi dayatsa yace kabeer
Tiren alewar yayar yace Yaya Usman!!!!


Aisha ✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!!*☠
Chapter 38 · 0% Book details