← Book details Hatsabibin Boka Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
CHAPTER 30 OF 41

PART 2⃣

Hatsabibin Boka Part 2 Complete Hausa Novel · about 4 min read

38
By gentle
Lady💃🏽


Sanadin haka nasamu hawan jinie saida nayi sati uku anajinya sannan nasamu sauki likita yatabbatar mun zuciyata ta kunbura aguji yimun abunda zaibatamun rai sannan inrage Yawan tunani

Yanisa shekaran jiya ana sallamoni nace bazan sake kwana dayaba sainazo kano ganin natashi hankalina karciwona yatashi """

Suka yarda muka taso fatana daya naga fateema hawaye suka zubo masa yace Ashe banada rabon sake ganinki fateema Nina San nayi bankwana da jindadi da farinciki ""

Nasan shikenan babu wani sauran jindadi agareni"" kiyafemun nasan nacutarda rayuwarki gabadaya wajen yayi shiru bakajin komai saitashin kuka daga shi har su muktar

Labila ma kuka takeyi hartanajan ajiyar zuciya" " yanzun duk wannan abun da mamanta takeyi Ashe akwai mata masu irin wannan rayuwar

Sundade suna kuka sannan malam garba yayi gyaran murya yace Muhammad kadaina kukan nan kasan bakada lafiya yanisa koda mahaiifiyarsu takoma ga mahaliccinta batakoma dakai araiba

Dantasan komai nikaina bata sanardani abunda yafaru da itah acen ba saida tarihi yasake maimaita kansa yarka gatanan yanuna khadija itama tatsilge rijiya dabaya

Rashin sakaci da addua dakuma riko da Ibada shine yakareta dayanzu itama sai labari

Muhammad yadago yakalleshi yace itama haka akaimata??? Yagyada kai sosai kuma bokanda yayiwa mamanta shine yayimata

Anan yasake basu labarin komai"" faruq yajinjina kai yace waime yasaka irin wadan nan bokayen baza arika kashe suba

Aiwadan nan barinsu cikin al umma bala ine saboda annobane"" Usman yanisa yace taya kake ganin mai aiki da aljanu irin wannan za a iyah farautar ransa cikin sauki

Aganinka akwai Wanda zaishiga dajin yatsirah daransa??? Mutuminda ya gagari aljanu ballatana Kuma mu mutane

Baxance bazai farautuba Dan baifi karfin Allah ba Amman kafin mutum yaziyar ceshi saiya nemi addu oin tsarin jiki sannan kuma yakasance mai takawa

Gabadaya wajen shiru yayi kowa da abunda yake sakawa aransa bayan shudewar wasu lokuta Usman yamike yace shizai shiga wajen hajiya labila ma tamike tabishi

Bayan fitarsune Muhammad yagabatar masu da matar faruq sadiya"" anan yake tambayar muktar shibaiyi aureba???

Malam yayi murmushi yace baiyiba kuma gashi" yagirma baisan meyake jiraba muktar murmushi kawai yakeyi yana Sosa kai

Khadija ce tafadamasu ai kuwa malam yayi murna sukacigaba da tattaunawa"" ""

Tunda sukabar gidan labila batadaina kukaba sunashiga gidan hajiya ta ruga dakinta

Hajiyar tana zaune falo tabita dakallo sannan tamaida kallonta wajensu kaleed dasuka shigo bayanta tareda sallama ta amsa masu bakinta sake

Saman kujerah suka zauna suna gaida itah" ta amsa tana tambayarsu me akaiwa waccen kuma???

Usman yace mefa daga gidansu khadija muke kinsan mahaifinta yazo shine damukaje yake bamu labarin abunda akaiwa mahaifiyar ta shine tayita kuka nasan tatuna da mahaiifiyar tane.

Hajiya tanisa tace sai hakuri kunsan dole taji wani iri uwafa akace aibabu wani Dan kwarai dazaiso ace ga mahaifiyarsa ta aikata hakan

Allah yakyauta sukace Ameen" tayi shiru daga bisanie tace wainikuwa babangida yanzun tana ina???
.yanisa alamun rashin jindadi yace abun yayi tsamari Dan hauka takeyi bata wasaba

Amman nasa ankaita asivitin mahaukata dalilin labila kawai nake jin tausayin lubabatu Amman tayimun abunda " harna mutu bazantaba mantawa da abunba saidai inkauda idona kawai

Hajiya tace hakane Amman aikomai yawuce saimu kalli abunda yake gabanmu"" yace hakane hajiya ina hafiz??

Tagyara zamanta tace yanxun kuwa yabar gidan nan kasan anmiyarda matarsa gida haihuwa

Usman yakishingida akujera yace Niger zamuje jibi nasan bazai sameniba kifadamasa yashirya dawuri yasameni gobe kaduna dagacen zamuwuce

Hajiya tace ikon Allah zakuje gaida kakannin khadija ne??? Yana kallon kaleed yace ah ah maigidanki zamuje tsaida maganar auren sa

Inaso idan muktar yashirya ahade harna labila kozatasamu Dan kwanciyar hankali kar damuwa tayimata yawa kafin muga yanda ciwon mamanta zai kasance

Hajiya tace ikon Allah kace kishiya za ayimun ina zaman zamana tokai maigida haka akeyi ??. Kaleed murmushi kawai yayi
.
Hajiya tace dole kayi dariya Amman bakoai Nina San bayan daurin dankwali da shafe shafe baza agwadamun komaiba

Dariya suka sa gabadaya Usman yace ina dayan maigidan nakie??

Tace wai Abdul yana islamiyya"kasan yanzun harda sukeyi baicika zama gidaba

Yace aikuwaa ya dace yadage kafin yagama secondary yasauke dannasan dayaje Kasar waje zaiwatsarda karatun

Yasamu abunda yasamu Allah yataimaka """basuwani dadeba Usman yace shizaiwuce tare suka wuce akabar labila

Gidansu khadija suka koma yayimasu sallama sukafito nan yabar khadija suka koma kaleed dadi duk yakumeshi

Yamatsu suje yaga zainab dinsa yau kusan kwaana uku basuyi wayaba kuma bazai kirataba soyake kawai taganshi

Washe gari Hafiz yaje kaduna yakwana dasafe Usman yakira Abdul yasanar dashi sukahade airport din sukabi jirgi zuwa Niger dama kaleed yasanarda hassan zuwansu

Jirginsu yana sauka akazo daukarsu kaleed saida yasake kwankwantawa hassan karfa afadawa zainab

Suna isa Gida fadar mai martaba sukaje bayan sungaisa kaleed yawuce gida anan yabar su Usman


Da sallama yashiga gidan mamansu tana wajen hutawarta yaran gidan suna ganinsa sukahau ihun murna Suna ga ya sultan gayaya sultan zainab tana daki kwance tayo bururut tafito

Haleema yadaga sama yanayiwa wasa yashafa Kansu kaitsaya wajen mom yawuce saibayanshi zainab taganie

Waifa fushi takeyi kwana biyun dabai nemetaba Amman yanzun data gansa Sam tamanta wani dadine taji duk yakumeta


Aisha✍🏼
[4/26, 7:38 AM] ‪+234 703 962 5239‬: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!!*☠
Chapter 30 · 0% Book details